Showing 33001 words to 36000 words out of 47324 words
yammaci lkcn, hankalinta ya tashi ma2ka
amma da yake tana da nutsuwa a dan lkc ta
fara rarrashina da kalamai masu dadi da saka
nutsuwa sai dai ina!!
bata sami kaina ba saima wani kuka daya kara
turnuke ni.
Mufida ta rasa yadda zatai dani tadan rike
kafaduna tare da cewa “HUMAIRA!! wai me
kike so ki zama ne??
Ke ba zaki iya jurar kaddara ba kenan??
Ko kina zaton Haka kawai Allah zai bar
bawansa ba jarraba ba.
kuma gsky ta fada fa 2nda faruk dai ba
mutuwa yayi ba amma yakamata tasan ba
yadda za‘ai koda ciwon kai ya sami faruk
hankalina ya kwanta bare hali irin wannan.
daga karshe dai na roketa alfarma da taje gd
ta dauko mana wasu abubuwan da zamu
bukata, tako mike tare da tambayata ina
mukullayen gdn??
Na dan kauda kaina kawai a raina nace gsky
wannan ta samu matsala, a ina na sami
nutsuwar daukar wani mukulli??
Zuwa jimawa na dubeta da shakakkiyar
muryata nace “kije kawai komai a bude yake.“
Ta dan bini da kll kawai tare da girgiza kai
cike da tausayawa ta juya ta fice.
Naja kujerata izuwa fuskantar faruk nayi
tagumi kawai, ji nake inama nice a kwance
bashi ba!!
Ina ma ni masifa ta riska bashi ba!!
ina ma nice hakan ta faru dani bashi ba!!
Sai byn wasu lkt mufida ta dawo, nazir da
abkn faruk su uku suka zo, momi ma ba shiri
ta bazamo.
Likitan dake kula da faruk ma yayi bayani
gamsashshe daya kwantar min da hankali
ma2ka, a cewarsa ‘faruk bai sami wata
matsala ba saboda kaf ilahirin jikinsa kalau
yake iya kansa ne kawai yadan sami buguwa
da karfen motar da sukai hatsari akanta shine
ma dalilin saka bandejin dake kansa sbd suna
tsammanin ko akwai inda ya fashe kuma babu
ma hkn yasa bayan wani lokaci suka cire,
akwai yiwuwar farfadowarsa nan da wayewar
gari.‘
Hakan yasa nadan ji sanyi a raina sosai, tbbs
abin yazo da sauki sosai nima na yarda da
hakan.
Gefe guda momi dasu nazir AL‘AJABI ya
ma2kar turnikesu ganin yadda nake taka
kafata tamkar bani ba, na fahimci momi nason
tambayata shiru dai kawai tayi.
Sanda dare ya tsala sannan ne duk suka tafi
ya rage ni da faruk kawai sai kayayyakinmu
daga gefe guda kuma y‘ar hayaniya na tasowa
daga waje da yake dakin da muke na
musamman ne ba kowa a cknsa sai kuma
nurses dake ta kaiwa da komowa don ganin
komai ya tafi dai-dai.
Na koma daga can gefen gadonsa na shimfida
darduma na fara sallolin nafil-fili da addu‘o‘in
samun sauki ga abin alfaharina guda daya tak
a duniya, Allah yasa yadda muke tsammani ya
zama haka ne.
Addu‘ar dana kwana inayi kenan don ban iya
runtsawa ba a daren.
*WASHE GARI*
misalin karfe 10:00 na safiyar ina zaune a
kasa bisa shimfidar da nayi nayi tagumi kawai
kusan hankalina baya jikina na tafi duniyar
2nani, gwauron numfashin da aka kawo yasa
ni dawowa hayyacina na dago kai da sauri na
dubi inda sautin ya fito.
FARUK ya farfado!!
abnd na fara fada a zuciyata kenan, nayi
zumbur na mike na zauna a gefensa.
fuskata tadan fara saki sanda na tbbtr da abnd
nake zato, a hnkl idanunsa suka bude sosai ya
yunkura ya mike zaune wani murmushi hade
da hawaye suka ziyarceni nadan kawo
gwauron numfashi tare da hada hannuna ckn
nasa.
Yace “HUMAIRA“ na amsa da “na‘am FARUK!!“
Meya faru dani haka ne??
A ina nake??
kina ina ne ba fitila a inda muke ne?? Nayi
saurin sakin hannunsa kirjina ya buga da karfi,
kaina ya sara tamkar kwakwalwata zata
rushe.
Ba kaganni bane??
Rikici kenan...anya kuwa..
Komeyasameshi..???
*WASHE GARI*
misalin karfe 10:00 na safiyar ina zaune a
kasa bisa shimfidar da nayi nayi tagumi kawai
kusan hankalina baya jikina na tafi duniyar
2nani, gwauron numfashin da aka kawo yasa
ni dawowa hayyacina na dago kai da sauri na
dubi inda sautin ya fito.
FARUK ya farfado!!
abnd na fara fada a zuciyata kenan, nayi
zumbur na mike na zauna a gefensa.
fuskata tadan fara saki sanda na tbbtr da abnd
nake zato, a hnkl idanunsa suka bude sosai ya
yunkura ya mike zaune wani murmushi hade
da hawaye suka ziyarceni nadan kawo
gwauron numfashi tare da hada hannuna ckn
nasa.
Yace “HUMAIRA“ na amsa da “na‘am FARUK!!“
Meya faru dani haka ne??
A ina nake??
kina ina ne ba fitila a inda muke ne?? Nayi
saurin sakin hannunsa kirjina ya buga da karfi,
kaina ya sara tamkar kwakwalwata zata
rushe.
Ba kaganni bane?? gani a gabanka.
Ya mitstsike idanunsa ya rufesu tare da
budewa ya grgz kai yace “wallahi bana ganin
komai sai duhu, meya faru dani ne haka??
Ya fada yana murza idanunsa.
Caraf naji hannuna biyu a kaina sbd tashin
hankali na dubeshi sosai idanunsa fa a bude
suke garau ba wani ciwo a tare dasu tayaya
ma za‘a ce baya ganin komai??
Na fadawa kaina.
Faruk da gaske kake??
Ya kara kikkifta yace “na daina gani fa
humaira!!“ Ya koma ta baya ya zauna ya dafe
kai tare da fadin “YA SALAM!!“
Na daki tsakiyar kaina da karfi na fashe da
kuka, wani irin tashi nayo waje da gudu izuwa
inda na hakikance nan ne ofis din babban
likitan dake kula da wajen, dakyar kuka ya
barni na fada masa abnd ke faruwa.
Da hanzari kuwa ya taso muka dawo dakin ya
fara jerowa faruk tambayoyi jimawa kadan ya
zare glass din dake idonsa yace “innalillahi wa
înna ilaihir raji‘un“, ya shafi gashin kansa.
Ni kuwa kara kaina nayi a jkn bango kawai
naci gaba da dankarar kukana, dai-dai lkcnne
momi da daddy suka shigo da sllmrsu.
A hankali suka karaso a sanyaye abin
mamakine a garesu ganin faruk ya mike harma
yana a zaune amma ina kuka maimakon
murna, lfy meye ya faru??
Daddy yayi saurin fada.
Na kasa cewa komai don bakina bazai iya mgn
a yanzu ba.
Ckn girgiza kai na jimami lktn yace “akwai
matsala zancen nan da muke daku patient
dinku idanunsa basa iya gani ko kadan, sbd
firgita ledar dake hannun momi subucewa tayi.
daddy kansa har wani ja baya yayi tare da
fadin
what??????
Ya daina gani??
To tayaya???
Ka sameni a ofis.
likitan ya fada tare da wucewa, jikin daddy
yayi sanyi ma2ka musamman daya dubeni ya
kuma dubi faruk wanda ke zaune bisa gado, a
hankali tamkar wanda kaza ta fashewa a ciki
daddy yabi bayan likitan momi kuwa zama
kawai tayi a zuba tagumi.
*doctor tayaya idanun mu2m zasu daina gani
alhalin suna a bude lfy ba abinda ya samesu??
Tambayar da daddy ya fara jefawa likitan
kenan.
ya gyara zama tare da cewa “wato Alhaji gani
bawai ya ta‘allaka akan ido ne kawai ba
amma kwakwalwa ita ke taka rawa wajen
tbbtr da ganin...“
Tayaya??
Daddy yayi saurin katseshi.
likitan ya dora da fadin “ta hanyar jijiyar dake
sanar mata cewa ido yaga wani abu sannan ta
tantance me aka gani din, ba ido kawai ba
harta kunne idan magana ta shigeshi sai an
sanarwa da kwakwalwa cewa anji wata
magana ta tantance abnd aka ji snn a gane
anji maganar.
Duk sanda aka ce jijiyar dake sanarwa
kwakwalwa wani abu da aka gani ta sami
matsala to tbbs makanta ta samu kmr yadda
nake da tbbcin abinda ya faru gareshi kenan
ta silar buguwar da yayi akai.
daddy ya kauda kai ckn mamaki da fadin
“buguwa akai matsala a ido.“
Kwarai kuwa “sbd abin ya taba mahadar
idanun da kwakwalwa ne.
Daddy ya dan dafa tebirin dake gbnsa yace
“kaga doctor yaron nan mijin y‘ata ne a shirye
nake na biya ko nawa ne akansa, abinyi??“
farin siririn likitan ya grgz kai tare da cewa “ba
wani abinyi Alhaji sbd shi sha‘anin kwakwalwa
ba yadda aka iya sai dai a tsaya aga ikon
Allah kawai.
Allah me yadda yaso wai a kasa da 24hrs me
gani ya zama makaho.
A snyyn da naga daddy ya dawo ne yasa ni
matsowa izuwa inda yake nasha gbnsa tare da
fadin “Shikenan ya makance ko??
ya daina gani har abada??
Ya zama....
Na kasa karasa maganar ta sarke min, lkc
guda wata bugawa da kaina yayi yasa na
sulale kasa sumammiya.
*******
Nan fa hankalin kowa ya kara tashi komai ya
kara rikicewa, sai dana shafe tsawon lkc
bansan a inda kaina yake ba.
A cinyar momi na farfado mufida na tsaye a
kaina tana yimin fifita, na cilla idanuna sashe
zuwa sashe lkc guda na dago kaina izuwa
mikewa zaune na zarce da kuka.
Momi ta jawoni jikinta ta fara rarrashina,
daddy da sauran mutane na zazzaune kowa ya
zuba tagumi suma suka shiga bani baki ciki
akan kaddara idan tazo ba yadda aka iya da
ita.
*Kwanaki biyu kacal muka shafe aka sallame
mu muka bar asibitin muka koma gida, daga
nan ne kuma wata sabuwar dagulalliyar
rayuwa ta fara, abubuwa da yawa suka sauya
izuwa bai-bai ba yadda suke tafiya a baya ba.
Aikin da faruk keyi dole tasa ya hakura domin
bazai yiwu babu idanu ba kuma gashi ba kmr
aikin gwamnati ba aikine da idan zaka iya ayi
dakai idan ba zaka iya ba shikenan an ajeka
babu saran samun komai, gashi kuma ummin
faruk bata nan kuma duk wasu kadarori da
dan abinda faruk keda shi suna hannunta.
Hakan yasa a dan kankanin lkc muka fara
shiga matsanancin yanayi sai da takai wani
lkcn abinci ma dakyar muke ci, wani lkcn sai
dai abokan faruk su taimaka mana.
Ina son na sanar da daddy don ya taimaka
mana amma faruk yace Na bari kawai mu kara
hakuri umminsa na gaf da dawowa komai
zaizo karshe, kuma dai nima din bana son
sanar musu sbd ina tsoron abnd ka iya biyo
baya.
Kamar yadda na saba ina ckn kitchen ina
sarrafa dan abnd zamu ci na tsaye nake na
dafa wani table dake gabana na tafi duniyar
dana saba zuwa wato TUNANI, gaba daya
hankalina ba‘a kan girkin ma da nakeyi yake
ba. alamun zamewa data faduwar da naji yasa
na dawo hayyacina tare dayo waje da sauri
izuwa falon, abnd kuwa nake zatone faruk ne
sai dai baije kasa duka ba. Nayi saurin rike
hannunsa nace “sannu! baka ji ciwo badai??“
Ya danyi murmushi tare da fadin “Ah ba abnd
naji karki damu.“ Ya mike tsaye.
Na jawo yar karamar bakar sandarsa na
makala a hannunsa muka tsaya a haka nace
“kayi hakuri laifinane danayi nisa ban dawo da
wuri ba.
Harka gaji da zaman kadaici kayi yunkurin
fitowa.“
Ya grgz kai tare da yin murmushin da koda
yaushe kuma a ko wane yanayi ya saba yi
yace “baki da laifi nine da karambani.“
Nayi masa jagora izuwa kan kujera na dubeshi
nace “bari naje kitchen ko?? mintu biyu kawai.
Ya gyada kai kawai, Na mike na koma.
Bayan na gama ne na zubo abincin wani dan
plate na dawo falon.
Zaune muke faruk nacin abncn muna hira ckn
nutsuwa, mun fuskanci juna ina lura da yadda
yake kai abncn bakinsa.
Ya dago kai yace “da alama fa ba cin abncn
nan kike ba??“
uhm! so nake kai dai ka gama tukunna.“
yayi shiru zuwa can ya grgz kai yace
“HUMAIRA ina tausayinki gsky kina shan
wahala ba karama ba...“
Nayi saurin katseshi nace “ka daina fadan
haka don Allah, abnd nake yima ne zai zama
wahala??
Ban taba klln abinda zanyi maka a matsayin
me wahala ba koyaya yake kuwa sbd ka
cncnci fiye da haka, Zanci gaba kuma da yima
iya iyawata har abada.“
Yayi murmushi kawai kmr zai ce wani abu sai
na kautar da maganar da wani zancen.
Bayan ya gama ne na jawo jarida sabuwa na
fara karanta masa halin da duniya ke ciki, idan
muka zo kan wani lbrn na ban dariya muyi
tare.
Sallamar da muka ji ce ta dawo da
hankalinmu, gabana ya fadi da naga momi ta
tsaya tana yi mana wani kallo ta tako a
hankali izuwa ciki.
Sannu da zuwa momi!!
Na fada dai-dai sanda faruk yayi saurin sakin
fuska da fadin “Ah! momi ce sannu da zuwa.“
A ynyn fuskarta nasan da matsala, sama-
sama suka gaisa da faruk na tashi nayi masa
jagora izuwa daki na dawo falon na zauna.
KE HUMAIRA!!!!!
momi ta fada sanda ta gyara zamanta a kjrr
da take zaune tare da dubana sosai.
Na dago kai nace “Na‘am“.
Momi tace “Wai baki da lafiyane naga duk kin
wani rame kin kanjame kin lalace??“
Na dan dubi jikina nace “rama kuma?? lfyta
kalau momi ba abnd ke damuna.“
Ah karya kike akwai, idan ba rashin lfy ba to
yunwa ko wahala akwai daya.“
hmm... Na gama gane inda ta dosa, na grgz
kai nace “ni dai-dai nake kuma ina ckn farin
ciki sosai.“
Karya kike akwai wani abu, kodai baki da lfy
ko kuma akwai yunwa a tare dake ko kuma
wahala me tsanani.
Na bita da kll kawai, ta dora da cewa
“tsakaninki da Allah kina cin abinci sau uku a
rana??“
Kina samun cikakken hutu koda na awa biyu
ne a rana??
Kina samun wani farin ciki a irin wannan
zaman??“
Nadan yi baya da kaina nace “To momi meya
kawo wadannan tambayoyin kuma??
Koda ina samu ko bana samu nan fa gdn
mijina ne ina da inda yafi nan ne??“
Kina dashi.
Tayi saurin cewa ta zarce da fadin “Duk
zaman dazai zama da kwarar juna irin wannan
to bashi da wani amfani don haka dole a samu
mafita akan haka don ba zamu zuba ido
wahala na neman kasheki a banza ba.“
Wani takaici ya rufeni na dauke kaina nace
“Banyi zaton jin haka daga gareki ba ko kadan,
a zatona kwarin gwiwa zaki bani akan kula da
faruk amma ba wadannan maganganun ba.
Haba momi faruk fa!!
Eh naji faruk sai me??
Ta fada tana dubana.
Na grgz kai nace “Toni bana daga ckn butulu
masu manta alheri a dan kankanin lkc, nidai
naji na gani kuma na gamsu zan iya koda
kuwa zan mu2 ne akan haka.
Momi tace “ke yarinyace da kike da kuruciyarki
sosai kula da makaho a gurinki ba karamar
masifa bace da zata iya sawa ki tsufa 2n kina
yarinya kada ki cuci kanki munyi magana da
daddynki dole ma asan abinyi.
Idanuna suka zaro waje kmr zasu fado, abnd
na dade ina tsoro kenan nasan zaiyi wuya
hakan bata faru ba.
Na sauka daga kan kujerar da nake na sauka
kasa na kwantar da muryata nace “Momi kada
kuyi haka don Allah, ki 2na abinda faruk yayi
mana bai kamata muyi masa haka ba, ni zan
jure koma menene.
Momi ta mike tace “kinga ana auna me zai zo
ne gaba ba abnd ya wuce ba, ba wanda zai
yarda yabar y‘arsa me gata gaba da baya a
yanayin da kike ciki da sake.“
Momi ki tsaya ki fahimceni.
Na fahimceki mana amma kiyi fatan daddynki
ya fahimceki idan ya ganki a wannan yanayin.
Ta fada tare da juyawa ta fice.
Na koma da baya na jingina da kujerar dake
bayana, tunane-tunane suka fara kaiwa da
komowa a zucita.
Abu daya dana sani duk rintsi ba wani dalili
dazaisa na rabu da faruk.
(Hmm za'ai butulci kenan)
Abin ya ma2kar dauremin kai, banyi
tsammanin jin haka daga momi a dan
kankanin lkc haka ba.
Na dade a zaune nayi tagumi kawai abin
duniya ya isheni, dakyar na iya mikewa na
koma daki, faruk na kishingide akan gado
idonsa dake sanye da bakin glass na klln
sama.
Na zauna gaf dashi, meye kike kuka??
Ya tambaya.
Nima nayi saurin tambayarsa da cewa “kuka
kuma??“
Na shafa kuma2na, yes gsky ya fada akwai
hawaye na grgz kai nace “ba kuka nake ba.“
Ya za‘ai momi tazo da magana me zafi, daci
da ciwo irin wannan kice ba zakiyi kuka ba??
ya sake jefo min tambaya.
Na kauda kaina a zcyt nace “dama yaji abnd
ya faru??“
Ya sauke kansa kasa yace “Watakila shikenan
lkcn rabuwarmu yazo, duk ginin da mukai a
baya ya rushe!! Sababbin hawaye sukayi
saurin gangaromin, na kwantar da murya nace
“Faruk idan kana fadan haka sai nayi zaton ko
baka da kwarin gwiwa akaina ne, ina so ka
yarda ba abnd zai rabamu har abada.
Ka yarda da haka. muka danyi shiru na wani
lkc ya gyada kai tare da cewa “Na dade da
yarda amma akwai tarin kalubale akan
yiwuwar hakan.
Sautin kukana ya sake fitowa na kwantar da
kaina kawai.
*BAYAN KWANAKI UKU*
Misalin karfe takwas na dare bayan mun gama
komai faruk ya dubeni yace “kyau kije ki
kwanta ki huta duk yau fa baki samu wani hu2
ba, na kada kai nace “badai ina tare da kai
ba??
Shine morewar tawa ai.“
Duk da haka dai hutu ma wani abu ne.
ya fada.
duk da bana son tashi amma sai da ya
lallabeni na mike na tafi daki, da yake a gajiye
nake sosai ina kwanciya barci ya kwasheni.
Faruk na zaune jim kadan da tashi na kamar
daga sama daddy ya fado da zazzafar
sallamarsa data sanya faruk saurin dagowa
bai iya amsawa ba har sai da daddy ya zauna.
Sannu da zuwa Alhaji.
Ya gyara zama sosai akan kujera ckn gadara
yace “Yauwa“.
Shiru ya gudana tsakaninsu nadan lkc zuwa
can faruk yadanyi kmr zai mike tare da cewa
“bari na taso humairan tana ciki.
A‘A yayi saurin dakatar dashi kana yace
“Wajenka nazo ba ita ba.“
A hnkl faruk ya koma ya zauna tare da cewa
Allah yasa dai lfy?
Ka taba ganina a gdnku??
daddy ya tambaya ya dora da fadin “To 2nda
ka ganni yau ka hakikance dole da dalili.“
Yadanyi shiru yabi da komai da komai na falon
da kallo a wulakance yace “Ah duk halin da
ake ciki lbr yazo kunnena kuma banyi mamaki
ba don nasan dole haka zata faru.
Sanin kanka ne yanzu ka zama misaki,
nakasashshe kuma makaho ba abinda kake iya
yiwa kanka bare kayiwa wani ba.
Hakan yasa ba zaka iya rike humaira ba a
halin da kake ciki kuma kai kanka kasan haka,
Naso ace ku zauna na har abada sbd yadda