Showing 21001 words to 24000 words out of 33160 words
Chapter 8 - MIJIN TACE 4 COMPLETE HAUSA NOVEL BY SODANGI.txt
nomawa a gonar Humaira
Farm'.
Nayi matuka zabge jikina, tebar da na ajiye tayi
matukar sauka na rasa nauyi mai yawa a tare dani
102
daga kilo sittin da biyar zuwa saba' in na dawo
arba in da bakwai zuwa hamsin.
Na kurma tsaya akan motsa jikina safe da yamma,
don in kara gyara jikin nawa ta yanda mai gidan zai
samu yanda yake so.
Masani da motsa jikin Mama na gama na dawo
nazo na samu Umahmah tana zaune tana jiran zuwan
nawa, wai abincina ta shiryo ta kawo min, kin san
Goggo nasa miki 'Asparagus' sanda daya Brocooti
daya ganyen celery danyen dankalin turawa guda
uku, cherry tomatu biyu, Beef tumatu biyu, cabbage
dan madaidaici, kwai dafaffe biyu
Na ce to na gode Umahmah bari in yi wanka
tukuna in fito ta ce min to, har nayi wankan nazo na
gama ci tana jirana in kawo miki madarar shanu na
dafa miki?
Na ce kawo min taje ta kawo min a kofi ina
karba na kafa kai na kwankwade, ta zuba min ido
tana kallona tayi murmushi ta ce, Goggo ke kam
kwankwadar madara ki ke yi nace eh, Umahamah kin
san mu komai addininmu ya koya mana yanda zamu
yi shi.
Don haka madara kwankwada muke yi, ruwa
musha a hankali, sai zuma kuma mu lasa, kin gane?
Tayi maza ta ce min eh.
A wannan lokacin ba Ado ba da dama kullum
jikina abin jin dadin shi ne kowane lokaci kuma cikin
103
tattalin jikin nawa yake don ya kara jiyar dashi dadin
da yake nema.
Ni da kaina ina jin dadin jikin nawa, ya yi min
warai-wasai, bana tare da wani nauyi, kullum
kuruciyata kara bayyana take, kwalliyar da na dama
nake yi saboda ina daukar kowane iri.
A daidai irin wannan yanayin ne da lokacin wani
irin lokacin da nake ganin tanfar ban taba samun
wata dama ta mallakar mijina kamar shi ba.
Ado ya dawo daga tafiya zuwa kasar Thailand in
da ya tafi taron kärawa juna ilimi kan noman Rania
kasashe masu tasowa, saboda a wannan lokacin ya
shiga kungiyoyin manoma daban-daban cikin kasa da
waje.
Kwalliyar mini siket da wata 'yar shirmanmiyar
riga nayi mishi, shi ne kuma ya taho min dasu in na
tsaya cewa nayi kyau ma nayi shirme.
Kallona Ado yake yi yana karawa, watakila ji
yake tanfar ya kama ni yayi ta lashewa tun lokacin
yin hakan bai yi ba.
Ban fa bai wa Mama maganinta ba, fuskarshi ta
dan yannutse alamar ba ta maganin ya somma shiga
mishi cikin harkokin rayuwarshi.
Bari dai zan nemi wacce zata rinka yi min
wannan aikin ina biyanta, don na riga na fara gundura
da yanda hakan yake shiga lokataina.
Nayi murmushi na ce, ai ba wani dadewa ma ake
104
yi ba, minti arba'in da biyar ne kawai. Ya kalli
agogon hannunshi kafin ya sake kallona, ai ba zan
iya jiranki minti arba'in da biyar ba, sai in ga kamar
awa arba'in da biyar din ki ka yiwo, muje in raka ki.
Na mike tsaye da nufin zuwa dauko alkyabbata
da gyalenta in sanya in rufe kwalliyar tawa, tunda
nasan ba zai yiwu in iya shiga wurin Mama a haka
ba.
Hannu ya saka ya jawo ni na fada jikinshi,
Humairah kina kallon yanda ki ka zama kuwa a
madubi? Ko ban kalla ba ai kana gaya min kuma in
dai nayi maka ka gamsu to ai shi kenan ya ishe ni.
Kin yi min na gamsu Humairah, kin zama tanfar wata
yar yarinya mai shekaru ashirin da biyar.
Nayi dariya na ce, goma fa ka rage min Kawu, ya
ce uh ba ki i ashirin da biyar din ba, babu mai
ganinki ya ce kin wuce hakan, don haka bar gonman
kawai a gefe in kin ga dama ma ki dora min a kaina
tunda ni kam ni ne...
Nasa hanu a bakinshi na ce na ce baka yi ba
kawu, ganinka nake tanfar yau ne nmuka faro komai in
don wannan tebar taka ne bata yi maka komai ba in
ban da mutunci da kwarjini da ta kara maka.
Ado ya kyalkyale da dariya ya ce, muje ki bata
magani mu dawo na sanya alkyabbata na rufe kaina
da gyalanta muka fita muka nufi dakin Mama, tana
ganinmu ta rushe da kuka.
105
Ni kam nasan ganin da tayi mana tare ne yasa ta
kukan gashi kuma na dan makara kan lokacin da na
saba zuwa bata maganin, amma Ado da bai gane
hakan ba rarrashi ya rinka yi yana bata hakuri tare da
tambayarta damuwarta.
Wani abu ke miki ciwo Mama? Tayi jagwale ta.
kara maida kanta ta kara zama abin tausayi, ta girgiza
kai uh'uh wasu hawayen suna kara zubowa, to
menene?
Kiyi magana mana Mama, ganin kidimewar tashi
a kanta ya kara bata dama ta sake rushewa da wani
sabon kukan.
Cikin kukan naji tana cewa, wai burinta ne kawai
ta gane ba zai cika ba a kanshi har ta mutu, da sauri
Ado ya zaro ido yana kallonta cikin kidima tare da
tambayarta menene burin nata?
To ba Ado ba, ko ni da ba wani damuwa nayi da
lamarinta ba, mu'amallah kawai nake yi da ita don ta
zame min dole, 6oyewa kawai nake yi nake kuma kin
yardan wa zuciyata dauke ta ita din damuwa ta ce
tunda nasan damuwarta a kaina tafi wacce nake da ita
a kanta yawa.
Kasake nayi ina kallon Mama tare da sauraron
abin da zai fito daga bakin nata a matsayin shi ne
burin nata, sai kawai naji ta kekkebe baki ta ce, wai
in ganka da mata biyu, kadan ya rage in yi subutan
hannu in buge bakin Mama da abin da nake rike da
106
shi na gwajin jininta.
Sai na daure kawai cikin zuciyata dai gaya mata
nayi ai ke da burinki za ki mutu Mama, Ado kuwa
shiru yayi na wani lokaci mai tsawo, cikin wani
yanayi da yafi kama da tausayinta ne yafi komai
kama shi.
Zuwa can sai naji ya bude baki ya ce mata kiyi
hakuri Mama in har na samu yanda zan yi to ba zan
bar ki har ki mutu da wannan burin ba, zan cika miki
shi nan ba da dadewa ba, in har muna raye dukkan
mu, kiyi hakuri.
Cikin yanayin shagwaba ta ce mishi, to. Hannu
yasa ya karbe abubuwan da na zo dasu din na
amfanin nata yayi mata komai saboda jikina ya riga
yayi min sanyi, na riga na gane wannan burin na
Mama na son ganina da kishiya.
In ba wata kaddarar ba zai cika a kaina, don
kuwa kalaman da yayi amfani da su wajen bata
hakurin sun sha bamban sosai da wadanda na saba
jin shi yana yi mata a duk lokacin da tayi mishi
magana kan ya kara auren.
Mafi yawancin lokaci murmushi yake yi ya ce
Mama kenan, ba wai bana son yin auren ba ne, ko
kuma na kasa yin shi lokacin yin nashin ne kawai bai
yi ba, don haka kiyi hakuri.
Ita kuma tayi ta zuga tana kokarin tunzura shi
kan wai ya kasa ne, sai ya ce to Mama in na kasa ma
107
ai ba wani abu ba ne dama karawan ba na kowa da
kowa ba ne na wanda yaga zai iya adalci ne, in ba za
ka iya ba sai ka zauna da guda dayarka kawai.
Ni da in yi biyun in zo ina zaluntar wata ko ana
zaluntarta ina kallo na rasa yanda zan yi ai gara min
in yi ta zamana a haka. Sai taja tsaki ta ce ai kuwa da
ka ji kunya.
To yau ba haka aka yi ba cewa yayi in har ya
samu yanda yake so nan ba da dadewa ba zai yi
sanadin cikan burin nata. kenan yayi nufin yi shi
kuma mutum ne mai yin aiki da abinda ya fada.
Tashi muje Humairah, kalmarshi da naji kenan
na dawo cikin natsuwata na fahimci ya gama yi mata
abinda ya kawo mu din. Sai dai duk da na gane
abinda yake shirin yin ban muna mishi wani canji ba.
Iyaka dai bayan ya samu bacci ya dauke shi,
maimakon nima in yi nawa baccin don in samu hutun
da ya dace da jikin nawa tsunduma nayi cikin tunani
mai yawa, in saka wannan in kwanče, in saka
wanca.
Mama zata yi min sanadin kishiya a daidai
lokacin da ni da mijina muka dunkule muka zama
abu guda daya, ya zama ni a zama shi. Zata sa shi
kawo min wata cikin gidana don ta samu hanyar
wargaza min gidan, tayi min sanadin fitina, tayi
dalilin da nima zan kasa zaman gidan mijina kamar
yanda itama nata gidan mijin ya gagare ta.
108
Tunda a yanzu din nan a yanda najin zuciyata, ai
ba zan iya zama da wata kishiya ba, bai yi min ita
tuntuni ba sai yanzu da na gama mike kafafuna, ya ce
in nade hanyoyi iri-iri kawai nayi ta tunanowa na
yanda zan yi in hana Ado yin auren saboda in ga
burin na Mama bai kai ga ci ba.
Sai dai tayi ta zama dashi yana cinta ita kadai a
ranta, tayi ta fama dashi tuni Ruwailah ta fado cikin
raina, kiranta zan yi in yi mata maganar tunda ni da
ita yanzu a dunkule muke, ta kuma san hanyoyin
shiga da fita iri-iri, bari dai ya kuskura ya ce min
yana neman aure, zai ga abin mamaki.
Mun soma zama da Ado a cikin wani yanayi da
shi bai san me nake ciki ba nasa ido da 'yan rahoton
da na kewaye shi da su akan dan kiris in suka ji to
suzo su gaya min sai kawai aka yi waya da daddare
kan cewar mai babban allo bai da lafiya.
Babana ne kuma yayi wayar, jikina ya dauki
rawa nan take na soma yin kuka duk da ina jin
Babana yana gaya mishi cewar a'a da sauki gashi nan
ma ita Binta tana ba shi kunu ina jin dai jikin girma
ne kawai ya yi addu'ar Ubangiji ya ba shi lafiya.
Ya juyo ya kalle ni. Mallam mai babban allo kar
yayi ciwo? In ban da mai babban allo an yi mishi kira
mai kyau gashi ya rayu cikin addini ga kuma gatan
ya'ya da jikoki a kewaye dashi an ce miki kananan
shekaru ne dashi?
109
Ya fa haura tamanin da dadewa, ban daina kukan
ba tunda a kam nasan komai tsufan mai babban alle
ina son shi ina kuma son rayuwarshi kullum fatana da
addu'ata Ubangiji ya kara mishi lafiya ne.
Miko annunshi yayi yana share min hawaye
tare da fadin sai ki himmatu muyi sammako da
sassafe muje mu dubo shi, in yaso ai daga can sai in
wuce tunda ina da tafiya a gabana.
Ke kuma in ki ka kwana sai ki dawo na ce mishi
to, amma ai gara muje da yara koda su Nusaiba ne
kawai tunda kana jin irin fadan da yayi min wancan
karon na kar in sake zuwa mishi gida ban kai mishi
yara ya gansu ba. Koda bai da lafiya in ya gansu zai
ji dadi, ya ce min to.
Kan ayi sallar Asuba mun gama komai, suma
yaran da za'ayi tafiyar dasu sun gama, Mama kuwa
naje na gaya mata na kuma ce mata ko zamu tafi tare
ta ce ina? Ba za ta ko ina ba da wannan jikin nata na
ce to.
Nayi mata addu'ar samun karin lafiya na bar wa
masu aikina guda biyu Sadiya da Tabawa sallahun
kula da Mama da sauran yaran da ke gidan, muka
Idar da sallar Asuba muka tashi.
Computer Hiace Bus mai cin mutum goma ne
muke tafiyar a ciki, dama kuma Adon ya sai min ita
ne saboda tafiya gida da yaran, ni da shi da Baba
Yahya ne a baya sai yan matan su hudu a tsakiya, sai
10
kuma Usman da dircba a gaba.
Ni kam dama tunda muka taso ban saki jiki nayi
wata magana ba in dai ba wata tambaya aka yi min
ba, lazimina kawai nake yi.
Ado yana ta amsa wayoyinshi daga wurare
daban-daban, kamar yanda dama al'adarshi take
saboda yanayin mu'amallar shi da Jama'a.
Ana cikin haka naga ya amsa wata waya da naji
ya ce ikon Allah! To muna nan akan ya na daga ido
na kalle shi banga wnai abu ba sai naji ya sake yin
wata wayar, kai Bala ka bar abin da ka ke yi kaje
gida ka dauki motata ta hawa ka debo min sauran
yaran nan kuzo ku same ni a Bauchi.
Ban yi mamakin umanin da ya yi wa Balan ba,
don nasan tsakaninsu ya wuce duk yanda ake zato,
mu'amallah yake yi dashi irin na da da uba, tunda
takai ma ya gaya min ya gayawa Umahmah cewar
Bala shi ne mijin da zai bata in har lokacin auren
yazo muna raye.
Na daga ido na kalle shi cikin natsuwa, na
tambaye shi wani abu ya faru ne? ya ce me ki ka
gani? Na ce uh'uh nayi shiru naci gaba da abinda
nake yi, shima ya kashe wayoyin nashi ya kara
gyarawa Baba Yahya jinginon da yayi a jikinshi yana
bacci wai don ya kara jin dadi.
Jimawa can sai naji ya ce min ke a rayuwari ai
ke 'yar gata ce Humairah nayi maza na ce mishi da
111
aka yi me? ya ce to kin rayu tare da uwa da uba da
Kakanni na bangaren uwa da uba.
Ki duba kiga Hajiyar Giyade irin yawan ran da
baiwar Allahn nan tayi, bara ne fa ta rasu. Nayi maza
na ce mishi eh, ai daga rasuwar tata ne ma na kara
tsorata da rashin lafiyar Mallam.
Ya kalle ni cikin natsuwa ya cc min, to ki kara
tsorata Humairah, Mallam zai yi ta zama a duniya ne,
jikokinshi na farko-farkon fa sa'o'in Inna ne,
mutumin da yayi irin wannan yawan ran ya bar
zuriya mai albarka irin ta Malla ya'ya da jikoki da
ya'yan jikoki ba a san yawansu ba.
Su Nusaiba nan duk ba yawan ranne yasa suka
san shi ba, ke kina zama kiyi nazari da tunani kan
ya' yan da suka rayu rayuwa irin tawa Humairah?
Nayi maza na daga ido na kalle shi ya ce, ni kam ai
maraya ne Humaira, tunda ban san mahaifiyata ba.
Babana ya rasu tun ban isa komai ba, a haka na
taso a tsakanin gidajen 'yan uwa da makwabta babu
wanitsayayyen da za ka gani a tsaye akan
al'amarinka, haka nayi ta dibi-dibin da nayi karatun
primary da secondary a lalace.
Saboda ina ganin wasu yaran unguwar yan
kadan suna zuwa a irin wannan lokacin ne fa Mama
tazo ta tafi dani, kafin zuwana hannun Mama ban
taba dandanar wani abu mai sunan dadi ba.
To ke fa? A cikin gatanki ki ka rayu mutanen da
112
suke sonki suna kewaye dake, don haka kar muje
gida ki samu jikinshi yayi tsanani kice zaki yi ta
rusa kuka wannan al'ada ce ta jahiliyya wacce
kuma aka hanata.
Cikin natsuwa da sanyin jiki na kalle shi na ce
jikin nashi yayi tsanani kenan ko? Bai yi musu ba
ya ce ch, gaba daya muka kama bakunanmu mnuka
yi shiru, sai addu'a kawai muke yi.
Mun isa Bauchi wajen sha daya da rabi ne na
safe saboda samnmakon da muka yi, ga kuma mota
lafiyayya uwa uba kuma shi ne mun godewa
Ubangiji ya tsare mana hanyar.
Tun daga karya kwanan layin runfuna ne a
kakkafe, Jama'aa ciccike har lokacin kuma Jama'a
isowa suke tayi, jikina ya dauki rawa kar-kar-kar.
Ado ya kama ni ya rike a jikinshi.
Kiyi hakuri Humairah, tun a hanya an gaya min
Mallam lokacin shi ya yi, ban gaya miki ba ne don
kar tafiyar ta zamo mana mai tsanani da yawa, kiyi
kuka ta hanyar zubar da hawaye ba laifi ba ne,
amma kar kiyi wani abinda ya sabawa Shari'a.
Tunda kullum a cikin karatu ki ke, karatu na
addini. To shi karatu da ki ke ganinshi yanda duk
ya kai da yawa to bai da wani amfani matukar mai
shi din ba zai yi aiki da abinda ya sani ba.
Shi yasa ma sai aka ce mana babu wani sani sai
113
wanda aka yi aiki dashi. Ade yana yi min
wadanan bayanan tuni ni kam awaye da majina
zuba kawai suke yi min.
Jama'a suka tartaso don ganin isowar Ado,
suna yi mishi sannu da zuwa Alhaji, barka da
isowa, abin da suke fada mishi kenan yana
amsawa, amma hankalinshi yana kaina, na yanda
zan yi in wuce cincirindon Jama'ar da ke zaune in
shiga gida.
Rike Mamanku Nusaiba, tayi maza ta kama ni
ta rike ungo jakar nan Hindatu, itama ta karba, to
maza Umahmah kuje. Haka muke wuce in na wuuce
inda maza suke 'yan uwana suka atre ni don an riga
an ji isowata.
Muna shiga gida na saka kuka sosai sai dai ban
yi ihu ko wani abin da ya saba ba, na riga na sani
ihu ko sabo ba zai dawo min dashi ba, ba zai
amfanar da mu da komai ba šai dai ma ya zame
mana wani sanadi.
Ubangiji ya gafarta mana.
"Sannu da zuwa Hajiya." Mafi yawan mutane
abinda suke fadi kenan, ina amsawa. Manya kuma
da suka fi kowa sanin abinda ke tsakanina da mai
babban allo suna ganina cewa suke yi.
Uh uhun, sai hakuri Humairah, yau kin rasa
Mallam, wannan maganar ita ce tafi komai Rara
114
tayar min da hankali ia karyar min da zuciya gaba
daya gidan a cike yKe har tsakar gida babu masaka
tsinke.
Tabarmi ake ta shisshimfidawa saboda iyali
sun riga sun hadu. amma kowa yana cikin
natsuwarshi babu koke-koke, babu maganganu a
koma gefe ana ta hira ana ba da labari a gidan
mutuwa.
Kowa cikin natsuwarshi yake, in ma yana
istigifari ko salatin Manzo ko kuma yana zaune
cikin jimami saboda yasan tilas watarana shima
zata zo kanshi.
Dakin Hajiya 'yar dubu na fara shiga can kusa
da ita naje na zauna saboda tana hango ni ta shiga
kokarin samar min wurin zama a kusa da ita din,
kama ni tayi ta rungume a jikinta tana fadin sai
hakuri, sai hakuri sai hakuri. Bar kukan haka kuyi
tayi mishi addu'a,.
Ina share hawaye ina ce mata ban gan shi ba ne
Hajiya da na ganshi wata kila da ya gaya min wani
abu, ta ce da kin ganshin ma maganar guda daya
ce, ita yayi ta nanatawa kuyi hakuri da gidajen
aurenku, kuyi bakuri da zumuncinku, bai fadi
komai ba bayan wannan.
Ranar da mijinki yazo kuwa lafiyar shi kałau
sun kai awa biyu a falon shi su biyu ya hana a shiga
115
bayan tafiyar nashi ne ya soma kukan ciwon kai
ashe tafiya ce tazo ban cewa Hajiya 'yar dubu ban
san Ado yazo wurin mai babban allo ba, shiru
kawai nayi.
Yan uwa suka yi ta baro in da suke suna zuwa
yi min ta'aziyya da na natsa nima sai na mike naje
na yi wa wadanda suke gaba dani lokacin ne naga
inda su Nusaiba suka yi masauki, wurin Hajiya
Kubrah.
Anyi zaman makoki kwana uku amma Jama'a
sai tururuwa suke yi suna ta isowa a cikin gida ana
ganin kamar za a kara zuwa bakwai sai kawai
Alhaji Maikudi ya shigo ya kara gaida Janma'a ya
ce to yau kowacce ta shirya ta tafi dakinta ya isa
haka.
Duk inda muke ba zamu fasa yi wa Mallam
addu'a ba, har sai ranar da tamu tazo ta same mu,
muka ce haka ne.
Muka tashi daga gidan rasuwa muka bi Inna
zuwa gidanmu, can ma gida yayi matukar cika
saboda su Bala da yara sun iso har iyayen Balan ma
Sun zowa Ado ta'aziyya, ga Yaya Ibrahim da
iyalanshi gaba daya, ga su Ruwailah har da su Baba
Tanimu.
Ga mutanen arziki kawayena da a yanzu nake
mu'amallah dasu matan abokan Ado, Babana va
116
shiga dawainiya da Jama'a, Zubaida ma haka, tun
da ita kam Sa'a can dakinta ma ta sauka gaba daya.
Shigowa nayi wurin Inna na samu Kawu Ado
da abokinshi na tuntuni, Mallam Umar wanda
yanzu shi da Inna babu wanda yasan tsakaninsu,
saboda mu'amallar dukiyar da suke yi.
Suna zaune kan shimfida a kasa su biyun ita
kuma Inna tana daga can cikin daki kusa da bakin
kofar dakin tana rike da labulen don ta rinka
hangen su don suji dadin maganar da suke yi.
To mutuwa kam ba