Showing 18001 words to 21000 words out of 33160 words
Chapter 7 - MIJIN TACE 4 COMPLETE HAUSA NOVEL BY SODANGI.txt
Adon waya ya dawo. amma abin
mamaki wai da ya tambaye ta abinda ya faru da yake
bakinta bai mutu ba, sai ta ce mishi ni ce nayi mata
sanadin hakan.
Watakila tayi zaton daga fadin hakan zai ce min
zo ki tafi gidanku, bana auren yanda ta saba ganinn
ana yi wa 'ya'yanta, sai kuma maganar ta kare ayi
min fada ya kuma shirya ya turata ita tare da Suwaiba
wacce bar yanzu aure ya gagare ta, to sun je sun
dawo gamu nan kuma muna zaune tare a gidan.
Wadannan dalilai da nake issafawa sai suka sa
auren nawa ya zamo auren da a daidai lokacin da
mutancn waje suke yi min hangacn jin dadi da farin
cikin da ke cikinshi saboda nasarorinshi na zahiri da
suke baiyane.
Ni kuma da nake ni ce a cikinshi cikin zuciyata
nasan yanzu ne nake zaman hakuri mai yawa, sai dai
kuma ban taba yarda fitintinun da ke kewaye dani a
cikin nashi sur sani na taba cewa da na sani ba, a
kullum na gayawa mai babban allo matsalolina ko a
waya ne.
Hakuri zai yi ta bani yana gaya min cewar shi
dan Adam haka rayuwarsu take, yakan girma ne yana
tare da matsalolinshi, don haka in yi ta hakuri. Dadin
89
abin dai kawai a wurina shi ne duk kokarin Mama ta
kasa shiga tsakanin Kawu Ado da Innata ta 6ata.
Tayi-tayi abin ya gagara, tayi juyin duniya ta rasa
yanda zata yi, bata ma kara tsinkewa da al'amarin ba
ta kara tsorata dashi sai a lokacin da Adon ya
zartarwa Sa'a hukuncin aurar da ita ga babban
amininshi Barrister Tukur Usman.
Wanda yasan Sa adatu tana da saurayin da take
So bai ma tsaya wajen yin shawara da kowa ba, izini
kawai yaje ya nema a wurin Baba.
Sai kaWai ya fadi daurin auren kowa yaji, Mama
tayi bakin ciki kanar zata mutu ta tasa shi a gaba
tana kuka ga Suwaiba shekara da shekaru babu aure,
ka samo mutumn mai muhimmanci irin wannan ka
dauki wata Sa'a ka bashi don dai kai sun shanye ka
ba ka ganin kowa ba ka son kowa sai su?
Ya ce ba samo shi nayi ba Manma Aminina ne yya
kuma yi min kukan matsalolin gidanshi ne ya roke ni
in ina da wata "yar da na san me tarbiya ce in yi
mishi hanayrta yana so.
Kin ga kuma yana cikin damuwa ba zan kara
mishi damuwarshi ba, ban yi mishi adalci ba in nayi
mishi hakan.
Yanzu ita Sa'a ba damuwa bace sai Suwaiba?
Yarinyar da bata son auren ban ganta tana yin kuka a
gabanka ba, yayi murmushi ya ce ai iyakar dai abinda
zata yin kenan Mama.
90
Ba za a kai ta gidanshi ta ki bin umarninshi ba,
be za te je tayi mishi rashin kunya ko wulakanci ba,
ba za taje ya ce mata yi ta ki yi ko bari ta ki bari ba,
sabods du a dakinsu uwarsu tana da tasiri mai karfi
akan 'ya'yanta.
Tana kuma da halin girma nayi wa surnıki adalci,
ni kadai nasan irin taimakon da tayi min akan aurena,
su Suwaiba kuwa ba haka suke ba Mama, ina jin ta
rannan tana gaya miki ko taje gida bata gaida
Babansu ko kallonshi bata yi, saboda bata da
lokacinshi.
Shiru kawai nayi muku, to yaushe zan dauke ta
in baiwa wani? In dai ba so nake in taje tana
w&stsakewa daga halin rashin mijin da take ciki ba ta
Soma cin mutuncinmu ni dashi.
Shi yasa na barta ta kawo shi ita da kanta, kayan
dakin dai zan bayar.
Hidima ta ban mamaki Ado ya yi wa Sa'adatu, a
lokacin auren nata irin hidimar da ko auren su
Umahmah ya tashi yi in yayi haka ya ci a yaba mishi.
Magana guda daya da ya gayawa Sa'adatu a
ranar da za'a kaita gidan mijin nata kuma ita ce dai ta
gamsar da ita tayi amfani da ita aka samu zaman
lafiya da kwanciyar hankalin da ake nema bai taba
kawo karanta wurin Adon ba balle maganar ta wuce
ta kai ga Innarmnu.
Maganar kuwa ita ce hukunci na zartar miki Sa'a
91
irin wanda uba ne kadai ke da ikon yiwa 'yarshi
hakan in har anyi mata tarbiyar da ta dace da ita duk
kuwa da ni din ba mahaifinki ba ne, na kuma san
hakan sai dai nasan ke din yarinya ce da aka yi wa
tarbiyar sanin darajar na gaba.
Na kua san ina da gira da mutunci a wunnki sai
nake ganin kamar ba zan yi iko dakc kiyi sanadin da
zan tozarta wurin mutuin da nake da kima a wurinshi
ba, don haka in kin ji ku zauna lafiya.
Shekaru biyu kenan da yin auren Sa'a ta haifi
danta Adam, har sun yi aikin Haji ita da Inna tare ya
biya musu suka tafi babu wanda ya taba jin wata
magana surukuta mai dadi suke yi shi da Ado.
Ire-ircn irin wadannan al'amuran sune suke kara
sanya ni hakuri da kokarin danne zuciyata a kan
al amura masu yawa ina kawar da ido akansu.
Amma duk da haka wani abin kure hakuri ake yi,
saboda a hali irin nawa halin da kullum Inna ke yi
min kirarin rashin hakuri a kan shi sai in rinka ganin
bai dace in yi hakuri da dole in kuma yi da abinda bai
zame tnin dole ba.
Dawowan Mama gidan Ado yayi dalilin da itama
Suwaiba ta dawo gidan da zama don ta ce ba za ta iya
ZAInan gidan ubanmu ba, in kuma da mutumin da ke
taimakon Mama kina a zahiri to Suwaiba ce.
Kan ya' yana a hade yake, don ko da sun yi
wayon sanin 1yayensu tun kan mu taso to a zaman da
92
ake yi dai kansu a hade yake, don ba a bambanta su
da komai ba, komai tare ake musu, suma duk abin da
zasu yi tare suke yi ba su da wata matsala ko wata
damuwa.
Amma zuwan Suwaiba sai ta tasa min su a gaba
da iya shege iri-iri, dan kankanin abu ne na yara zasu
yi sai ta ce uhun, wai su masu gida ko?
Saboda ita gidan ubanta ne yasa take yi muku
haka, ta bugi Umahmah ko Mama ta buge ta bai taba
damuna ba, don nasan duk tsiyarsu ba za su gana
mata %50 din abin da suka gana min ba.
Don haka ko a jikina saboda na riga nayi ilimin
sanin cewar zaluntar yaro bai cutar dashi da komai
sai dai ma ya zamo mishi wani alheri a rayuwarshi ta
gaba.
To amma neman da take yi na ta rinka 'shiga
tsakanin Umahmah da dan uwanta tana batawa shi ne
abin da naji ba zan lamunta ba, tunda abin da ke
afruwa a tsakaninsu din hali ne kawai na kuruciya.
Suna mata tana musu kamar yanda take yi
tsakaninta da kanmenta, da ni ce na haife su, gara
wadancan ma duk sun fi karfinta in dam be za'ayi
dukanta zasu yi.
A duk lokacin da maganarsu tazo gabana kuma
na kan yi hukunci ne bisa cewar ta basu hakuri don
ita ce karama duk da mafi girman da aka yi mata na
kwana bakwai ne.
93
Ba kuma don komai nake yi hakan ba sai don in
hada kansu su zama abu daya, su sani su kuma yarda
da cewar yancin da ita take dashi a gidan bai wuce
wanda suke da shi ba.
Don haka rannan da na sake jin Suwaiba tana
shiga naganar Su tana cewa ai tunda kuka zo zaman
maula a gidan ubanta sai kuyi jayin bakuri da ita sai
na gangara daga inda nake.
Naje na shiga wurin nasu Suwaiba tana ciki na
tambayi yaran abin da ya faru suka mayar min na
kalli, Suwaiba na ce mata a wannan bayanin ne ki ke,
fadin wannan maganar wa wadaanan yan yaran
ya'yan cikinki?
Sau nawa ki ka haifi wadannan? To bana so kar
in sake ganin ki a wurinsu bana son ganin kina shiga
min harkar yara, ta ce har da taki ma na daina, na ce
to da yafi miki daidai.
Tun daga ranar ta daina gaishe ni, in na gaishe
tan ma ta amsa a laiace ba fita tana kallona bata yi
min sallama ba ta dawo kuma a lokacin data ga
dama.
Naga zata zubarwa mijina da mutuncin da ake
ganinshi da shi tunda ba wani shiga na mutunci take
yi ba shi kuma ba zaunin gida bane balle yasa abinda
take yi.
Don haka nayi mata magana kan ta daina yawan
fita, ina take zuwa tunda ni da ita ai ba wasu dangi
94
muke da su a Dabai ba, balle ta ce min wurin 'yan
uwanmnu take Zuwa.
Sai kawai tavi min maganganun da na kalle su a
matsayin rashin kunya, gudun 6acinrai sai yasa Ado
yazo gida daga Abuja, sai na ce mishi ga abinda ake
ciki don ya sani.
Sai kawai ya ce min kai Humaira, kananan
maganganu irin wadannam rinka hutar dani kawai ki
daina gaya min su ko dai kiyi maganin abin kawai da
kanki ko kuma hanya mafi sauki shi ne ki gayawa
Mama.
Nasan zata tsawatar na ce mishi to duk da ba
dadin hakan naji ba.
Rannan sai wani abu ya sake hada ni da Suwaiba,
naje na samu Mama ina gaya mata, sai kawai ga
Suwaiba tana biye da ni tana magana har tana tafa
hannu, ni fa sai dai in za ki mutu ki mutu in za ki yi
rai kiyi rai.
Don duk tsiyarki ba zan bar gidan ba ba wurinki
na zo ba, ba kuma don ke nake zaune ba, kin ce in
daina kula 'yarki na hada na ce har kema bana
kulaki, bana shiga harkarki, ba na shiga harkar
'ya'yanki dukkansu wurin Mama nazo gida kuma
gidan Kawuna ne.
Na kalli Mama, wacce tayi shirù tana kallon
tsiwar da Suwaiba take yi min, na ce Mama kina jin
ta? Sai kawai naji taja nin tsaki ta ce min
95
Ke tafi can ni ki bani wuri da fitinarki ta tsiya,
ke yanzu ai na riga na gane ki gaba daya burinki bai
wuce kiyi min abin da hawän jinina zai tashi ba ya
karasa ni in mutu, in yaso burin uwarki ya cika a
kaina.
Na kalli Mama nayi murmushi na ce lnnata ai
bata da sauran buri akan ki Mama, tunda gidan da ki
ke yi mata gadara a kanshi kina fadin naki ne ya
zama nata, mijin da ki ka kwace mata gashi can kin
baro mata shi saboda ya gagare ki.
Nan kurna da aka dawo aka zauna nawa ne, tunda
mai kishiyoyi da 'ya'yan miji ma takan nishadi in ta
samu wuri ta ce gida da mnijin nata ne ita kadai balle
ni da ni kadai din ce.
Mama ta kama kuka, Suwaiba kuma ta kama
maganganu ba dai ita kadai ce a gidan ba wooo! Na
ce ai ita bata dame ta ba, ba kin san gidan ba? Ai kin
san bata kishi da ita.
Ai Inna bata da sauran kishiya, dama Mama ce
matsalarta, tun kuma daga ranar da tayi kuskuren kin
jin kashedin da masoyanta suka rinka yi mata, ta
dauki Ado ta danka min shi a hannuna da nufin
zaluntar uwata, nayi wuf na kama shi na dunkule shi
wuri daya na dankawa Innata shi bata sake zamowa
matsalarta ba.
Na wuce su nayi tafiyata cikin zuciyata ina fadin
Mama dai kam yau na zage ta duk abinda Ado zai yi
96
kuma sai yayi kawai mu gani.
Ban dade da fitowa daga dakin nasu ba sai ga
Suwaiban tazo ta wuce ni ta fita nayi waya na ce wa
maigadi ya kulle gidan kar wanda ya sake shigowa
kowane ne sai an gaya min, ya ce min to.
Sai da aka yi sallar magariba Suwaiba ta dawo
maigadi ya ki bude mata kofa tayi juyin duniya ya
ki, Mama ta turo keken ta na guragu don bata riga
tayi karfi ba tukuna, tazo ta same shi ka bude mata na
ce.
Cikin stawa take ba shi umarnin, ya ce Goggo ce
ta ce kar a bude, tayi-tayi abin ya gagara sai ga ta a
kofar dakina na ce kisa a bude wa Suwaiba gida ko?
Cikin tsawa tayi maganar na ce to, ba ta kuma
zaci to din zance ba na kali Hindu na ce mata jeki ki
ce wa solori ya bude mata kofar, tana gaya mishi ya
bude, Suwaiban ta shigo.
Muna nan a haka Suwaiba bata sake fita ba don
tasan taná fita zan sa a kulie har Ado ya dawo,
shigowar dare yayi na kuma riga na shiryawa zuwan
nashi, don sabuwar kaza ce a jikina.
Kwanaki uku kuma kenan tunda naci ka riga ta
jika a kidime kwarai ranar ya kwana, Humaira, na ce
mishi naam ya kara matsowa jikina va kankae kina
da wani sirri a tare da ke Humairah da wani lokaci ki
ke kidiar da ni, ki rinka sanya ni ina jin tanfar dai ke
din budurwa ce.
97
Shiru nayi ban tanka mishi ba.
Washegari da safe sai da na slirya mishi abin
karyawanshi ya gama komai ya yi wanka ya kintsa
aiken Mama biyu ta waya wai tana son ganinshi,
amma bai samu fita daga dakin nawa ba sai gab da
azahar.
Don haka sai da yaje yayi Sallah ya dawo sannan
ya shiga wurin nata, ya dan dade kafin yayi waya wai
in je.
A dakin na same su ranshi a 6ace kwarai da
alamar ya ji maganganu iri-iri, amma duk da haka ya
kalle ni saboda kwalliyar da nayin yasan táshi ce.
Meke faruwa ne Hurmaira? Cikin natsuwa na ce
mishi kamar me? ya ce ina nufin mc ya hada ki da
Mama? Nayi maza na ce babu komai.
Mama tayi maza ia ce ba ki zagen ba za ki ce
mishi babu komai? Suwaiba ta ce wai ita ga
mu...Ado ya yi maza ya katse ta in ki ka zage ta a
gabana ranki zai 6aci, na kalle shi cikin natsuwa na
ce mishi.
Ni babu abin da ya hada ni da Mama tunda ba
abokiyar magana ta ba ce, uwata ce kai ne ka ce in
wani abu ya faru tsakanina da Suwaiba in daina gaya
maka, in kawo kara wurinta zata tsawatar mata.
Ya ce haka ne, na ce to karar na kawo sai
Suwaiba tayi min rashin kunya a gabanta nayi mishi
bayanin komai har kawo kan abin da ya faru duka,
98
sai dai na ki yarda da cewar ni maganganu da Mama
nake yi na ce da Suwaiba ne.
Ado yayi shiru na lokaci mai tsawo saboda
ranshi ya 6aci kwarai, don kwa ko ban amsa da
Mama nake yi ba ai shi ya ji abinda na fadan sai dai
kuma nasan zai san ita Mama ita ta fara tsokanata.
Shiru yayi cikin matsanancin tunani, yayin da ni
kuma nayi shiru cikin natsuwa ina sauraron abinda
zai ce, sai Mama ta fara yi mishi bayani, ita
Humairah bata gane ba ne ita so take duk wanda zai
zauna a gidan nan sai ya yarda ta maida shi talolo
kamar yanda ta maida wannan yaron.
Ado ya daga kai ya kalle ta ya ce wa Ibrahim?
Tayi maza ta ce ebh, shi to ita kuma Suwaiba ba za ta
yarda da hakan ba, don ita ba sakarya ba ce irin shi,
-ba ruwinta tazo ba ba don ita tazo ba.
Tunda gidan nan ba nata ba ne ita da yan
dakinsu da zata ce sai ita da su ne za su zauna a ciki,
gida ai naka ne amma take bugun kirgin nata ne yayi
maza ya katseta ba bugun kirjin bane nata ne kuma
tunda suwaiba tace ba wurinta tazo ba.
Kema kin fada ba wurinta tazo ba, to ta bar mata
gidanta kawai, azo a zauna a gida ace ba wurin matar
gida aka zo ba wurina aka zo'ni mazaunin gida ne?
Humairah ai bata adawa da 'yan uwanta, Mama
da ke take yi shi yasa da ta samu damar gaya mii
magana ta gayaa miki, ba kuma zan kyale ta kan
99
rashin kunyar da tayi miki ba.
Ai ta zauna da Ibrahi babu abinda bata yi mishi
ba, ta kuma zauna da Kaltume da ya'yanta tsawon
wata goma bata ji ko ganin wani abu mara dadi ba,
saboda bata da matsala dayan uwanta. Don hakka
Suwaiba suna da gidan uba ta koma can ta zauna.
Mama ta ce uhun, za ka kore mu dai kawai tunda
kasan hakanne zai fi yi mata daidai, ai kaima kasan
ba zan zauna a in da Suwaiba ba za ta zauna ba in dai
ka ce ta tafi to tare zamu tafi.
Ya ce to shi kenan Mama, in kun ga hakan yafi
miki sai ki bita ni dai nasan ban ce ke ba amma
Suwaiba kam a gabana ta amsa ta ce ba wurin
Humairah tazo ba, to in wurina ne ni bani da gida
zaman nata ya isa haka ta tafi kawai.
A ranar Suwaiba ta tafi, ina jin Mama tana gaya
mata inda zata, wai kar ta ce gidanmu ban san yanda
aka yi ba sai kuma gata ta gama bin dangi ta gaji ta
koma gidan namu.
Ta bude dakin Maman ta shiga ta zauna ita
kadai, Innar tawa kuma ita ce dai mai daukar
dawainiyartata.
Barin Suwaiba gida sai Ado ya dorawa diyarshi
dawainiyar baiwa Mama magani da safe da yamma
tunda da rana kam bata nan tana makaranta, sai ni in
je in bata.
Tunda Ado ya dorawa Umahmah wannan
100
dawainiyar ya hadata da aiki saboda kullum taje
baiwa Mama magani tunda ba maganin ba ne kawai
sai ta motsa mata jiki, to bata fitowa sai da kuka.
Tunda ba za ta gama ba sai ta jawo wata sanda da
ta sunne a gefen gadon nata ta rafke ta dashi wai tayi
mata mugunta.
Kullum tazo ta gaya min zante mata to kiyi
hakuri Umahmah ai kin san bani na saki wannan
aikin ba ko? Ta ce min eh.
Rannan ina dakin Ado da rana saboda yazo gida
week end na kalli agogo na ce mishi bari in je in
baiwa Mama magani lokaci ya yi, ya ce a'a babu inda
za ki yanzu Umahmah taje ta bata na ce ishi to.
Sai ga Umahmah ta dawo tana kuka da iyakacin
Rarfinta, sallama biyu tayi kafin Ado ya bani izinin
amsawa da bata umarnin shiga inda muke din.
Durkusawa tayi a kasa tana cewa, Baba ka
taimake ni ka ce ni da Hindu da Nusaiba ne zamu
rinka baiwa Mama magani da motsa jiki, kowa sau
daya a wuni tunda su ba ta dukansu. Amma ni
kullum sai ta buge ni.
Da sauri ya ce duka Umahmah? Ta ce ch, ka
gani? Yanzu ma ta buga min sanda a dan yatsana
yayi maza ya kama hannun nata yana dubawa ban
san abin da ya tuna ba sai kawai naga ya yi
murmUshi.
Ya ce, Mama kenan, ba kya iya tashi kiyi komai
101
ba kya iya yi wa kanki komai amma kin ajiye sanda
don dukan wadanda ki ke son duka?
Ya dago ya kalli Umahmah ya ce, Umahnmah,
tayi maza ta ce na'am Baba, ya ce daga yau na sauke
miki nauyin kulawa da Mama da maganinta da motsa
jikinta, duk ba naki ba ne.
Zai zamo na Mamanki bari ke in dora miki
nauyin kulawa da Maman naki kin san irin abincin da
na canza mata don gyara min jikinta? Tayi maza ta ce
eh Baba.
Ya ce to ki rinka shirya mata shi kina bata ita
zata kula min da Mama.
Umahmah tayi dariya cikin tsananin farin cikin
canjin da ta samun ta ce mishi sau goma zan rinka
bata ko sau ashirin Baba?
Ya ce, a'a Umahmah ai rage kiba da rage teba
nake so tayi ba karawa ba, don haka sau uku kadai za
ki bata, ta ce mishi to. Tana murna tana tsalle don
dadi, tasa kai ta fita. Tun daga nan bai wa Mama
magani da motsa mata jiki ya dawo kaina.
Gaskiya ne, tunda Ado ya tilasta ni janyewa daga
cin abinci mai nauyi irin namu na dafawa na janye
daga cin nama mai yawa, na koma cin irin
ganyayyakin da ake