Showing 6001 words to 9000 words out of 60293 words

Chapter 3 - WATA BAKWAI BOOK COMPLETE by Lubna Sufyan.txt

19 Feb 2025

9157

Tasa hannu ta dafe kirjinta kaman yana mata ciwo.


*


Wani abu yaji ya tokare masa wuya wai wannan yarinyar me take ji dashine haka da zai mata magana ta share masa.


Yar wacece ita da kamar shi zai mata magana tai kaman bataji shi ba.


Muryarsa a dake can kasan makoshi yace mata


"bana magana amin shiru."


Miqewa tai da niyyar bar masa wajen gaba daya.


Cikin wani irin zafin nama yasha gabanta saida ya tsoratata.


Ganinta tai can like da kasa dan ta tabbata in fuskarshi zata kalla sai ta daga kai. Saboda dogo ne.


Kanta a faffadan kirjinshi ya tsaya.


Kanta ta sadda qasa bata san ganin shi batasan yana mata magana ba taqi ya fita harkarta ba ya kasa gane hakan.


"Matsa in wuce ta fada"


muryarta na rawa kanta a qasa.


"Look at me... ki bani amsar maganar danai miki"


Ya buqata yana zuba mata idanuwansa. Ji yake kamar ya kwada mata mari sai ta dago ta kalle shi.


Baya son maimaita magana. Ko yaita fadar abu daya ka kasa ganewa. Bata mishi rai hakan yakeyi ba kadan ba.


Wannan natacciyar yarinyar ta kasa gane level din hakurin shi yakai karshe.


Numfashi yake ja yana fitar dashi a tsanake ko zai controlling bacin ran da yake ciki.


Husna tana jin hawaye na shirin zubo mata. Sam bata son takura ya kasa gane takura mata yake.


Kaucewa tai ya sake tare hanyar yaga alama yarinyar nan tana gwada haqurinsa.


Batasan waye prince ishaq ba harda rashin huddy ya sake mayar dashi haka.


Shi ya sashi zama so cool din nan. Da kudi akace tai masa hakan ba zatayi ba.


Gab da ita ya kara matsawa yau kome take ji saita sauke shi ta kalli fuskarsa.


Yanajin hucin lumfashinta a kirjinsa.


*
Husna kam zuciyarta ci gaba tai da dokawa tunda take bata taba yin kusa da namijin daba muharraminta ba haka.


Ammar ne yake mata yawo a kwanyarta ga kuma qamshin natacce daya addabeta so take ya kauce ta wuce yaqi.


Taga alama inba abinda yace tayi ba bazai barta ba.


"Ba zani abuja ba kabani hanya in wuce."


Ta fada da sauri dan batason yaji yanda muryarta ke rawa.


Murmushi yai duk da baikai zuciyarsa ba.


"I didn't asked you ko zakije ne. Nace ki shirya. And ki kalle ni kibani amsa"


Ya fada idanuwansa nakanta.


Ta soma qulewa a hasale tana shirin yin kuka tace


"wai kai wanne irin natacce ne ka qyale ni nace ba zani ba!"


Kuma sam taki dago fuskarta ta kalle shi.


Lumshe idanuwanshi yai ya bude su a hankali. Akwai rigima kenan ya fada cikin zuciyarsa.


Hannunsa yasa ya dago mata haba cikin idanuwanta ya kalla.


Ji tai duk wani karfi na jikinta yana narkewa. Duk wata gaba ta jikinta ta mata sanyi.


"In kina so zaman lafiya you have to take note of three things.


Ba.amin magana cikin hargowa.


Bana magana aimun shiru.


Bakuma nason gardama da maimaita abu."


Ya karasa yana kallonta deel cikin idanuwa.


Husna tana jib dumin hannun shi dayake kan habbarta a ko ina na jikinta.


Kamar habar tata tana da wani dangantaka da sauran inda take jin dumin nakai mata.


Hannu takai da niyyar ture mishi nashi dai-dai lokacin da mararta ta wani irin murda mata sai da ta ji lumfashinta ya na neman daukewa.


Hannunshin da zata ture ta kama ta rike gam tana kiran


"Wayyo mamina...."


Ji tai abin bawai na wasa bane ta sake kama hannun shi ta riko dam tana yin kasa.


Takan sha wuya ba kadan ba lokacin period dinta sai dai yau saura kwana biyu take tsammani ga abin yazo mata a bazata.....!


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣7⃣


This one is for my mentor and my clients. Thank you for putting up with my shits.


Prince ishaq kam hannunta yabi da kallo da wani yanayi a fuskar shi.


Gani yai da gaske takeyi cikin alamar tsoro yace mata


"ke meya hakan wai?"


Ta ma kasa magana kawai wayyoo mami take kira ta dafe ciki da hannu daya. Dayan kuma ya rike da na prince ishaq dam.


Baya son ganin wani cikin yanayi. Hakan na tuna mishi abubuwa da yawa.


Tsugunnawa yai Allah ya zuba masa tausayi musamman ma mata.


Cikin damuwa yace


"Are you okay? wai meke damunki?"


Daqyar tace masa


"cikina..."


Wani abu da ya dade bai motsa ba a jikinsa yaji. Koma menene yafi karfin zuciyarshi.


Baisan lokacin daya kai hannun shi kan cikinta ba.


"Dai-dai ina yake ciwo? Murdawa yake? Zafi?"


Kaman bata masan yanayi ba. Pillow din kujera ya dauko ya ajiye kasa ya samu ya zame hannunshi daga nata.


Kamata yai ya kwantar.


"Stay right here"


ya fada ya mike da gudu har kafarshi ta taka step din farko na benen zai hau sama kawai kamar wanda aka dokawa guduma akai.


Ya tuna da alkawarin dayai ma kanshi na kin sake taba wani patient a rayuwarsa.


Na barin career din daya so tun yarintarshi. Fasawa yai. Ya sauko da kafarshi.


Wajen husna ya dawo da take kwance ta hade jikinta. Ya tsugunna. Muryarshi a tausa she yace mata.


"Sannu kinji bara na kira doctor? Or we should go to the hospital? Can you walk?


Girgiza masa kai tai muryarta can qasa tace.


"zai tafi basaika kira kowa ba."


Hade fuska yai yace


"Ban fada miki ba.amin musu ba? Ko yan aikin gidan nan ne basu da lafiya hospital ake kaisu."


Duk zafin ciwon da husna take ji bai hanata harararshi ba.


A ranta tace wato ko yan aikin gidan nan. Itama ai ba catai tana da wani matsayi ba. Kaman yanda bata gabanshi bata kuma san me yasa ya aurota ba. Haka itama baya gabanta.


Tana kallonshi.Wayar shi ya dauko tana jinsa ya kira.


A wajen ya zauna duk motsin da zatai zai mata sannu.


Har doc din ya qaraso.
Cike da girmamawa taji sun gaisa kuma ya kira shi da prince ishaq.


"Prince ishaq" ta maimaita. Daman sunan shi ishaq kenan.


Tambayoyi doc din ya soma jero mata yanayin amsarta yasa ya fahimci period ne takeyin nata mai wahala.


Yadan rubuta mata magunguna yace bawani abu bane period dinta ne zai dai-dai ta inta sha wannan magungunan.


Ya maida hankalinshi kan prince ishaq yace.


"You know the rest.... "


"I quit. Sau nawa kuke son in fada maku?"


Yai maganar da wani yanayi a muryarsa.


Murmushi kawai doc din yayi yana daukar jakarsa. Yace ma husna.


"Allah ya kara sauki"


Ta amsa da amin muryarta can kasa.


"ka tafi da prescription din saika sa a kawomana"


Prince ishaq ya buqata.


"Alright Nabarku lafiya"


Doc din ya fadi yana ficewa.


*


Kallonta yake a nutse.


"sannu ya fada a cikin sanyin murya."


Tana jin shi. Yanda idanuwansa ke mata yawo a jiki. Shiru kawai tayi masa.


Bata so yana mata magana. Ita dazai tashi yabarta ma da taso.


Jin tayi shiru ga idanuwanta a rufe ya sashi daukar tayi bacci.


Ya sauke wani dogon numfashi. Sam baya son matsala.


Auren nan matsala ne a wajen shi. Yanzun idan irin wannan yana faruwa shi ya zai yi ne?


Jin tunani zai haye masa yasa shi miqewa ya fita daga dakin.


Cikin hadiman gidan ya tura mata guda daya don shi baida lokacin dazai bata yana kula da ita tunda bashi ya ajiyeta ba.


Kawai dai wata irin zuciya gareshi idan yaga mata cikin rauninsu.


Sai yanzun ma kalamanta suke sosa mishi zuciya.


Ya rasa meyasa natacciya bata son kallon fuskarsa kuma bata shakkarsa shi.


Wato yanda yake kiranta natacciya shiya bata damar ce masa natacce.


Ko dayake yafi ganin laifin mai martaba a wannan karin.
Shi ya takura masa ya aura masa ita kaman yanda yanzun ma yasa shi tafiyar nan da ita..


Sam baya son daukar kaya don ya tabbata shi zata zame masa.


Abinda zaije yi abuja yana bukatar sirri kuma mai martaba yafi kowa sanin haka.


Dashi kadaine zai zauna hotel abinshi. In yaje gida mutanen da yawa na iya sanin yana garin abuja.


Dafe kai yai ya sauke numfashi dai-dai lokacin da wayarsa ta dauki qara alamar kira ya shigo..


Sanin kowa keda ringtone din yasa shi fito da wayar daga aljihunsa ya lumshe idanuwansa sannan ya dannan wayar ya kara a kunne.


"Yaya wacece wannan data dauke hankalinka haka? Kar kasa in tsaneta tun kafin inzo.....baka da lokacina sam."


Cewar nasir da yake maganar kamar zaiyi kuka.


Yasan babu macen da ta isa ta dauke mishi hankali daga kan kanin nasa koda huddy ce balle wannan natacciyar duk kyan da take dashi kuwa.


Kawai dai damuwa ce tai masa yawa.


"Haba mana nasir. Wacece ma ta isa? abubuwane sunmin yawa babu lokaci sosai amman everything is gonna be alright karka damu."


"Yaya sune ko? Ba zasu barmu mu huta ma ranmu bane wai? Ko in dawo gida?"


Prince ishaq zai iya jin tsantsar damuwar da nasir din ya shiga.


Don haka yai kasa da muryarshi yace.


"No! Ka tsaya ka gama exams dinka kana jina ko? I am okay! Komai zai tafi dai-dai in shaa Allah"


"To fadamun what is going on? " nasir ya bukata.


Prince ishaq ya dafe kai.Sanna yace.


"Drop it nasir. I am serious ka kyale maganar nan"


"Hmm"


kawai ya furta ya kashe wayar.


Prince ishaq ya soma tunanin kila dai saiya dinga rubuta abubuwan daya kamata yayi saboda yawan mantuwar da yake yi these days.


Ya saba kiranshi a kullum yaji lafiyarsa da yanda komai na rayuwarsa yake tafiya amman a satikan nan ko dan text din baya samun damar tura masa.


Bayan damuwar da take zuciyarsa baya buqatar wata damuwar kuma dan haka text kawai ya tura masa ya kwantar mada da hankali.


Ji yai iskar wajen ta masa kadan. Ji yake kamar kar nasir su gama exams dinsu ya dawo Nigeria.


Zaman shi a England yafi masa kwanciyar hankali. Yasan masu farautar ransu da son gadon mulkinsu duk abinsu zasu bar masa kaninsa in yana can nesa...


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣8⃣


This one is for you safiyya galadanci. And know that prince ishaq said yes to you being his lil sis. He LVY loads.


A big thank you to the readers. Writing this will be boring without you guys.


Asabe tai zaune a wajenta har doc din ya dawo da magungunan daqyar ta tashi tasha.


Bata jima ba ta samu bacci cike da mafarkin ammar dinta.


Bata farka ba sai da yammaci sosai. A hankali ta bude idanuwanta....yanayin yanda taji jikinta ne tasan cewa ta baci ta dan gyara kwanciya da niyyar tashi taga Asabe a zaune cikin ladabi.


Tasan ita ta shigo wajenta bayan fitar natacce.


"Badai tun dazun kina nan ba?"


Husna ta tambaya da mamaki a muryarta.


"Ranki ya dade ina nan koda zaki farka ki buqaci wani abu....ya jikin naki?" ta amsa a ladabce.


Ita kam bata son wannan girman da suke bata nauyinsa takeji a kunyace tace


"da sauqi zaki iya tafiya abinki nagode."


"Ki huta lafia"


Asabe ta fadi ta mike ta fice,ciwon da takeji yayi sauqi sosai tashi tai ta nufi dakinta.


Kanta tsaye toilet ta nufa ta soma yin wanka don ta tsaftace jikinta.


Ta wanke kayan data bata ta dauro towel ta fito.


Wata er jaka data zubo abubuwan da tasan zata buqata ta dauko Always dinta ta duba saura guda biyu.


Ta dauki daya ta shafa farin almiski a jiki saboda yana dauke karnin jini kuma yana maganin ciwon sanyi da qwayoyin cuta da dama.


Bayan ta gama shiryawa tunani take tasan dole ma ta fita shopping tana buqatar kanan abubuwa na amfani.


Tsaki taja a fili tasan ba zata taba tambayar natacce zuwa unguwa ba don bai kai wannan matsayin a wajenta ba.


Shiru tai tana sake sake. Dazun da mararta ke ciwo sai taji kamar yasa hannu ya taba mata ciki.


Wani zafi taji kirjinta nayi. Inba tsabar naci ba inama ruwanshi da ita da har zai taba mata ciki.


Tama manta shi nashi hannun data kama ta rukunkume.


Dan rainin hankali wato jibi zamu tafi abuja ta nanata a zuciyarta wallahi yama rainani ta furta a fili.


Inba raini ba shi yana ma da qafafuwan dazai kwaso yazo wajenta yana fada mata zaiyi wata tafiya kuma har ma da ita.


Tunda a nata tunanin bata ga me yasa zai sanar da itaba. Babu ruwanshi da ita. Ko gaisawa basu taba yi ba.


Sai tai kwanaki bata ganshi ba.


Tome zatai masa in sun tafi taren ko kuma dai salon ya qara takurata fiye da wacce take ciki ne a yanzun?


Gabanta taji ya fadi. Kar dai ace so yake sai sunje abuja yace zai hada shimfida da ita.


Tunanin hakan kawai yasa taji hawaye sun cika mata idanuwa. Goge su tai. Tana tuna alkawarin datai.


Cewar ba zata sake zubda ma auren nataccen nan hawayenta ba.


Ko me zai faru kuwa. Tadai san akwai rikici kwance in har abinda take tunani yai shirin faruwa.


Wata irin kewar ammar take ji kaman zuciyarta zata fito. Wayarta ta dauko.


Tun satin bikinta aka qwace wayoyinta duka aka bata wannan aka kuma sake mata sim babu number din kowa saita yan gida da kuma kausar.


Ta sake jin wata tsanar natacce a zuciyarta. So take taga karfe nawa. Dan tana son fita sosai.


Idonta yakai kan date din wayar. Jitai kanta ya wani sara. Lokaci daya wani irin jiri ya kwasheta.


"06-03-2015"


Bangon wajen ta dafa tana kiran


"Inalillahi wa ina ilaihi raji.un" babu adadi ko zuciyarta zata samu nutsuwa daga yanayin da ta shiga a wani bangaren kuma tunani yakaita wani lokaci can baya..............!


*** ***


Tana kwance kan gado wayarta ta dauki ruri.


Jin kidan kawai ya bayyana murmushi a fuskarta.


Dagawa tai ta kara a kunne hadi da yin sallama.


Ya amsa mata daga dayan bangaren ya dora da.


"Haba mana tawan. Sai anjamun aji za a daga wayar? "


Dariya tai wani son shi na sake shigarta tace.


"Nawan ni na isa kawai dai..... "


"Kawai dai me?" tanajin murmushin dake muryarshi.


Itama murmushin take a kunyace tace.


"Nayi kewarka ne nawan"


Ajiyar zuciya ya sauke da tanajinta har ta cikin wayar kamun yace.


"Idan na fadi nawa a fili zaiyi yawa tawan. In shaa Allah 06 ga watan 03 zan dawo"


Lumshe idanuwanta tai saboda hawayen da taji suna mata yawo.


Muryarta na rawa tace.


"Wata ukku kenan nawan"


Sai da yai jim sannan yace.


"Tawan ki mun addu.a ke dai. Randa na dawo ba zanyi awa biyu ba za.ai maganar aurenmu in shaa Allah."


Ba zata iya ci gaba da maganar ba. Dakyar tace.


"Nawan zamuyi waya anjima"


Shima shiru yai na wani lokaci kamun yace.


"Babu damuwa. Ina sonki sosai. Take care of you for me"


"You too" ta amsa tana ajiye wayar tasan zai kashe.......




💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣9⃣


This one is for you mumy bilkisu. Allah ya kara dankon soyayya da oga. Allah ya shirya yara ya musu albarka.


Cikinsa yaji yana masa qara kuma yasan yunwace tun tea din daya sha da safe bai kuma samun natsuwar qara saka ma cikinsa wani abuba.


Abinda ya kara bata mishi rai tunanin waccan natacxiyar yarinyar daya fado mishi cikin jerin muhimman tunanin daya kamata ace yanayi.


Fada ma kanshi yake cewar auren shi dayake kanta bashi ya nema ba. Saboda haka ba matsalar shi bace. Ya fita hakkinta tunda ya kira mata doc. Ya kuma tura a kula da ita.


So baiga dalilin dazaisa ace yana tunanin ko taji sauki ba. Duk da hakan ba bakon abu bane wajen shi in har akan marar lafiya ne.


Ita din daice baya so tana kutso mishi kai cikin tunani.


Bai baro inda yake ba sai bayan la.asar.


kansa tsaye dining room ya wuce.


Plantain da qwai yaci yasha fresh milk ya fito.


Dakin shi ya shiga ya watsa ruwa ya saka wani farin yadi marar nauyi. Tunawa yai a dining yabar keys dinsa ya fita ya dauko.


A babban falo ya hadu da natacciya kallo daya yai mata zuciyarshi ta wani harba.


Rabon dayaji ta numfasa masa haka tun huddy.


Tayi kyau duk da bayason fadar haka cikin doguwar rigarta abuja style daurin dankwalinta simple sai mayafi.


Tunda can yana son yaga mace cikin shigar kaya purple kowanne irine.


Lokaci daya yaja wata qatuwar qofa ya kulle zuciyarsa baima san yanda akai qofar ta soma budewa ba.


Da alama fita zatayi don akwai qaramin mayafi a jikinta tasa shade shima purple.


Cike da mamaki yake kallonta....kaman koda yaushe kanta a qasa ko inda yake bata kallaba asali ma rabawa tai ta wuce kamar baya wajen.


Ficewa tai abinta.


Murmushi yaji ya qwace masa ya jima rabon dayaji ya bayyana a fuskarsa haka kawai inba mahaifiyarsa yake tare da ita ba ko suna waya da qaninsa..


Yasan ko qofar farko ba zata wuce ba,babu wanda ya isa ya bude mata gate batare da izininsa ba.


*


Hanyo yi taita bi. Bata san gidan nada girma haka ba sai yau.


Daya daga cikin hadiman gidan ta sa ta rakata har kofar gidan.


Sai da ta ganta a wajen

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login