Showing 24001 words to 27000 words out of 49582 words

Chapter 9 - AUREN BAZATA COMPLETE BOOK BY ZAINAB YAKASAI.txt

yarinya "Aunty Shukra Kinga yaya ze dakeni ko

" ME kika yi masa Shukra ta tambaya tana kallon Safeer da Fuskar tausayi (Irin kar ya daki Miemie) "


" Harara na tayi ya bata Answer yana dauke kai "



" Shukra ta dawo da kallonta kan Miemie wadda take ta zare ido kamar tayiwa sarki karya, Miemie bakya jin Magana ko kina abun kamar karamar yarinya, Ya Safeer din sa 'ankine da kike hararar sa?


" A a Aunty Shukra yi hakuri bazan kara ba "


" Kima kara, Shukra ta fada tana jan hannun Miemie zuwa daki "


" Koda suka shiga dakin kayan Miemie suka hau hadawa, Sosai Shukra ta yiwa Miemie nasiha kan halayenta, Da alama nasihar ta shige ta don har kuka sai da tayi tana bawa Shukra hakuri "


" Tun 7:00 pm suka tafi gidan Mamah maida Miemie, Mamah tayi mamakin nitsuwar Miemie don yan kwana kin da tayi a gidan Safeer sosai ya ke mata fada, Shukra kuma tayi nasiha "




" Sun dade gidan don se wajen 11:00 su Aysher suka rakasu mota suka tafi gidansu"


"Washe gari Da Safeer zai tafi Office sai da ya sauke Shukra a gidan Ammii sannan ya wuce "


" 4:30pm Safeer ya shiga Office din Haiydar da sallama a bakin sa, Ya samu guri ya zauna yana fuskantar Haiydar "

" Malam wae yaushe zaka fito da mata ne kayi Aure, ko baka gaji da zaman gidan Hajiya ba?


"sai nan da shekara uku meye matsalar ka?


"Kaga Malam in zaka dawo hayyacinka ka dawo Miemie fa tayi maka kankanta kabarwa Abdallah kawae ka nemi wata "

" Bazan bar masaba yaje shima ya nema mana inji Haiydar ya fada rai a bace "


" To na fahimce ka bakada Budurwa ne shiyasa, Ko kanason Aysher na baka ita "


" Banason ta ni Miemie nake so kuma ko kaine babanta baka isa ka hanani AUREN taba" Haiydar ya fada sanda ya mike yana tattara kan table dinsa "



" ni na isa na hanaka auren Miemie? Allah ya baka Hakuri zo muje gidan Ammii zan dauko Shukra sai ku gaisa ma "


" To kawai yace sannan suka fito a tare kowa ya shiga motar sa suka kama hanyar gidan Ammiii "


" Sanda suka je gidan Ammii ana kiran sallar Magrib saboda haka basu shigaba sai da sukayi sallah a wani masallaci kusada gidan "


" Sai bayan sallar isha sannan suka baro gidan Ammii, Areef harda kukansa (Kukan rabuwa) "


" Washe gari Safeer beje Aiki ba fita yayi yayo musu siyar yar duk wani abu dayasan zasu bukata kuma bazasu samuba acan "


" Da yamma wajen karfe biyar Safeer da Shukra kwance akan gado rungume da junansu suna hirar su ta masoya akayi Knocking a kofar parlour "


" Safeer ne ya mike yasa rigarsa sannan ya fice don duba waye "


" Yana bude kofar yaga wata yarinya kamar Shukra take da yarinya a hannunta, Yarinyar na ganinsa ta fara mika masa hannun alamar ya dauketa tana kiransa da Daddy"



"Hannu yasa ya karbeta sannan suka gaisa da Mamanta, Guri ya bata ta shigo parlourn sannan ya wuce bed room din Shukrah don kiranta "



" Da fara 'a dauke a Fuskar ta ta karaso parlourn "Sannu da zuwa Ibtee, ya Gida ya Amal?


" Lafiya kalau muke, ae Amal fushi take dake tunda kin dena zuwa gurinta "


" Eyya Amal tayi hkr tana raina wlh, Naga ta makale wa ya Safeer kamar ta sanshi "



" Ae da alama mijin kin nn yana son Yara da yawa, Yaushe za haihu ne Ibtee ta fada tana neman daga rigar Shukra "


" Rike Hannun Ibtee Shukrah tayi tana dariya, Ke ni banida ciki fa "

" Zama ki fadi gsky ne "


" Daga nn Shukrah ta mike ta kawo wa Ibtee lemo da ruwa "


" Sai da aka kira sallar magrib sannan Safeer ya kawowa Ibtee Amal yawuce Mosque, itama gidanta ta tafi"



"Zuwan Ibtee ne ya hana Shukrah hada musu kayan su sbd hk bayan sun gama cin abinci sunyi sallar isha shukra ta shiga daki don hada musu kayan "


" A tare suka hada kayan da Safeer sannan sukayi shirin bacci don jirgin karfe bakwai zasu bi "


"Safeer ne ya musu addu ' a ya tofe musu jikinsu sannan suka kwanta rungume da juna"


"Yimin labari me dadi Shukrah, Safeer ya fada mata a kunnenta "

"Ya Safeer ni ban iya lbr ba sai dai kai ka yimin, Shukra ta fada kasa kasa"

"To zan miki wani iri kike so "


" Kowanne ma "

" Nan Safeer ya fara mata labarin cikin kunnenta "


" Sai dariya Shukrah take kyalkyalawa tana kara shigewa jikinsa, a takaice dai sai da Suka raya daren ranar, "


" Tun kafin Asuba Suka farka sukayi wanka sukayi nafila suka jira sallar Asuba, Tea kawae suka sha suka sa kayan su a booth suka tafi gidan Mamah "

" Aysher da Miemie suka dauko sannan suka wuce Airport "


" Jiran minti goma sukayi sannan aka kirasu, Suka wuce suna daga musu hannu, Zo kuga kuka gun Miemie harda birgima a kasa wae kar Shukrah ta tafi ta barta "

" Aysher ce taja motar ta maidasu gida har amotar Miemie kuka take, suna zuwa gida ta kwanta a parlour sai bacci.......





SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞
[4/18, 6:59 PM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻






WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA







Dedicated to Miemie bie 😘





2⃣5⃣




"Cikin jirgi Shukra sai bacci takeyi daga Zaunen da take, Safeer ne ya kwanto da ita jikinsa dan tafi jin dadin baccin"



"Ko da aka kawo musu abinci ma be karba ba don yasan Shukra bazata ciba, kuma dama shi bayajin yunwa, Cigaba da Aikinsa yayi har suka isa San Francisco "



" Jirginsu na landing Shukra ta farka tana raba ido, Mikarda ita safeer yayi suka sauko a tare "



" Wayarsa ya dauko ya shiga dialing number Ahmad, Wanda tana fara ringing ya dauka don dama sunyi waya da safeer ya fada masa sun kusa sauka "


" Mota Ahmad ya dauko yazo ya samesu a zaune kan resting chairs na airport din, safeer na ganinsa ya mike da fara 'arsa sukayi musabaha kafin suka gaida da Shukra "



" Nan ya kwashi trolley dinsu yasa a mota suma suka shiga suka kama hanyar gidan sa "


" sun samu tarba ta musamman gurin matarsa Azeeza, Yar Nigeria ce itama, bayan sun ci abinci ne kuma Safeer da Ahmad suka fita dan ganin inda za a gina Company 'n sukabar Azeeza da Shukra suna hira kamar dama can sun san juna "


" Har dare basu dawo ba, Abinda ya daga hankalin shukra kenan sosai take son ganin mijinta, wayarta ta dauka da niyyar kiransa sai kuma ta tuna batada number sa, Dan karamin tsaki taja kamar zatayi kuka wae batada number mijinta (Abin takaici) "



" Azeeza ganin dare yayi sosai kuma dawowar Ahmad ba yanzu ba yasa ta nunawa SHUKRA dakin da zata kwanta, Ita kuma ta shige nata, Zaman kusan awa biyu Shukra tayi amma shiru Safeer be dawo ba sbd hk ta shige daki kawai ta kwanta "


" Shiru tayi bayan ta kwanta zuciyar ta cike da tunanin Safeer, Batajin zata iya bacci ba a jikin Safeer ba juyi kawai take a kan gadon sam bacci ya ki zuwa, Ahaka dae bacci barawo ya kwashe ta "



" Cikin bacci taji ana shafa ta tai saurin bude ido don dama baccin beyi wani nisa ba "


" Cikeda shagwaba take kallon sa idonta taf da hawaye

"Ya Safeer shine kaje kayi zaman ko, Ka barni inata jiranka" Tafada tana fashewa da kuka


"Jawota yayi jikinsa yana bubbuga bayanta a hankali
"Yi hakuri Shukra cute kinki insha Allah gobe bazan dade ba yau dinma dan farko ne bakiga guraren da mukajeba, Amma wallahi kina raina sai tunanin ki nake"


"Murmushin jin dadi tayi ta kara shigewa jikinsa 'kaci abinci ya Safeer?


"Naci dazu Shukra yanzu wanka zanyi "



" A tare suka mike suka shiga toilet din ya tsaya a gefe ita kuma ta hada masa ruwan wanka "Bitayi jefensa zata wuce yayi saurin rike hannunta"

"Ina zakije kuma ya tambayeta kasa kasa yana kashe mata ido daya "

" Zanje in fito ma da kayane fa ta bashi Answer tana kokarin kwace hannunta "


" Kara damke hannun yayi 'ki bari muyi wankan mana "


" A a ya Safeer nifa nayi tun dazu "

" Ban yarda ba sai kin sake "


" Kasa cigaba da jayayya dashi tayi dan haka kawae sai ta rufo musu kofar toilet din ta dawo ciki "


" Safeer ne ya shiga ciremata kaya, ita ko kunya duk ta hana ta sukuni sai sunkuyar da kanta take, haka dae ya gama cire mata kayanta tsaf shima ya cire nasa ya hau jikata da ruwa "


" Itama jikashi ta fara yi suna dariya abinsu, A hk dae suka soma wanke junansu wanda tun Shukra na nokewa har sai da ta saki jiki "



" Safeer na gani ya fito daga toilet dauke da Shukra a hannunsa kamar wata baby ya nannade ta da towel, Karasawa yayi ya kwantar da ita a tsakiyar gadonsu sannan yaje inda trolley 'nsu ya dauko cream ya dawo kan gadon "


" Kunce towel din jikinta ya shiga yi inda Shukra ta runtse idonta, Shiko ko a jikinsa sai da ya cire mata towel din gaba daya sannan ya soma shafa mata cream din cikin wani salo me wuyar fassaruwa yake shafa mata, Shukra dai jinta tayi kamar ba a duniya wani irin abu ne taji yana yawo a jikinta, batasan lokacin data janyo hannun Safeer ba ya fada jikinta "


" Nan suka shiga kissing junansu cike da kaina wane zasu cinye kansu, Romancing kansu sukayi tayi kamar ba gobe, Niko ganin haka yasa na fito na barsu susha love "







" Washe gari tun 7:00am Safeer da Ahmad suka bar gidan har dare Shukra nata baza ido ba labarin Safeer, Hawaye ne ya cika idonta tanason ganin Safeer tana tsananin bukarsa, Gashi ta manta bata karbi number sa ba "


" Ganin kuka na neman cin karfinta yasata mikewa da sauri tashige daki, Kwantawa tayi kan gado ta rungume pillow tana kuka mara sauti "


" Karar wayarta ne ya katse mata kukanta, kamar bazata dauka dan saida yazama missed call ma sannan ta dago wayar ganin Aneesa ce me kira yasata saurin dialing "



" Ringing biyu Neesa tayi picking

"Hello Neesa luv ta fada can ciki"

"Shukra Y kk, Ya jikin kuma?

"Jikin me kuma Neesa nace miki banda lafiya ne?



"Muryanki ya fada min bakeba "


" Keni lafiya na kalau "



" uhmm, Yaushe zaki haihu ne Neesa ta tambaya tana dariya kasa kasa "


" Wani irin Haihuwa ana zaune kalau ae ni sainaci amarchi na kamar shekara 2or 3 kafin na fara haihuwa "



" Koba shekara biyu ko uku ba Neesa ta tambaya tana dariya sosai "


" Dariyar me kuma haka Shukra tace wane zatayi kuka "



" Jinayi kince shekara uku Shukra wa yasani ma ko yanzu kinanan da katon cikin ki, Zama da kyar tashi dakyar Aneesa ta bata answer "


" Dogon tsaki kafin ta kashe wayar ta ta kifa kanta jikin pillow ta cigaba da tunanin other half nata "



" Tanaji Neesa nata kiranta amma batabi takai ba ta cigaba da tunaninta tana addu a Allah yasa kar yau ya dade kamar jiya "



" To yau kam Su Safeer sun dawo da wuri dan agida sukayi sallar isha, Bayan sun idar sukaci abinci sannan kowannensu ya shige dakinsa "


" Shukra bako kunya ta tashi tabi bayan Safeer inda ta tarar harya shige toilet, Azeeza ma ganin Shukrah ta mike yasata itama mikewa tabi bayan Ahmad "



" Sai da Safeer ya kira Haiydar sukayi hira sosai, Sanda sukayi sallama ne Haiydar ya fara tambayar Safeer Shukra "


" Safeer ya dawo da kallon shi kan Shukrah dake kwance akasa ta nannade kafafunta da nashi kamar mejin sanyi,Gashin kanta ya rufe mata fuskarta, Hannu yasa ya ture Gashin gefe ya dago kanta, sai anan ya gane ashe ma bacci take, Nan dae ya fada ma Haiydar Shukrah tayi bacci sukayi sallama, sannan yayi wa Shukrah addu a shima yayi "


" Sai da Safeer da Ahmad sukayi kwana 5 basa zaman gida Shukrah har ta fara ramewa "


" Shukrah ce zaune kan abin sallah bayan ta idar da sallah azahar tana yiwa Safeer addu 'ar kariya, Jin datayi a turo kofar dakinsu yasata saurin dagowa "



" Ware ido tayi tana kallon sa da mamaki, Tunda sukazo san Francisco basu taba haduwa da rana ba "



" Fuskarta dauke da Murmushi ta karaso ta rungumeshi "


" Ya Safeer sannu da zuwa Shukrah tace tana riko hannunsa, Ta zaunar da shi a bakin gado ta haye cinyarsa bakinta yaki rufuwa dan dadi "

" Yawwa Shukra na sameki lafiya?

"Lafiya kalau, Ya Aikin?


"Alhamdulillahi, Aiki ma ankusa kammalawa "


" Masha Allah shiyasa yau kadawo da wuri knn"

"Eh mana, Gobe ma bazan fitaba zan kaiki yawo "


" Ihun murna Shukrah ta sa kafin ta mike taje ta hadawa Safeer ruwan wanka, Bayan ya shiga toilet ne ta fito masa da farar t-shirt da three quarter ta fesa musu perfume ta zauna tana jiran fitowarsa "


" Shukrah ce kwance kan jikin Safeer da alama bacci zasuyi "

" Kinsan irin son da nake miki kuwa Shukrah "

" Saurin sa tafin Hannunta na dama tayi ta toshe bakinsa 'Yi shiru Ya Safeer kayi bacci kaji "Shukrah ta fada tana harar sa


" Harshen sa yasa yana tsotsar tafin hannun nata, Bata janyeba haka bata hana saba, sai ma kwantar da kanta datayi a kirjinsa hade da lumshe ido, A haka dae bacci me dadi ya kwashe su............






SHUKRA YAR GATAN MIEMIE BIE 💞
[4/21, 9:01 AM] 🎀Shukra yar gatan miemie🎀: 👮🏻AUREN BAZATA 👮🏻




WRITTEN BY
ZAINAB YAKASAI
SHUKRA





Dedicated to Miemie bie 😘





2⃣6⃣




"Kamar yadda Safeer yayi wa Shukra Alkawari kan cewa ya yau baze fita ba haka kuwa akayi be fitan ba,"



"Bayan Sallar Azahar ne Safeer ke Sanar da Ahmad yana so ya fita da Shukra, Ahmad din kuma ya Amince ze zagaya dasu suga garin kamar yadda Safeer din ya bukata"



"Dukansu na gani a harabar Gidan cikin Shirin su na fita, Ahmad ya zauna a driver sit inda Safeer ya zauna a gaba Shukra da Azeeza kuma Suka zauna a baya "


" Mesium ya fara kaisu, Sannu a hankali yake musu bayan duk abinda suka gani,Bayan sun gama da Mesium ya daukesu ya kaisu San Francisco state University sosai suka zagaya a cikin University kafin suka fito suka tafi wani hadadden Restaurant nan Suka ci abinci suna ta hira abinsu, "


" Bayan sun fito ne Shukra taga wani dan Asibiti karami a gefe tace tanason shiga, Ae kuwa sai da suka shiga aka zagaya dasu, tayi kuma magana da wata likitan ido inda Shukra ke fada mata Optometry ta karanta, Sosai Doctor taji dadin Haduwa Da Shukra har tayi mata tayin Aiki cikin Asibitin, Shukra ta mata bayani kan cewa ita bakuwa ce a San Fancisco Aiki ne ya kawo mijinta, Sun dan taba hira kadan Sukayi Exchanging phone number daga nn sukayi Sallama Suka bar Asibitin "



" Koda Suka bar Asibitin ba gida Suka wuce ba Saida suka ce Bitch suka yi kalle kallensu sannan suka dawo gida da niyyar gobe zasuje San Fancisco state zoological garden "



" Koda Suka dawo Gidan Sallar isha kawae sukayi kasan cewar sunyi Magrib nan cikin Asibiti, Kwanciya Shukra tayi bacci me dadi ya dauketa, Shi kuma Safeer sai da Suka dade da Ahmad a Parlour suna magana kan Company kafin sukayi sallama kowa ya shige dakinsu "




" Bayan Safeer yayi shirin bacci ne ya kwanta kusa da Shukra yana ta binta da kallo kamar me Shirin gano wani abu a tare da ita, Kawai gani yayi ta kara haske tayi wani kyau, Idan har idonsa be masa karya ba ze iya cewa Shukra tayi kiba, To ko weather garin ta karbeta ne "


" Matsawa yayi sosai ya Rungumeta a jikinsa yana shafa ta sai yaji jikinta yayi santsi kamar jikin jariri, Ransa yana basa wani abu sai kawai ya share, Yana addu 'ar Allah yasa hasashensa ya zama gaskiya A haka dae bacci ya kwashe shi "



" Washe gari gurin sha daya bayan sun gama breakfast ne suka shirya sai Zoological Garden, Sosai gurin yayi wa Shukra kyau dan ko kusa bazaka hadasu da na Kano ba don iya shi ta taba zuwa "



" Riko Hannun Safeer Shukra tayi lokacin da Zuwa zo Gurin lion, Yana ganin su ya fara ihu yana tsalle kamar yana son fito, Shukra ta kankame Safeer a jikinta ta fasa masa kuka jikinta har wani rawa yake ta tsorata iya tsorata har bata iya jin abinda Safeer din ke ce mata "



" Sun dau Tsawon lokaci a haka Safeer sai shafa bayanta yake yana bata hakuri a Ransa kuma yana tunanin wannan irin tsoro na Shukra "


" Shukrah ce ta fara dagowa daga jikin Safeer ta kalle shi tana goge hawayen fuskarta
"Ya Safeer mu tafi gida Zazzabi nakeji"


"Sannu Shukra bari su Ahmad su Dawo sun dan za gaya can ne ya fada yana jan hannunta suka zauna "



" Riko shi tayi sosai don har yanzu a tsorace take Shima ganin hakan yasa shi Kwantar da ita kan kirjinsa yana buga bayanta a hankali, A haka su Ahmad suka dawo suka samesu inda Safeer yayi musu bayanin komai, Nan dae suka koma gida"




"Shukrah ce ta fara shiga gidan ta kwanta nan palour ta rufe idonta, A tare suka shigo dukkansu, Ahmad da Azeeza suka shige dakinsu Safeer kuma ya dauki Shukra cak ya kai daki ya kwantar "



" Sai wajen 3:20pm Shukra ta farka duk jikinta ba dadi ga Zazzabi ta rasa inda zatasa kanta taji dadi kawae sai tasaka kuka, Safeer yana toilet yajiyo kukan Shukra ya fito da Saurin sa ya hawo kan gadon inda take "



" Shukrah tayi Saurin fadawa jikinsa ya kankameshi kamar zata shiga cikin sa, Nan yaji jikinta yayi zafi sosai abin ya bashi tsoro, Yayi Saurin kwantar da ita ya fice daga dakin "



" Azeeza kadai ya samu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login