Showing 27001 words to 30000 words out of 33160 words
Chapter 10 - MIJIN TACE 4 COMPLETE HAUSA NOVEL BY SODANGI.txt
natsuwa ya ce ina jin kunyarki ba zan iya
ba, shi yasa nake so kiyi in adalci ki bani ita. Na
wuce shi naje nayi kwanciyata gabana sai faduwă
yake yi, kar dai Adó ya shigo min dakin nan ya ce zai
fitar da yarinyar nan don ban san abinda zai faru ba.
131
Sai aka yi sa'a har gari ya waye bai shigo ba, sai
dai kuma in bata jin zirga-zirgar, shi nayi zaton ko
lemon tsami yake nema da jar kanwa bai samu ba.
Washegari da safe na kammala abin da zan yi na
sallah da jan carbina na mike zan fita don shiryawa
yara abin karyawa da tafiyarsu makaranta.
Sai na kalli Bilkisu na ce mata ke je ki đakinki
kin ji, yanzu ba zai zo miki ba balle ya taba ki tunda
gari ya waye ta ce min to.
Tuni su Nusaiba suna kicin suna kokarin
kammala komai, don sallamar kannensu kafin suma
su sallami kansu, saboda sun riga sun saba ko ban
fito ba ba za su yi komai don haka ina shiga akan
kammala suka gama suka tafi.
Suna fita suka bar gidannan sai kawai na hango
wucewar Ado zuwa dakin yarinyar nan kan kace
meye wamnan sai kawai na jiwo ihunta akidime.
Jikina ya rinka rawa nayi matukar kidia na gigice
na rinka jin tanfar wani abu yana yi min yawo a jiki,
ya rasa hanyar fita, waiyo! Wayyo!! Wayyo!!! Abin
da kawai nake fadi kenanz uwa can nayi sa'a wani
tunani yazo min na bar waiyo na koma 'lahaulah'.
Ban san tsawon lokacin da na dauka ina cikin
wannan kidimar ba, sai kawai na ji ni jike sharkafda
gumi, na mike naje nayi wanka na yiwo alwala nayi
nafila raka'a hudu nayi addu'o'i na shafa na zauna
gaban madubi ina shafa mai ina kallon kaina a
132
madubin.
Ko da bani da nonuwa a tsaitsaye i din kuma ba
zai yiwu ace Ado zai yi wuju-wuju dani ba, a cikin
ganiyar kuruciyata nake na kuma riga na zaina mace
mai daraja wato dai mata irin na zsmani da kana
ganinsu ba sai an tsaya yi maka bayani ba.
Don baka na tsayarwa raina da cewar da wuni in
wani ya ce bai sonka to lokacin ne wani kuma zai ce
shi da kwana yake kaunarka, don haka ba zan
lamunci irin wannan matsanancin bakin cikin ba
daga gare shi, don zai iya nukurkusani ya karya min
zuciyata.
Kwalliya sosai na tsaya nayi ba don komai ba, ba
kuma don kowa ba sai don in tabbatar wa kaina
cewar kuruciyar da nake kirawa kan nawa tana nan.
Daga ido nayi na kalli agogo da nufin in ga
lokaci don fitar da nake son yi in bar gidan ya gama
abin da yake a dakin ya fito bai same ni ba, sai kawai
naji gabana ya fadi
Sha daya da rabi ne lokacin dora abincin ranar
gidan yayi, gashi mai girkin bata zo ba, na ce tay1
hutun kwana biyu don ta huta wahalar hidimar da aka
yi kenan, in har ban tsaya ni nayi girkin ba yara za su
dawo gida basu samu abin da suka ci ba.
Kan haka na fito na shiga kicin na soma aikina
abincin gidana bakina da zuciyata basu daina
ambaton lahaula' ba.
133
Duk da ban shiga kicin din don kowa ba sai don
yaran da nake gudun kar su dawo gida basu samu
abincin da zasu ci ba, ban kuma iya yin girkin yaran
kawai na fita na bar sauran mutanen gida ba.
Don ban saba ba, ba kuma zan iya barin iyalin
gidana da yunwa ba, don haka sai kawai na shiga
aikin girkin sosai, gefe daya ina yin dafaduka mai
hade-haden kayan lambu gami da naman rago a ciki.
Daya gefen tuwon shinkafa ne miyar agushi,
wanda nima shi nake sa ran zan ci don in rage
matsananciyar ramar da nayi a kwanakin maganar
aurennan zan ci abincin girki na kwana biyu.
Na sake yin farfesun kayan ciki da na yi wa hadi
sosai na kuma yi na kaji saboda Balkisu, a dalilin
nanata min da zuciyata take yi cewar ita yarinyar bata
yi min komai ba, bata da wani laifi a wurina, ba ita ta
kawo kanta ba, ba ita taga mijina ta ce tana so ba.
Sannan kwata-kwatanta bata wuce Umahmah ba,
ashe kuwa ko don Umahmah ta samu wadanda zasu
yi mata adalci a rayuwa zan yi wa Bilkisu.
Na hangi fitowar Ado daga dakin ban san sanda
bakina ya ce mishi dan iska ba, sai da na tuna mijina
ne nayi maza nayi tayin istigfari.
Yara suka shigo da gudu suna murnar ganina a
kicin din su, na shiga zuba musu ina mika musu da
kananan na fara kafin na is kan nmanyan.
Ado ya shigo ya same ni ina magana da su
134
Umahmah dukansu saboda na lura in ba yi nayi da
gaske ba shiga za su yi cikin lamarin da ba nasu ba
ne, suyi kane-kane.
Babu wani zumudin bukin da suka yi sai ma da
Sa'adatu tayi musu kaca-kaca ne suka je suka yi
kwalliya.
v Nusaiba ai kun san Babanku yayi aure ko? Hindu
ta ce eh Goggo, amma ai mun girmeta ma, na rage
fara'ata na ce uwarku ce, ko kun girme ta zaku
girmamata don matar Babanku ce, balle ma ba ku
girme ta ba, za dai kuyi sa'anni ne kawai.
a Ina maganar ina zuzzuba musu farfesun a
kwanuka daban-daban ina ajiyewa, ga kuma abincin
shima duk na zuba musu shi na sake bude oven na
dauko wata katuwar kaza da na yi wa gashi na
musamman na hada na sake jawo flask na cika da
ruwan tea mai citta na ce ku diba kuje ku same ta
bakuwa ce ku sata taci abinci ta kuma sha tea suka ce
to, suka diba suka tafi.
Ado ya matso kusa dani, nawa abincin fa? Ban
iya yi mishi magana ba, na dauki na Mama na tafi
wurinta sai da nayi sallama sau biyu bata amsa ba,
nasa kai na shiga tunda nasan tana ji na.
Sannu Mama, ta ce yauwa sannu kadai, ta bude
ido sosai tana kallon irin kwalliyar da nayi, na zauna
ina bata abinci, Ado ya biyo ni yana tambayata ina
abincin shi? Kan in yi magana Mama ta ce mishi har
135
ka fito daga dakin amaryar ne?
Shima bai amsa ba balle ni, to kaima kenan ana
jin haushinka ba a baka abinci ba to balle kuma ita
wannan aure ai fata dai kawai Ubangiji yasa ba asarar
dukiya aka yi ba, tunda ban ga alamar yayi wani
tasiri ba.
Na fito daga dakin Mama na dawo nawa nayi
maza na dauki gyalena zan fita, sai ga Ado ya shigo
ina za ki Humaira? Maimakon in tsaya gaya mishi
inda zanin sai kawai na soma yi mishi kuka.
Kuka kuwa mai tsananin gaske, saboda bakin
cikia shi ya ishe ni, kiyi hakuri, hakuri yake ta bani
sai da ya ga na dan natsu sai ya ce min ban fa yi miki
wani aibu ba Humairah, ban kursa zalunce ki ba, ba
kuma zan zalunce ki ha.
Saboda ban yi aure don na gundura da ke ko kin
ishe ni ba, nayi ne don ina son karawa yin hakan
kuma ba laifi ba ne, gode ni'imar da aka yi min nayi
Na roi alfuoarki ki ba ni mu zauna lafiya kar kiyi
min abin da k: ka san úa car ba kya yi min.
Kar ki fita ba da izinina va, zan hakura da komai
amma ban da wannan, in ki ka dan yi hakuri da ni
kadan nayi miki alkawarin zan yi mai yawa da ke.
In ki ka dan kawar min da kai ki ka yi min
kawaici na miki alkawarin zan ji kunyarki, in kuma
yi ta girmamaki, saboda ke din dama kina da girma a
wurina. Yanzu muje ki bani abinci yunwa nake ji,
136
nace ai ya kare, ya sake kallona cikin natsuwa kafin
ya ce min Humairah kenan.
Kina ganin idan ki ka azabtar dani da yunwa da
akwai wata riba da hakan zai kawo miki? Ai yanda ki
ka shirya abin da ya dace ki ka tura wa Balkisu tare
da yara sa'o'inta don su debe mata kewar zaman
gidan su saboda kin yarda bata yi miki laifin komai
ba, ba ita ta kawo kanta bani naje na kawo ta.
Haka ya kamata ki yarda nima da na kawo ta ba
laifi nayi ba, Humairah. Sannan ko da nake ni na
ajiye ku dukanku kin fi kowa sanin ina gudun bacin
ranki, ina tsoron ganin fushin ki.
Ina yin komai ko barin komai don neman zaman
lafiya dake, to na roke ki kar kiyi amfani da damar da
ki ke da ita a kaina don ki kuntata min ki hana ni
morar halal din da aka halalta min.
Kalaman nashi suka dan sani natsuwa, naje na
dauko daya kazar da na bari a cikin oven din na kai
mishi falonshi tare da ruwan matsattsen lemo, to
zauna mana na ce mishi IRa zuwa na dawo wurina ina
shiga wayata na dauka saboda rurin da take yi.
Gabana ya fadi kar dai wani laifin aka je aka
cewa Inna nayi take nemana? Jikina a sanyaye na
Soma amsa wayar tata, sai naji ta ce min, taro ya tashi
lafiya? Na ce lafiya Inna.
Ta ce, to Ubangiji yayi miki albarka, ke da
zuriyarki, ya saka miki da alheri, ya kuma baki
137
hakuri da juriyar rike girmanki, na ce to amin Inna.
Muka dan fara hira da ita har na dan saki jiki na
gaya mata wulakanci da cin mutuncin da Ado yayi
min, na shiga dakin matarshi da rana tsaka, sai da
tayi ajiyar zuciya kafin ta ce min.
Kar ki rinka kokarin shiga tsakaninshi da ita,
babu ruwanki kamar da ido kawai kan al'amarin nasu
kamar yanzu ne kawai sai ki ka zafin shi yana ta
raguwa a zuciyarki.
Yafi Yafi ace za ki rinka damywa da su ku rinkka
samun matsala ke dashi har ita yarinyar tayi wayon
da zata gane kina da damuwa a kanta, sai ta raina ki.
Kin ga abu ya baci kenan, aa ce haka ne Inna.
Muka dan yi shiru kadan sia naji ta nişa ta ce ai
kishiya zafi ne da ita, sai kayi hakuri in ba haka ba
sia ki ga ka gudu ka bar ladanka.
Na ce ai aima dazu ji nayi kamar in gudun, tayi
aza ta ce kar ki fara ai gidanki ne kiyi mata adalci,
kawai Ubangiji zai hore miki zama da ita na ce to.
Dama Inna ta bani sosai na in saki jiki in yi magana
da ita.
Magana kuma ba irin ta uwa da 'ya ba kawai, a'a
har da zancen kawa da kawa aminan juna tana yi min
magana in muka soma gaisuwa zata sako min
maganar kishi'.
Watakila don tasan shi ne babbar matsalata ta
lokacin ni kuma da yake na riga na kidime bana iya
138
boye mata zafin da nake ji, in yi tá gaya mata abinda
nake ji da yanda zuciyata take tafarfasa in fadi
maganganu masu zafi a kanshi.
Rannan ma dai da'yake na riga na tunzura da
yawa saboda abin da nake ganin yanayi da tayi min
wayar ce mata nayi, kai ni kam Inna to me zan sake
yi da Kawu ne kuma? Me zai sake yi min in ga ya
burge ni kuma a rayuwar nan Inna?
Ai ni kwata-kwata gaba daya ya riga ya fita
kaina babu abinda na tsana irin in ga wulgawarsu ko
in ji maganarshi balle in gan shi ya shigo in da nake,
sai in ji kamar in mike kawai in rufe shi da duka in yi
ta duka.
Dariyar da tayi ne yasa na katse zancen nawa,
nayi shiru, me yayi miki da zafi ne haka Baban
Umahman? Na dan yi murmushi saboda jin sunan da
ta kira shin na ce bare-barenshi ne yayi yawa Inna.
Ba ki ga irin rawar jikin da yake yi akan yarinar
nan ba, shi yasa ma na ce ni kam ko ya sake dawowa
wurina ba zan sake sauraronshi ba, tunda dai abin
nashi haka ne na hakura dashi na bar mata shi na
yafe, suje can su karata kawai
To in ki ka yi hakd ai ba kiyi mana adalci ba,
nayi maza na ce kamar ya ya Inna har da ke a ciki?
Tayi murmushi ta ce, dani kai tsundum a ciki, ke din
ai tanfar uwa ki ke a gare ni a yau, zaman lafiyarki da
kwanciyar hankalinki a gidan aurenki yana nufin
139
al'amura masu yawa a gare ni, don nasan shi ne
kwanciyar hankalin 'ya'yanki.
Ni nasan babu wani bare-baren da rawar jikin da
zai yi akanta da har zai tsole miki ido, in ba kin bar
abin da yake gabanki kin maida hankalinki a gare su
ba. Me zai mata ya kai wanda ya yi miki?
Ai babu shi, maganganu masu dadi tayi ta yi min
har dai na ahkura na yarda da cewar wai duk abin da
yake yin bai kai wanda ya yi min ba, amma ni kam in
ban da Innan ce ta gaya min haka da ban yarda ba.
Don gani nake tanfar babu ma in da aka taba yin
irin abin da shi yake yi din. A haka sai gashi ya dawo
dakin nawa, kashedin da 'Inna tayi min na cewar
matukar ba-shi ne ya kawar da kai daga gare ni ba, to
kar in bijire mishi dashi nake shirin yin aiki.
Don haka nake ta fatan shi din da kanshi ya fita
hanyata tunda ni kam a yanzu nafi so ya bar ni kawai.
Zo nan kiji Maman Umahmah cikin zuciyata na
ce wani,wayon zai yi min don kuma ya kan kira ni
Maman Umahmah ne a irin lokutan da yake-ganin
tanfar al'amura suna shirin cabe mishi a tsakaninmu.
Ai babu wata amaryar da zata yi irin amarcin da
ki ka yi a hannuna, Humairah ke ce fa, ya. soma
lissafo min alarmura masu dadi da suka gudana
tsakanina da shi a lokacin amarcin da muka yi
sannan ya kalle ni ya ce to a yanzu wanne nake iyawa
a ciki?
140
Sannan ke ce Humairah da na kamu da sonki sai
na iya tsayawa na nunawa kowa har da wadanda bai
kamata in yi musu wannan tsaurin idon ba, cewar ke
din ke kadai nake so, ke kadai nake bukata.
Zan kuma iya barin kowa saboda ke a yanzu wa
zai sani in yi irin hakan? Ado ya soma lissafo min
al'amura da tun ina jin shi ne kawai har ya soma sani
murmushi har ya sani na hakura na fidda komai çikin
raina nasa hannu biyu na karbi al'amarin aurena.
Shi da kanshi Ado ya fahinta tare da sanin cewar
Inna tayi tasiri mai yawa a cikin harkar
zamantakewar rayuwar aurena dashi da kuma
amaryar da yayi, don haka kullum a cikin girmamata
yake, kullum kara ganin mutuncinta yake yi.
A kullum kuma in ya bude baki zai fadi wani abu
game da ita, to alherinta da karemcinta gami da
adalcinta ga suruki shi ne abinda yake bayar daa
labarinta akai.
Rannan na wuni cikin farin ciki da zumudi
saboda Ado ya gaya min zai tafi Abuja gobe, a dalilin
hutun da ya dauko ya kare, dadi ya kama ni a
Zuciyata na ce zan dan huta da ganin mu'amallarshi
da 'yar yarinyar nan da ko kunyar tubewa a gabanta
ba yayi, duk da karancin shekarunt.
Tsananin farin cikin nawa ne yasa na yi wa Inna
waya nake bata labarin da zai yi, sai ta ce min ba da
ita zai tafi ba kenan? Nayi maza na ce, a'a shi kadai
141
zai tafi, ta ce to me zata yi miki a gidan ba shi ita
kawai ya tafi da ita, ai kawaici yayi miki kin ga kumnà
ki sata ta bishi da kanki yafi ace shi ne ki ka kure
hakurinshi ya ce zai tafi da itan.
Ko ba zai iya yin hakan ba ne? na ce zai iya
wanda yafi wannan a ta ce to kin gani.
Duk da bana son tafiyar tasu tare na daure nayi
abinda Innan ta ce in yi.
Dadi yayi matukar kaa shi sai dai ya daure ya
hadiye ya biyo ni dakina yana muzurai, to tunda kin
ce dole sai an tafi da wannan yarínyar ai sai kije ki ga
shirin nata wannan wani shiri zata iya? Na ce mishi
to.
Duk da ni na ce ayi tafiyar tare da ita bayan
tafiyarsu kuka nayi tayi, to ina ga in da shi ne kawai
ya zartar da hakan? Bayan tafiyar tasu ne Innan tayi
min waya don jin lafiyata, na ce mata sun tafi Inna
amma nayi kuka.
Tayi murmushi ta ce share hawayenki ki
wastsake babu wani abinda zai je ya yi har ya kusa da
kusan-kusan abinda yayi miki, ko yake yi miki a
yanzu. Na ce Inna kenan, ta ce eh ai gaskiya ce kawai
mai ita kuma yana iya yiwa kanshi hukunci.
Sai mutum bai cin zamaninshi ya hana wani cin
nashi zamanin, ai kin ci naki Maman Umahmah kina
a kai tunda me akai da maza? Don haka itarna barta
taci irn nata saboda naki zamanin vavi tsawo ya
142
kuma yi karko mai kyau.
Amma menene? Me zai je yayi sabo? Wane dare
ne jemage bai gani ba? Ai sai na ranar mutuwarsa ke
ce fa aka bashi ke yana da shekaru talatin kina da
shatara, kin san muhimmancin shekaru talatin wurin
da namiji kuwa shekaru ne na kamala da cikar
halittarsa.
Shekaru ne na ganiyar karfi, shekaru ne na
abubuwa masu yawa da ba zai yiwu in yi ta lissafo
miki su ba, sannan a wancan lokacin bai da wani
nauyi kece ke kadai, bai da wani uzuri sai naki, bai
da wata bukata sai taki, bai da wani abinda yake so
sai ke gaba daya lokacinshi naki ne, gabba daya
hidimarsa taki ce.
Ba yanzu da ya riga ya gama mallakar
hankalinshi nauyin Jama'a da kuma abubuwa masu
yawa suka hau kanshi ban da haka kina ma da wasu
darajojin a wurinshi ke kadai ce zai yi surukata da
uwarki irin surukutar da yake yi dani ba zai sake
yiwa uwar wata hakan ba.
Saboda ya riga ya girma sannan ban da
wadannan duka sai kuma ki ka yi sa'a ki ka zama
kece ki ka zamo mishi uwar Umahmah, ki ka sake
zuwa ki ka haifan mishi Baba Yahya.
Ko wadannan biyun kawai ki ka tsaya akai ai kin
san kin haifi abin da yake so, to balle gasu Zainab, ga
Khadija ga Fatima, don haka kar ki yarda ki mance
143
ni' imomin da aka yi miki kije kina sa ido kan abin da
bai taka kara ya karya ba.
Kullum ki tasa al'amarin ya'yanki a gaba kar ki
zalunci dan kowa balle sakaiya ta taba miki yayanki,
nayi aza na ce to Inna.
Kullum kalaman Inna suna kwantar min da
hankali su sanyaya min zuciyata su kara min son
ya'yana da ganin darajar su, ba.wai son 'ya'ya irin
na rashin kwaba ba, a'a son 'ya'ya irin na hakura da
abinda ka ke so ko yin abin da baka so saboda su
saboda rayuwarsu ta gaba ta inganta.
Kalaman nna ne suka kara sanya ni na yarda na
gane na kara hakuri na kara kyautatawa mijinam, ita
kuwa matarshi na maida ita tanfar yar uwa bani da
wata ita balle in je ina sha'awar zaluntarta,
musamman kuma da yake nafi kowa sanin mijin
nawa Dr. Ado Sulaiman zai yi min kawaici ya ji
kunyata ne ya kuma yi ta girmamani kan abin da
yaga ina yi na adalci, amma ba zai taba yarda da
zalunci ba.
Rannan da daddare muna hira da Inna a waya
saboda hirar tamu ta zama ka'ida yanzu kullum sai
mun yi, na ce mata ai dazu na fita Inna.
Tayi maza ta tambaye ni, ina ki ka je? Na ce
robar nan naje na cire, Inna tayi dariya ta ce kishi dai
ya motsa kenan, na ce ba kishi ba ne Inna, na dai gaji
ne kawai, ta ce ai shi din ne dai.
144
Na numfasa