Showing 36001 words to 39000 words out of 47324 words
kuke son junanku musamman irin halaccin da
kayi mata to amma magana ta gsky hakan ba
zata samu ba.
A matsayinmu na iyayenta ba zamu zuba ido
muna gani y‘armu ta kaskance ta lalace
karshe ta mu2 a wahale ba.
Don haka ina me umartarka da lallai ka
sawwakewa humaira ba tare da bata lkc ko
jinkiri ba.“
sbd grgz a firgice faruk ya dago kai duk da ba
iya ganin komai yake ba amma sai daya mayar
da fuskarsa zuwa inda yake 2nanin cewa anan
daddy ke zaune, fuskarsa ta canja ma2ka
bakinsa na rawa yace “Alhaji! wannan
maganar da kazo min da ita ta ma2kar
gigitani!!
Don girman Allah ka taimakeni kada ka rabani
da humaira, duk duniya Allah ne gatana
humaira ce gatana ita kadai ke taimako na don
Allah....“
Wannan ba wani abin damuwa bane, akwai
kudi dazan baka wadanda sun isheka ka auri
mata hudu ma idan kana so su kula dakai
nidai bukatata ka sakar min y‘ata ban haifeta
don irin wannan wahalar ba.
daddy ya fada.
Faruk ya grgz kai yace “kome zaka bani kuma
komai yawansa baikai muhimmanci da kimar
humaira a idona ba kuma idan ina dashi zan
iya sadaukar dashi akanta, ka rike koma meye
nidai ka barmu tare don Allah.“
daddy ya kara bata rai yace “bawai nazo ne
muyita wani doguwar muhawara dakai ba so
nake yadda kazo gida na dauki y‘ata na baka
to ka dawo min da y‘ata gida.“
faruk ya grgz kai yace “To kuwa bazan taba
iya yin abnd kake so ba.“
Da sauri daddy ya dubi faruk ya maimaita
abnd ya fada ckn salona tambaya, kace ba
zaka iya ba??
daddy ya mike tare da cewa “kuskure mafi grm
da zakai a rywrk shine kaki sakar min
y‘ata.Dama can ba tsararka bace na amince
ka auretane kawai sbd irin larurar data shiga
amma kaima kasani badon ka cancanta ka
aureta bane.
Na baka 24hrs kacal lallai ka dawo min da
y‘ata gida ko kuma kaga abnd zanyi maka.
Idan kunne yaji......“ Ya juya ya fice.
Faruk ya dafe kai ckn tsananin takaici
innalillahi...... bakinsa yama gaza kai karshen
addu‘ar daya faro.
Yadau tsawon lkc a zaune bayan tsawon
min2na ne kuma ya lalubi sandarsa tare da
mikewa ya taho a hankali ya shigo daki, takun
tafiyarsa ne ya tasheni daga barcin da nake,
nayi saurin tashi na bishi da kll, duk da yadda
yake so ya boye damuwar dake ransa sai data
fito.
Yana zama na fara da tambayarsa “meye ya
faru kuma??“
Yadanyi yake da cewa “kinga wani abune??“
Na gyada kai nace “tbbs akwai damuwa.“
Ya dan gyara zama yace “daddynki ne yazo!!“
Nayi saurin zabura, daddy?? me yace??
Ya kukai dashi??
faruk ya grgz kai yace “bai kamata kiji ba sbd
bashi da dadin ji.“
Na sani abu me dadi bazai kawo daddy ckn
gdn nan ba amma duk da haka zanso ji, don
Allah me yace??
Kmr bazai ce komai ba zuwa can yace “Ya
bani wa‘adin awanni 24 lallai na....“
2n kafin ya karasa na katseshi da cewa
“awanni 24??“
hmm... Tayaya yake zaton zama na har abada
za‘a kawo karshensa ckn awa 24??
Kayi hakuri mijina wannan tatsuniyace kawai.“
Duk da yadda naso na nuna ba wani damuwa
amma ni kaina a zuciyata nasan karya nake,
bansan yadda zanyi da wannan kalar masifar
data sake tinkaromu.
*** Sai byn kwanaki biyu da yammaci muna
zaune da faruk muna hira, kamar dirar mikiya
daddy ya fado, juyowa daya nayi muka hada
ido naja da baya a tsorace tare da cewa
“Innalillahi!!“
Meye?? waye??
faruk ya tambaya.
Ubankane!!!!!
Daddy yayi saurin fada 2n kafin nace komai.
Me nace maka??
Yaya mukai dakai??
ya tambayi faruk yana dubansa a fusace, ya
dora da fadin “to yau ko kana so ko baka so
sai y‘ata ta dawo gida tare muke da yan
sanda na shigar da kararka sai munyi shari‘a
dakai.
ya juyo gareni ckn tsawa yace “uban me kike
yi anan?? wuce mu tafi.“
wayyo faruq kadebo ruwan dafa kanka..!
A maimakon na iya cika umarnin da daddy ke
bani sai na tsaya ina binshi da kallo kawai,
idan na dubeshi sai kuma na juya na dubi
faruk dake tsaye ya kasa cewa komai na tbbtr
kunnuwansa a bude suke yaji abnd zan iya yi.
Alkawarin dana daukarwa kaina na kasancewa
da faruk a duk yanayin da yake ciki yasa duk
wani tsoro yakau daga zcyta, ni ban wuce na
tafi kmr yadda daddy ke cewa ba kuma bance
komai ba har sai daya kara buga min tsawa a
karona biyu.
“Ki wuce mu tafi nace“.
Maganar ta daki kwakwalwata, yaune karon
farko da daddy ke daka min tsawa kai tsaye
haka amma maimakon na firgita sai na kara
gyara tsayuwa ma na tsaya kyam nace
“daddy! ka dubi grmn Allah da manzonsa
karkayiwa faruk haka, ka 2na sanda ya
taimakemu ya rufa maka asiri kai kanka dani
daduk danginmu, me yasa yanzu mu kuma ba
zamu saka masa ba??
Idan wai don ni kakeyi don ka samar min da
farin ciki ka rabani da wahala, to ka barni
kawai sbd ni farin cikina anan gdn yake, faruk
mijina ne har gobe kuma zan iya zama dashi a
kowanne yanayi.“
Daddy ya zaromin ido yace “gsky na yarda
baki da hankali, banda haukanki ina ke ina
zama da nakasashshe makaho??
Abin kunyane ma ace kmr ni y‘ata mijinta
makaho ne, abnd yayi mana a baya ya wuce
mu gaba muke hange idan ke baki da 2nani
mu muna dashi kuma bazamu bari wahala ta
kasheki a banza ba, ki wuce nace!!“
Fuskata ta canja ma2ka naja da baya nace
“Ina me baka hakurin cewa wlh ba inda zanje
ba yadda za‘ai na tafi nabar gdn mijina wanda
yaso ni sanda kowa ya gujeni yake kyamatata,
kuma ba akan wani dalili ba.“
Cikin tsananin AL‘AJABI daddy ya bini da kallo
yace “Ni kike gayawa haka??“
Ba tare da tsoro ba nace “Kayi hakuri amma
ya zama dole in fadi hakan sbd kokoluwar
butulci ne abnd kake so kuma banyi halacci ba
idan nayi haka, na zabi na zauna anan har
mu2wa tazo ta riskeni.“
Kin zabi wannan makahon akan mu iyayenki??
Daddy ya fada yana me nuno ni.
Na gyada kai nace “Eh! haka nake nufi sbd
mijina ne ko a wajen Allah hakkinsa a yanzu
yafi naku.
Hakanan dady yajuya yatafi tare da gargadin
bani basu..
********************
faruk ne xaune abakin gado yana tatunanin
dani kaina bansan me yake tunawaba..
Gyaran murya yayi alamun yanason yace wani
abu naisaurin dago dakaina..yace
HUMAIRAH.!! Nace na'am yace kishirya gobe
zamuje gidanku."!
Yinme? natan bayeshi..zamuje muba dady
haquri akan abin daya faru..
Da SAFE WAJEN KARFE 10;00 ranar asabr.....
Tsawon min2na talatin muka dauka sannan
muka gama shirye-shiryen tafiya, abinda ya
bani mamaki yadda faruk keyi tamkar zamu
inda ba zamu dawo ba.
Bayan mun gama kuma yace na rufe duk wasu
kofofin gidan na ko‘ina, cikin rashin fahimta
nace “wai faruk ina zamu ne??
Ina tsammanin cewa kayi gdnmu zamu mu
dawo??
Meye kuma na sai mun garkame kofofi??
Faruk yadan hade fuska yace “ba gdnku zamu
ba siyar dake zanje inyi.“
Duk da yanayin da nake ciki sai da nayi dariya
na kada kai tare da cewa “Ba haka nake nufi
ba faruk abin ne kawai ke bani mamaki,“Na
dan taka daga gbnsa izuwa kan kujerar da
hijabina yake, na kara yin dariya a karona biyu
nace “wai ka siyar dani, ashema zaka iya siyar
da kanka kenan??“
Naja sandarsa muka wuce kai tsaye izuwa
waje tare da cgb da hira har muka fito izuwa
harabar gdn muka zarce izuwa inda motar
faruk take, na budewa faruk kofar ya shiga na
mayar na rufe tare da zagayawa na shiga na
tuka motar muka tafi.
Ckn nishadi muke tafiya ina sanar dashi duk
wani wuri da muka gifta ko wani abu daya faru
dai-dai sanda zamu gifta, a haka har muka iso
tsaleliyar katafariyar unguwar, SARAUNIYA
STREET!!
makeken Allon dake kafe yayi mana maraba.
2n daga nan fuskata ta fara canjawa shekara
daya curr kenan rabona da mahaifata na fara
tuno rayuwar data faru dani a baya, na fara
2no lokutan baya sanda a wannan hanyar ake
tukani a tsaleliyar mota, sanda nake takama
ina fankama, nake ji da kaina.
Ba yanzu da rayuwa ta canja ni ta karfin tsiya
ba. A hankali muka cgb da ratsa kyawawan
gine-ginen dake hamshakiyar unguwar da duk
wanda ka gani a cknta to ya wuce raini, har
muka iso tsalelen gdn namu.
hmm... birki naci kawai a gbn gidan ina
kallonsa, da ace wani zaizo wucewa yaga
motar danake cknta da yadda na koma idan
zanyi rantsuwa nan gdnmu ne bazai yarda ba.
A hankali na danna worn har sau uku a hankali
karamar kofar ta bude me bude gate din yabi
motarmu da wani wulakantaccen kallo naji
sanda kasa-kasa yake cewa “Bafa kowanne
talaka ke shiga gdn nan ba.“
Waye ne??
Ya tambaya.
Na sauke glass din motar a hnkl na leko da
kaina waje, 2n kafin nace komai yaja da baya
adan tsorace ‘ranki ya dade!!‘
Ya juya da sauri ya koma, jim kadan tafkeken
gate din ya fara budewa.
Naja motar izuwa harabar gdn nayi parking
tare da fitowa ina me bin harabar gdn da kll
sashe zuwa sashe.
Abubuwa da yawa suka fara dawo min, duk
inda na kalla sai wani abu ya fado min wanda
faru a dai-dai wajen.
Idona ya ciko da kwalla.
Dai-dai lkcn ne faruk ya fito daga ckn motar
wanda hakan ya dawo da hankalina gareshi na
tako naja sandarsa muka nufi ckn gdn.
Ma‘aikatan gdn kuwa sunyi dandazo sai
gaisheni suke duk wanda na gifta ta kusa
dashi, wasu ma harna fara manta sunansu.
Da sallamarmu muka shigo tafkeken
kayataccen falon, ba kowa sai hafsa y‘ar aiki
tsaye a gbn plasma dake kafe tana y‘an goge-
goge.
Ta amsa sllmr tare da juyowa muna hada ido
ta dafe kirji, LAH! aunty humaira!.
Hajiya! Hajiya!!
Ga humaira tazo.
Da sauri momi tare da daddy suka fito, momi
ta dubeta tace “meye??“
hafsa tayi nuni damu.
Dukkansu sukai turus suna kllnmu, momi ta
dubi hafsa tace “To na gansu jeki.“
Hafsa ta ajiye duster dake hannunta ta juya
tare dan dago min hannu tana murmushi, na
gyada mata kai kawai ta fice.
Daddy wanda ya kllmu ya dauke kai yaci gaba
da gyara maballin rigarsa lkc guda ya dago kai
ckn tsawa yace “uban me kuka zo yimin a
gd??
Meya kawo ku??“
Na dan kara matsawa gaf da faruk nace “ka
fada masa abnd kace kazo ka sanar masa
kawai mu tafi.“
Faruk ya gyara tsayuwa yace “Zuwa nayi don
na sanar dakai abnd nasan dole sai kayi
dariya, abnd nasan shi kake so kaji kuma shi
kake so ya faru.
Insha-Allahu daga yau ka daina tsanata kuma
komai yazo karshe.“
Faruk yaja hannuna izuwa kan kujera muka
zauna.
Momi da daddy ma suka zauna kunnuwanmu
duk a bude so muke kawai muji me faruk zai
fada.
faruk yace “Alhaji na sani duk duniya ba
wanda kake so kamar y‘arka guda daya wato
humaira, sannan kuma ba wanda ka tsana kmr
ni faruk sbd dalilai da yawa, musamman yanzu
da dalili me karfi ya karu akan nada.
Banga laifinka ba don kana son kwatowa
y‘arka yanci donta rayu ckn rayuwa me dadi
da nayi 2nani ma sai naga hakika kafini gsky.
Nayi iya nazarin da zanyi na gano cewa
zamana da humaira babu komai a ciki face
takaici da damuwa....“
Na katseshi da karfi nace “FARUK!!“
ya daga min hannu da fadin ‘ HUMAIRA! minti
daya.‘
ya dora da cewa “akwai cutarwa kwarai kmr
yadda kake fada idan naci gaba da zama da
humaira a haka kuma nima bazan so ta rayu
har ta mu2 da bakin ciki ba don haka gata na
dawo maka da ita har gida kmr yadda ka
nema kuma zan tafi na.....“
Nayi saurin mikewa tsaye nayi dawurwura a
guri daya naja da baya da sauri na fizgo wata
sharbebiyar wuka na dan yanki hannuna kadan
jini yayi tsartuwa kai tsaye na wuce da ita
wuyana.
daddy da momi suka mike da sauri tare da
zaro ido, momi tadanyi kara da fadin “iohhh!!!!!
humai...“
Faruk ya mike tare da cewa “humaira me kika
dauka??“
Ba tare da tsoro ba nace “WUKA!! wuka ce
faruk! kuma zan kashe kaina idan har ka tafi
ka barni.“
Ya tako izuwa inda yake jin motsina ya tsaya
cak a gabana yace “Karkiyi haka!! duk
tsananin tashin hankali da ukuba kada kiyi
yunkurin kashe kanki domin tashin hankalin da
zaki tarar yafi wannan, zaifi ki nemi wata
mafitar amma ba wannan ba.
Ya miko hannunsa tare da cewa “bani wukar.“
Nabi fuskarsa da kallo wadda keda tasirin
saurin sani ko hanani da kallo na saki wuka
kasa na rike hannunsa nace “Karkayimin
haka??
Nice fa humaira koka manta ne??
Kace ba zaka tafi ba don Allah kaji??
Kace da wasa kake faruk!!
Ya banbare hannuna daga nasa yaja da baya
yace “bakin alkalami ya bushe ba yadda muka
iya, don kin rabu dani ba yana nufin shikenan
ba.
Kece dai humairar nan ta baya zaki samu
wanda yafini kiyi rayuwar farin ciki.
Ki manta da ba2na kawai ki dauka baki sanni
ba a rywrki ki shimfida sbwr ryw, nina tafi.“
Ya kai karshen maganar ya juya ya nufi
hanyar fita...
Natausayama faruq..!
Koya rayuwanshi xata kasance..? Ko
yararuwan ita humaira zekasance...?
Sekucigaba da binmu
Dan samun sauran labarin. sekashiga blue
rubutunnan kayi like(y)
L‘AJABI part 20
with----->Aßu Fer'ezerh
Daddy yace “Yayi kyau faruk kuma ka birgeni
akwai kudin da nayi maka alkawari zan baka ka
tsaya ka karbi cheque din.“ Faruk ya juyo hawaye
suka kwararo ta kasan glass din dake sanye a
idonsa yace “ka rike kudinka bana bukata.“
Ya sake binmu da kallo wanda ya kara rikitani ya
juya ya fice.
Innalillahi wa inna ilaihir-raji‘un.
Abin da AL‘AJABI sai kace almara!! Faruk da
kansa ke furta rabuwa dani?? Da kafarsa zai fita
daga inda nake??
Idona yakai ga fuskar daddy wanda keta
murmushi yana annashuwa.
Da sauri na nufi hanyar fita inda faruk yabi nabi
bynsa duk da kiran dasu momi keyi min baisa na
dakata ba.
A guje na karaso inda yake tuni har ya fito
harabar gdn duk da cewa da ma‘aikata masu
yawa suna ta kaiwa da komowa bai hanani tarar
gbnsa ba, na rike sandar dake hannunsa zafafan
hawaye suka kwararo da idanuna ckn
sheshshekar kuka nace “Faruk kana nema rana
ka cnz min daga hakikanin yadda nasanka izuwa
wani daban, ko a mafarki ban zaci haka daga
gareka ba. Yanzu ma a haka tayaya zaka tafi??
Faruk ya grgz kai yace “indai don ta tfy ne karki
damu na tbbtr salih yazo??
Yayi nuni da inda motar da muka zo take. Na
juya na kll inda ya nuna, kwarai yazo kuwa. zcyt
ta fada min.
Ya dora da fadin “Na gaya masa dama ya biyo
bynmu zai daukeni ban bari kin sani bane sbd
kada ki gane akwai wani abu.“
Na kara gyara tsayuwa nace “amma faruk
yakamata ka tausaya rywta a karona biyu ka
sani idan ka tafi ba lallai na dauki dogon lkc ba
zan bakin ciki da takaici zasu kasheni, idan ma
wani wuri kake so kaje na yarda zan bika muje ko
ina ne kuma duk rintsi da wahalarsa zan iya
jurewa....“
Ba inda zaki bini humaira kuma baki isa ki fita
daga ckn gdnnan tare dani ba, na hakura dake na
hakura da tarayyarmu 2nda ba wahayi akayi
mana dole sai mun zauna tare ba.
Ya fada yana me daga murya.
Bakina yadau rawa na dan taka kadan izuwa
gfnsa nace “faruk!! nice fa!! ni kake gayawa
haka??
Anya kuwa kasan abnd kake fada??“
Ya gyada kai tare da cewa “kwarai!! da hnklna
kuma duk abnd nake fada shine abnd nake nufi
har ckn zcyt.“
Tfyr hawayena ta canja izuwa kara sauri nace “A
takaice kana so kace duk irin kaunar da kake
yimin a baya yanzu babu ita??
Duk yadda alkawuran da mukai zaka karya su??
kenan soyayyar da muka dade muna raina ta
mu2, yanzu babu ita 2nda har zaka iya tafiya ka
barni...“
Yayi saurin juyowa yace “EH! babu ita na dade da
kankareshi daga zuciyata wanda shine ya bani
krfn rabuwa dake.
Dai-dai lkcnne daddy da momi suka karaso.
Na dubeshi nace “idan ka tafi kai da kanka sai
kayi dana-sani me girma...“
dana-sani??
Ya tambaya yana dubana ya dora da cewa “Ai na
gama dana-sani 2nda na yarda na aureki,
wannan shine kuskuren da nayi mafi girma a
rywt.“
Kaina ya sara da karfi Bansan sanda nace “karya
kake faruk!! Ni nasan baka isa ka tafi ka barni
har abada ba ko ka daina so na ba.“
Ya juyo yace “Kece makaryaciya humaira amma
ni duk abnd na fada gskyne, zan tafi na barki
kuma bazan taba dawowa ba har abada.“
Ya yunkura zai tafi nayi saurin rike rigarsa ya
juyo muka dubi juna nace “Ka daina zaton ni kmr
kowa ce a gareka, nasan maganar da zaka fada
ta gaske da wadda bata gaske ba.
Nasan abinda zai yiwu a wurinka da wanda
bamai yiwuwa bane, abnd kake fada yanzu har
abada bazai yiwu ba.
Nasan kana fadan hakane sbd kawai kana son na
kyaleka ka tafi, idan kuma har da gaske kake ka
juyo ka rantse min da Allah Ka daina sona kuma
zaka iya tfy ka manta dani har abada!!“
Ya tsaya kawai ya kasa motsawa.
Na katse shirun ckn daga murya da cewa “Ka
fada mana idan zaka iya“.
jimawa kadan ya juyo a hnkl tare da grgz kai
yace “humaira kinsanni ma2ka fiye da kowa a
duniya, kinsan abnd zan iya yi da wanda bzn iya
ba.
Nayi karya idan nace “Zan iya cire sonki daga
zcyt kona manta dake a tsawon rayuwata.“
Yayi kasa da murya yace “Amma ina so ki
fahimta yau ba zabi bane a garemu, dole ne mu
rabu.
Bashi da wani alfanu cgb da zama a yadda muke
sbd kowa baya son zamanmu tare kuma ba wnd
keda shirin taimaka