Showing 30001 words to 30540 words out of 30540 words

Chapter 11 - Kuyanga Book Complete by Nabilancy Love.pdf

ance abinda ta Haifa yarasu

Yarima yace " Eh, Sunkusa Aure da LAMIDO...

SAHABI yakatseshi da sauri "ya akai hakan dama soyayya sukeyi?

Nan yarima yazayyane masa komai

SAHABI yace " Gud ammafa naji dadi LAMIDO yaburgeni Allah yasanya Alheri

Yarima baikulaba yai masa sallama

Acan kasan ransa soyayyar Zeenatu na nan baxai mantawa

******
Anata shirye shiryen biki akowane bangaren

Shi yarima agidansa na cikin gari zai zauna baiyda ra,ayin zama acikin gidansu wai kada
atakura masa shida amaryarsa

Shiko LAMIDO sashi guda aka gyara masa agidan me dauke da dakuna agidan gidan yasha
gyara babbane dama ba kowa ciki

Aka zuba komai na alfarma agidan

Lefe yazo daga Dubai akwatuna goma Sha biyu cike fal da kaya tsadaddu

Komai dozinne ciki koina acikin gidan da wajen gidan zancen kayan lefensa akeyi domin
sunhadu sunburge kowa

Saida aka kaiwa takawa yagani yace sunyi yasa albarka kana mata suka hadu suka dauka
bayan Su MAMAH DA FAATU sun gani aka kaiwa KUYANGA

Tsoffinsu sunsaka albarka sunyaba Angyagije Zeenatu anfiddata kunya dukda sunsan arina

Shiko Yarima karya yahada ackn kayan duk don ace nashi sunfi na LAMIDO

Harda key din mota yasaka akan lefen mahaifiyarsa ta saka takardun gida duk akan lefen
gudummawarta duk don mutane suga na LAMIDO lami ne sannan su burge mutan Kaduna



Amarya anata rawar kai anatashan magungunan karin Ni,IMA da tsukewa sbd gurin anshigeshi

Tun fara karatunta a Abroad tayi soyayya da wani Anwar yamaisheta tamkar mata ta amince
masa daga baya ya yaudareta yana gama karatu yakoma kasarsu yamance da ita

Shiyasa data hadu da yarima takasa ta tsare saida taga natsaida lokacin Aure sannan
hankalinta yakwanta

Duk kashe kudin da akai alefenta baisa sunyi rawar jiki ko an yababa tunda su ba farin shigar
komai bane ita kanta motocinta biyu na hawa tanada gidaje kuma

Aiko dai yan kawo kaya suka koma jiki asanyaye danma anbasu tukuici me tsoka

Rana bata karya saidai uwar diya taji kunya

Allah yakawomu wannan rana

Ranar Asabar takama ranar daurin Auren da nadin sarautar

Ancika agdn sarki anata kade kade da bushe Bushe da algaita LAMIDO yasha kwalliyar
sarakai

Yayinda yarima yai tashi ta angwaye daidai misali ba yabo ba fallasa yasha tsadaddiyar shadda
babbar Riga d yar ciki

Saida akayi nadi LAMIDO yazama sarki sannan aka daura auransa da KUYANGA kana akayi
shagulgula sannan wasu suka dunguma da angoma Yarima suka tafi daurin Aurensa Kaduna

Andauro Aure antaho da Amarya a ranar domin sai dare suka iso aka ajiyeta a gidansa dake
GRA

Itako KUYANGA data tashi daga wannan suna daga yau ta tare ackn gidan sarkin A gidan
mijinta LAMIDO daya zamo sarki ayau



To fans saimu Tara a page din gaba *GIMBIYA ZEENATU* Cigaban KUYANGA

Wanda zakuji badaqala da cakwakiya ackn Wanda nake muku zaton yafi wannan Dan haka
kada kubari abaku labari

Taku har kullum Auntyn Sayyada da Shahida

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login