Showing 9001 words to 12000 words out of 37941 words

Chapter 4 - BABBAN YARO book 3 Book End Complete by Binta Umar Abbale .pdf

24 Jul 2025

3126

fuskar ta... Hankalinsa kan wayar shi yace." Wanka me kikayi da rana haka."
Shiru nayi masa kawai ni so nake ya bar mun dakin naga ma futa zaiyi daga gidan dama duk a
takure nake zaman shi a gidan kwana biyu kacal. Yace."ko mafarki kikayi."?


Sarai na fahimci inda maganar sa ta dosa share sa nayi na zauna kujerar mirror a takure aje
wayar yayi ya karaso gurin, k'amshin turarasa ya dabaibayeni rumfa yayi min hade da tsare ni
da idonsa yace." Ina tambayar ki. "? Shiru nayi masa ina jin fad'uwar gaba.... Sunkuyowa yayi
ya talfamo fuskata cikin tafin hannuwan sa ya kura min ido, ni kuma sai kauda kaina nake cike
da fargaba. Bakinsa yake kusantowa dashi fuskata na rintse idona da k'arfi na mike, shima
Mik'ewar yayi da sauri ya rike hannuna yana ya mutse fuska yace." Meye haka? Kike wani
furgita da abunda kin San shi." Nace"Wai ba futa zakayi bane don Allah kayi tafiyar ka idan
zakaje ni Wallahi na kan rasa inda ka sanya gaba ka k'yaleni mana. "

Miskilin murmushi yayi yace." Futa zanyi amma na fasa kuma kece kika hanani futa." Da
gefan ido na kalleshi ina kokarin kwace hannuna a hannunsa, fuskarsa ya kara kusantowa da
tawa nace "Wai meye hakane."? Cikin shakakkiyar murya yace." Sha zanyi.!!!!!! Yanda ya fad'i
maganar zaka tabbatar bashi da kunya.. Nace" me zaka sha."? Bakina yana nuna da idonshi!
Ban San sanda naja tsaki ba ina kokarin fuzge hannuna cike da takaicin sa kamar ba d'azu
yaga yimin rashin mutumci ba.


Bude idonsa yayi sosai ya zuba su a kaina! Nayi kasa da nawa ganin yanda NASA suka yi ja
gasu sunyi kananu dasu yace." Nu kike wa tsaki kan nace zan sha bakin ki."!! Shiru nayi kaina a
kasa zuciyar na wani irin bugawa.!


Gyad'a kansa yayi yace." Kinyi dai-dai Zan sha karshen ki yanzu kin jawowa kanki."!!! Kafin in
Ankara ya dauke ni cas bed din ya cilla ni na mike da sauri ina nuna masa baby dake bacci da
hannuna... Ko a jikinsa yayo kaina zai danne Allah ya bani sa'a na mike da sauri na dira kasa
kofar futa na nufa kafin in bude ya kama ni ya matse jikin kofar rigar jikina ya sabule daga tsaye
yayi min rik'on tsauri!! Shanyayyun idonsa ya zuba min tsoro ya shige ni domin nasan kaina
bana so ya gano a matse nake dashi yasa na dinga kauce wa shi kuma yana kara kusan to ni
har ya samu nasarar kama bakina ya fara tsotsa kamar Wanda ya samu sweet

Jikina nane yayi bala'in mutuwa jin yanda yake tsotsar harshe na hade da leb'una na ban San
sanda na bude masa bakin gaba daya ba na cigaba da hadiyar yawun shi da ba tare da nasan
a wace duniyar nake ciki ba. Gaba ki daya ya gigita min lissafin domin tuni ya cire min brziya
inda yake wasa da hannunsa a guda a k'irjina yana fidda wani irin nishi!!!! K'afafuna suka tsami
sun gagara daukata sai na fara kokarin fad'uwa k'asa tare muka zube dashi, nayi plate kasa shi
Kokarin cire rigar jikinsa yake da ta fara ya mutse wa dake shadda ce ya jefar gurin k'afafun sa
ya raba a kaina ya rankafo sosai Brest dina guda ya kama da bakinsa yana tsotsa d'ayan
hannun kuma yana Mirza d'ayan.... Wani irin hali na shiga mai mutukar wahala rintse idona nayi
tam! Domin bana so na bude na kalleshi saboda kunya na lura bashi da kunya ko guda ganin
yanda ya wani k'aramin shu'uman idonsa yana kallona ga beast dina a bakinsa yana Mirza
guda na kasa hanashi..... Hannuna guda ya rike a nashi yana sakin wani irin nishi kafin in an
kara naji tsinin a barshi a jikina da k'arfin ta tsorata nayi sosai na bude idona sai na ganshi daga
shi sai gajeran wando duk ya cire kayan jikinsa, kamar in kurma Ihu naji ganin baya cikin
hayyacin sa yasa na tattaro k'arfin da yayi min saura na kwace kaina, fad'uwa yayi gefe na mike
da sauri.... Hannunsa ya sanya ya jawo kafata na fado kanshi.... Idonsa ya rufe tsam!! Yak'i
kallona matse ni yayi a jikinsa yana sakin ajiyar zuciya... Mintuna goma muna haka sannan ya
sake ni Mik'ewa yayi yana hararata ya shige toilet cikin wata irin tafiya. Ni kuwa da sauri na
kauda kaina ganin yanda wani Abu ya mike cikin wando sa duk na tsorata. Yana shiga toilet din
nayi saurin Mik'ewa kayana na sanya da sauri na futa daga d'akin.

*6/12/2019*
[12/7, 7:46 PM] .: *BABBAN YARO*
*76*






Ido muka had'a da granny dake zaune a parlor tana gyara carbin ta, kallo ta bini dashi cikin
zargi.. Take naji kunya ta kamani saboda nasan dole ta fahimci wani Abu aikuwa tace"Lafiya
kika futo a gigice."! Karasa nayi kusa da ita jikina babu kwari Sam naki yadda na kalleta
nace"Lafiya Granny ." kallona dai takeyi tana gyara carbi ni kuma kunya duk ta ishe ni, tace" Ina
Abban baby." Yana ciki." Abunsmda nace kenan nayi shiru.


Minti biyar tsakani na dai-dai ta hankalina tace"Nasan abunda ya koro ki a guje daga daki."
Kasa kallonta nayi ina mamakin tsohuwa da sa'ido, ta cigaba da cewa"Har 'yar Uwar ki ta kare
rayuwar ta ban tab'a gani ta guji mijinta ba ke meye dalilin ki."? Nace"Granny ban fahimci
abunda kike nufi ba."!

Hararata tayi tace"Ni ba yarinyar bace Asma'u kin futo daga d'aki kina haki! Da zare ido kice
min babu komai. Me kike nufi."? Kallonta nayi ganin yanda ta fututtuke fuska ! Bude baki nayi
zanyi magana ta d'aga min hannu babu wasa a fuskarta tace"Tashi ki koma gurin shi.""! Baki na
rawa nace"Ina...in ai futa zaiyi."

Tace"Idan baki tashi kinje ba Allah yana fushi dake wallahi mala'iku na tsine miki Ko mu da
muke mutan da ba muyi gudun miji ba sai Ku 'yan zamani ni d'in nan da kika ganni kullum sai
na bawa mijina hakkinsa har sai ture ina so kiyi koyi dani ko mijin ki bai neme ni ki ki mik'a masa
kanki."

Dariya tsohuwar ta bani ni kam ina ganin duk irin tsananin sha'awar dake damuna bazan iya
Neman shi ba, tace"Ki tashi ki koma dakin wannan guje-gujen da kikayi ya nuna min har yanzu
wani abun bai afku ba. Ke dashi, Saboda haka maza so nake ki samu cikin 'yan tagwaye."
Sosai naji kunyar ta jin abunda take fad'a narasa me yasa tsoffafi basa jin kunyar fad'ar

magana.

Kafin nayi wani yunk'uri ya fito daga d'akina fuskar shi a had'e! Kai tsaye bedroom dinshi ya
nufa granny tace"K'ato zo nan." Tsayawa yayi daga bakin kofar yana kallonta, tace"Kazo nace"
babu fara'a ya karaso gurin tace"Meye ya faru naga ta futo tana nishi
"! Tambayar granny ta bashi mamaki k'warai murmushi yayi cikin zuciyar sa, kana ya kalli
agogon hannunsa yace." Neman ta nayi a shimfid'a taki."! Kai tsaye ya fad'i maganar kunya da
takaici kamar su kashe ni.... Granny tace"koda naji dama nasan hakane to koma ciki gatanan."
Dariya yasa yace." Ni na fasa dama futa zanyi sai na dawo." Kokarin tafiya yake granny
tace"Kayiwa Allah ka koma ciki yanzu zanturo ta." Yana dariya yace." Nafasa fa domin wannan
maganin da kika bani ya daina mun aiki." Granny tace"Zan nemo maka wani insha Allah ai duk
laifin ita Asma'u ne da ta hanaka.""" Tab'e baki yayi yace." Rabu da ita granny ina ganin zan bi
sha'awar Inna Suwaiba ne." Granny ta kalleni tace"Kinji ko."? Tsabar bakin ciki da takaici yasa
na mike na bar musu gurin da ita dashi duk na lura basu da kunya hummm.

Amjad kaya ya sanja domin dai shaddar dake jikinsa duk ta ya mutse ya futo cikin suit granny
na zaune a gurin tana sakawa da kwance wa yayi mata sallama daf da zai futa tace"K'ato don
Allah kar ki bi matan banza ka rike sha'awar ka har ka dawo gida ga iyalinka insha Allahu zan yi
mata fad'a." Sosai tsohuwar ta bashi tausayi Sam bata son ta ganshi cikin damuwa yace." Kar
ki damu granny insha Allah zan kiyaye sai na dawo." Tace"Ubangji Allah ya tsare min kai duk
inda kake ya kare ka daga sharrin mahassada da magauta."

Rambo ne ya bude masa mota ya shiga ya zauna ya zauna kusa dashi doh-doh yaja motar
suka futa daga gidan.....Gabakid'aya ma'aikatan shi sun hallara a gaban shi mutum guda ake
jiran zuwan shi wato Bashir Manager har yanzu bai zo ba zargin da ake masa ya tabbata kenan
Amjad duk wani bunkice ya gama shi kan abunda ya faru a company sa wattanin baya da suka
wuce,al'amarin ya faru ne da saka hannun Manager wato Bashir da hadin bakin k'ananun
ma'aukats Wanda sune suka ji tsananin azabah da horo suka fad'a.... Amjadu yayi mamaki
wannan al'amari Babu abunda baiyi wa Bashir ba na rayuwa Da abunda zai saka masa kenan
take police din dake tsaye a bayan shi da 'yan jarida suka nufi gidan Bashir din cikin motar su,
sunyi alk'awarin duk inda yake zasu nemo shi dole yazo ya fad'i wad'anda suka sanya shi aikata
wannan mummunan aiki.

Ko da suka isa gidan Manager sun taddashi cikin tsananin damuwa da tashin hankali ga ciwo
yana fama dashi a kwance yake magashiyan ga iyali ga rashin abinyi babu abunci hakkin Allah
da Amjad ya kwantar dashi da ciwon zuciya... Babu imani police din nan suka tasa k'eyar sa
gaba 'yan jarida na ta faman daukar shi a hoto, tun a mota yake kukan takaici da nadama da
yasani bai aikata ba gashi kud'in da ya karba gurin aikata abun 'yan fashi sun shigo sun kwashe
domin shi yana ganin kamar da hadin bakin Mai citta gurin zuwan 'yan fashin gidan sa yayi biyu
babu uku ba ko daya bashi ga tsuntsu bare tarko hausawa suka ce idan kace tukunyar wani
bazata tafasa ba tom kaima taka baza tayi ba..... Kafin kace komai har jama'ar gari sun fara
taruwa a kofar rujajan company da ya Riga ya mutu babu mamora du suna dauke da
abubuwan duka suna jiran Manager su sambade shi... Labari ya watsu a gari dalili wasu

kafafen yad'a labarai da suka fara maganar... Haka a ka shigo da manager a rirrike 'yan sanda
na kare shi saboda dukan da jama'a suke kai masa da gorori duk da haka sai da suka fasa
masa kai jini ya dinga d'iga a goshin sa duk yayi wiki-wiki suka isa dashi gurin mai gayya mai
aiki wato Amjadu Mainasara.

Mai girma governor tsaye a parlor shi hankalin shi a mungun tashe jin abunda yake faruwa a
gari, shifa ya dauka yaron ya hak'ura Ashe kwance-kwance yayi musu sai da suka saki jikinsu
mutukar sunan shi ya futo cikin wannan badakalar to babu shakka yasan ya gama amfani a
garin kano yasan jama'ar gari sai sun kusa kashe shi da iyalinsa gashi daf ake da zab'e bayan
nan kuma yasan daga sama gurin shugaban kasa sai ya fuskanci hukunci mai tsanani watak'ila
ma sai ya daure shi.... Kaiwa yake yana kawowa cikin tunanin Neman mafuta.


Matar shi ta futo cikin kwalliya ta tardar shi cikin wannan halin nan take tambayar sa duk ya
warware mata komai murmushi tayi tace"ka kwantar da hankalin ka mijina Kaine dai akan mulki
kana da damar da zaka iya sawa ka hana kuma insha Allahu mulki sai ya dawo hannunmu
mune zamu maimainta zama kan kujera daram!! Ka sanya su Lauje da fafake Kumurci tare da
police suje su tashi taron idan ta kama ma su saki harbi da tiyagas tom zakaga kowa na kokarin
guduwa domin ceton ransa. Nan su Lauje sai su dauko manager din su zo dashi mu kuma mun
San inda zamu yi dashi ka San dai karshen zancan."


Take governor ya yarda da sha'awarar matar shi ya tashi tsoffafin ya ranshi da police na gidan
gomnati suka nufi gurin domin tashin taron da tarwatsa jama'a


Wani irin mari Amjadu yake kifawa Bashir yana tambayar shi dalilin da ya sanya ya aikata
wannan mummunan aiki Bashir sai da ya suma sau uku domin Amjadu zagewa yayi ya dinga
labta masa wata murtykekiyar bulala yana fad'i "Bashir baka da amfani a duniya nan tunda
dakai za'a had'a baki ayi wa Allah da manzon sa izgilanci kai cire ta tawa ni me sauki ne tunda
bawa ne makaskanci irin ka, da iyakar ni kuka tsaya abun bazai dame ni ba, dani da Ku kunje fa
mu cikin masifa da tashin hankali da fushin Ubangji ko ka fad'a min wad'anda suka sanya ko
baka fad'a ba min ba ni na sam su kuma karshen su yazo da izinin Allah."!!


Manager ya fad'i a gurin yana wani irin nishi! Mai wahala kafin kace kwabo ya kara suma take
Amjad din ya kwara masa ruwa sanyi karara ya mike a zabure!Wanda yayi dai-dai da sakin
harbi a gurin ji kake tas!tas! tas! Kafin kace kwabo gurin ya hargitse!! Hayakin tiyagas ya d'ume
gurin sai atishawa ake ana Neman d'auki!! Wannan ya basu damar shiga ciki Amjad na ganin su
sun shigo a guje ya sanya su Rambo su dauke manager su b'oye ko ina ne domin yasan shi
suke nema..... Bindiga suka saito dai-dai kanshi zasu harbeshi yayi saurin sunkuyawa!! Take
suka wuce da gudu!!! Rambo dake sab'e da manager a kafad'a ya fara kokarin haura Katanga!!

Lauje ya hango shi da sauri ya fuzge bundigar hannun wani d'an sanda ya saita k'afar Rambo
ya bashi harbi take Rambo ya fad'o kasa shi da Maneger dake a sume!! Ihu Doh-doh ya kurma!!
Yayo kan Rambo yana duba k'afar shi dake zubar da jini!! Ganin Lauje da wani d'an sanda sun
yanko da gudu gurin ya sanya Doh-doh daukar Manager a kafad'a cikin jarumta ya fara kokarin
haure Katanga... Lauje! Ya duba hannunshi, Ashe lokacin da yayi harbin jefar da bundugar yayi
a gurin!! Da gudu ya juya da baya domin d'aukota! Amjadu ya soka masa hancin ta a k'irjinsa
fuskar sa a mutukar murtuke!!! Lauje ya d'aga hannunsa sama! Cikin saranda! Amjad ya hade
hannunwan sa biyu cikin jarumta ya murde su ya rike tamau! Suka fara tafiya har suka karasa
inda Rambo yake kwance cikin jini yana nishi lokacin kuma Doh-doh ya samu nasarar dirga da
Meneger k'asa ya nemi mab'oya Ashe bai tsira ba 'yan jarida da sauran police d'in gidan
gomnati sunga shi take suka rufa masa baya..... Wani d'an jarida shi ya fara isa gurin ya ji
lokacin da menegar yake cewa"Duk wannan abun da ya faru daga gomnati ne me girma
governor shine da wasu 'yan kasuwa suka tilas tani tare da bani makudan kudi miyan goma sha
biyar kan in b'ata sana'ar Amjadu domin ya durkushe a cewar su bashi da amfani kuma Asali
shi din ba Dan Asalin najeria bane babu yanda za'ayi yazo ya dinga cin moriyar kasa saboda
haka Dole a rusa company yaje kasarsu su ya gina musu shine ni kuma nazo muka hada baki
da wasu daga cikin ma'aikatan company muka futar da kaya masu dauke da sunayen Allah da
manzon sa." Manager yana kuka yake maganar ya rike Doh-doh sosai yace." Ka nemar min ga
fara gurin ubangidan ka nasan mutuwa zanyi ko na rayu nasan governor bazai barni inji dad'i
ba. Aikuwa wannan d'an jaridar ya gama nad'e maganganun manager a na'urarshi.. Manger ya
fara wani irin tari kafin me ya amsa kiran ubangiji bayan yayi Kalmar shahada Allah kenan
manager ya mutu da kalmar sha hada a bakin sa.


Ganin Police din gidan gomnati sun kusa iso wa gurin yasa wannan d'an jaridar Neman
mab'oya wani siririn guri ya shiga ya b'oye yana gyara na'urar shi inda ya saita camera shi
dai-dai gurin yana daukar duk abunda yake faruwa a gurin.... Menegr suke kokarin kwace wa
daga hannun Doh shi kuma ya rike gawar tamau yak'i sakinta domin yana hango zuwan Amjadu
gurin Wanda yake rike da Lauje!! Sai da suka iso gurin sannan doh-doh ya sakar musu
meneger Amjad ya buga masa tsawa akan me!! Yace." Sir Allah yayi masa rasuwa yanzu.""

"Hahahahaha"!!! Yaran gidan gomnati suka kwashe da dariya take suka saki gawar maneger ta
fad'i a gurin.... Kumurci ya nuna Amjadu cikin tsageran ci yace." Abunda kake son ji daga
bakinsa baza kaji ba!! Ko bai mutu ba mu zamu kashe shi!!! Mu kaishi lahira! Hahahahaha!! Kai
da kake D'an karoro d'an gudun hijira kazo garin mutane kana mana mulkin mallaka wallahi
idan kayi wasa sai mu maida ka garinku na gado tsirara.!!! Amjadu yaji zuciyar sa na wata irin
tafasa ga takaicin manager ya mutu bai fad'i komai ba ga takaicin maganganun da kumurci
yake yab'a masa, cikin zafin zuciya ya saki Lauje! Da ya galabaita ya fad'i gurin kan Kumurci
yayi cikin jarumta ya Kai masa naushi!!! Kafin kace kwabo fad'a ya hautsine tsakanin Amjad da
Kumurci, fad'a da gabb'ai! Ba da makami ko bundiga ba............

*Tofaaa*
Ran maza ya b'aci








*7/12/2019*
[12/7, 8:59 PM] .: *BABBAN YARO*

*77*





Sosai ake bata kashi tsakanin Amjad da Kumurci sai tada k'asa suke yi a gurin, Kumurci dake
mak'ale da wata matsiyaciyar wuk'a mai mugun kaifi a jikinsa ya fuzgo ta da sauri ya d'aba ta
kirjin Amjadu!!! Cikin zafin nama ya k'wace kansa daga rik'on da Amjad din yayi masa suka bar
gurin a guje!! Doh-doh yayi kan ubanginsa da da gudu ya d'ago shi cikin tsanani. Tashin hankali
jini tuni ya b'ata masu jiki, cikin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login