Showing 27001 words to 30000 words out of 180982 words

Chapter 10 - CAPTAIN AHMAD JUNAID COMPLETE Book .txt

"ni da ita muka yi girkin, tuwo da vegetable soup" ya hade rai yace "Who ask yhu" dariya tayi tace "Toh don ma na gaya maka" ya tabe baki ya mike ya dauki wayarsa ya nufi kofa, mikewa tayi ta bi bayansa da sauri, sai da suka fita yace "Hajja fa?" Tace "Bata nan taje gidan kawarta yau, kasan gobe xa mu koma" ya kalleta yace "Wa yace maki tare xa ku koma, bayan Abban ki yace ya ba mu ke" hade rai tayi tana kallonsa tace "Wa yace maka haka" murmushi yayi ya bude kofar parlour'n Mumy ya shiga ta bi bayansa. Kasa ta xauna tana kallon Mumy tace "Mumy wae ba da ni Hajja xata tafi ba gobe?" Mumy tace "ba tace nan xata bar ki ba" hawaye ne ya cika idonta tace "A'a ae ni ban ce xan xauna ba" Mumy tayi dariya tace "Toh bari idan ta dawo sae ki gaya mata, Meye abun kuka" dariya Junaid yayi yace "Ae sai dai tayi na jini nan xata xauna ita da fatima da khadija" ta fashe da kuka tana kallon Mumy, Mumy ta hararesa tace "kaga wuce dinning ka ci abincin ka bana son haka" mikewa yayi ya nufi dinning yace "Yi hakuri Mumy" mikewa Humainah tayi xata fita daga parlour'n Mumy tace "Ina xa ki" tana goge fuskarta tace "Xan je in jira Hajja" Mumy tayi dariya tace "Ai yanxu xata dawo, xo kiyi xaman ki a nan ki jirata" bata tsaya ba tayi ficewarta a palon. Har aka kira Magrib Junaid na kwance palon Mumy duk ya rasa yanda xae ce mata xai fita, mikewa yayi ya nufi toilet din palon yayi alwala ya fita xuwa masallaci, yana dawowa ya nufi part din Abba sanin ya shiga yanxu, Hajiya ce a parlour'n tana jera masa abincin supper a kasan lallausan rug din tsakar parlour, ya karasa ciki kansa a kasa yace "Ina yini?" Hade rai tayi tace "Ka fita don Allah abinci xai ci ynxu" tsayawa kallonta yayi, dai dai lkcn da Abba ya fito daga bedroom dinsa, Abba ya karaso cikin palon yana kallonsa, karasawa yayi inda Abba ya xauna, ya xauna daga kasa shi ma, a hankali yace "sannu da dawowa Abba" Abba yace "yauwa sannu, ya aikin?" Har lokacin bai dago ba yace "Alhmdllh!" Abba yace "Gud! Daxu baka shigo gaishe ni da safe ba" shafa kansa yayi yace "Na shigo Umma tace kana bacci" Abba yace "Ohk, amma baka karasa bedroom ba" junaid ya gyada kai kawae, Abba yace "kafi kowa sanin bana baccin safe ae" shiru Junaid yayi bai kuma cewa komai ba, kallonsu kawae Hajiya keyi ta gefen ido tana jera abincin da take rai ba dadi don bata so haka ba, Abba ya sauko kasa ya jawo babban food warmer, ya dau plate xai dibi shinkafa, Junaid ya karba yace "Bari in xuba maka Abba" sake masa spoon din Abba yayi, ya dibi shinkafar da stew a gefe da cow meats, snn ya xuba masa vegetables a kai kamar yanda ake masa, Abba ya dauki wani spoon din yace "Bismillah" sai da Abba ya fara ci sannan Junaid ya debi shinkafar a hankali ya kai bakinsa, Hajiya kamar ta hadiye xuciya ganin ko ta kanta Abba bae bi ba, taunar abincin kawae junaid yake ba don yayi masa ba, banda girkin Mumynsa babu na wanda yake ci, girki in ba nata bane ko kallonsa bai yi, shiyasa a ko da yaushe take bata tym dinta tayi masa girki, a tare suka gama cin abincin da Abbansa, bai yi Mamakin sakkowan Abba da wuri ba don in dai suka hada sa da shi, bai daukan lkci yake kuma jawo sa jiki, kwata kwata baya fushi mai tsayi da only son din nasa, hakan ba karamin daga ma su Hajiya hankali yake ba, sun dai rasa yanda xa su yi da Junaid a gidan, a tare suka tafi masallaci sllhn Isha da Abba, sae da suka dawo ya ba Abbansa hakuri a kan abinda ya faru jiya, Abba yace "Its Ohk, ka dai kiyaye halshan ka nan gaba" yace "In'sha Allah Abba" sun jima suna hira da Abba sannan yayi masa sai da safe ya mike ya fita ya shiga part din Mumy, tana xaune palo tana kallo, ya xauna gefenta ya dauki remote xae canxa tasha, Mumy ta karbe remote din tace "ya haka, bari a gama program din mana" kallon Humainah dake kwance kusa da fatima yayi yace "Har kin hakura xaki xaunan kenan?" ta daga kai tana kallonsa bata tanka sa ba ta dauke kai, Mumy tayi dariya tace "babban kawai" bude kofa aka yi hade da sallama, Junaid ya kalli agogo jin muryan El-Ameen, ya ga tara da rabi, Mumy tace "Kai dai baka jin fitan dare koh El-Ameen" junaid yayi murmushi yace "Kin manta likita ne Mumy" El-Ameen ya karaso parlon ya xauna yana murmushi ya gaida Mumy, da fara'a tace "lfya lau bokon turai ya aiki" yace "Alhmdllh Mumy" Fatima tace "Welcome bro" yace "Thank you sis" kallon Humainah dake xaune hankalinta na gun kallo yayi sannan ya kalli Junaid, Mumy tace "baki gaida yayanki ba Humainah" ba tare da ta kallesa ba tana ci gaba da kallonta tace "Ina yini" idonsa na kanta yace "Lfya lau" hira suka dinga yi da Mumy, ganin hiran ba me karewa bace Junaid ya mike ya nufi kofa yace "Ina part dina in ka gama karyan" dariya Humainah tayi a karo na farko ta kalli El-Ameen da ya hade rai yana kallon Junaid, Mumy ma tayi dariyar tace "Ae dae ya fi ka wllh tun da har yana daurewa yayi karyar" Junaid dake bakin kofa ya saka dariya yace "Surutun fa iyakansa a gida Mumy, mutumin da ko magana bai iya yi ma mace ba a waje sai kame kame," El-Ameen yace "Ehh ae kai naga ka iya d'an rainin hankali" banda dariya bbu abinda Humainah ke yi Mumy da fatima na taya ta, Junaid ya juya ya fice daga parlorn yana murmushi, mikewa El-Ameen yayi yace "Bari in je Mumy" Mumy tace "Toh fatima xata kawo maku abinci" toh kawae yace ya fita, Part din Junaid ya nufa ya samesa xaune a parlor ya kunna Tv, El-Ameen yace "Yau ban gan ka ba, kuma I was calling tun daxu baka responding" Junaid yace "I wasn't in a gud mood ne yau" El-Ameen yace "Wacece wannan yarinyar dake xaune parlorn Mumy" Junaid ya kallesa yace "Ya aka yi" d'an sosa kai El-Ameen yayi yace "Umm, tana da kyau ne" dariya Junaid yayi yace really?" El-Ameen yace "What's funny, Allah tana da kyau" Junaid yace "Toh bari ta shigo" ko rufe baki junaid bai yi ba sai ga ta ta shiga palon da sallamarta rike da tray din abinci, El-Ameen ya sunne Kai murya can kasa yace "Don Allah ka rufa min asiri kar kace komai Junaid, wasa nake" Junaid ya fashe da dariya yace "Humainah" ae da sauri El-Ameen ya mike ya rufe bakinsa da hannu yana xaro ido, junaid ya dinga dariya yana tura hannunsa amma yaki sake sa, tabe baki tayi ta ajiye trayn hannunta tace "Mumy tace in kawo" da karfi Junaid ya tura El-Ameen yace "ke kin yi saurayi likita" ae ko rufe baki bai yi ba, El-Ameen yayi hanyar daki da sauri ya shige ya rufe kofar, Junaid ya dinga dariya har da rike kai, hade rai tayi tana kallonsa, can tayi tsaki ta juya ta fice daga parlon, kin fitowa parlor El-Ameen yayi har kusan Karfe goma, Junaid ya shiga dakin yace "Toh wai a haka xan baka kanwar tawa kana kunyar ta!" El-Ameen dake xaune gefen gado yace "ta tafi?" Junaid yace "Aa tana parlor" shiru El-Ameen yayi sai kuma ya mike ya cire shirt din jikinsa ya nufi bathroom, junaid ya bi sa da kallo yana dariya, wanka yayi ya fito sanye da bathrobe, ya nufi closet din Junaid ya fiddo pyjamas ya sa sannan ya dawo ya xauna yana kallon Junaid yace "Amma ba nan xata kwana ba dai koh?" Junaid ya hararesa yace "Nan din xata kwana" El-Ameen ya daga kafada yace "Ohk ni kam am spending the nyt here today, its late and bana son ta gan ni, I came purposely because of ur patient, they've diagnosed her, that is an mata genetic screening, brain scans, neurological exam i.e (checking of vision, hearing, and balance) and other tests, and you knw wat?" Shiru Junaid yayi yana kallonsa, El-Ameen yace "They've found out that she is suffering from post-traumatic stress disorder (PTSD), and this is a serious potentially debilitating condition that can occur in people who have experienced or witnessed may be a serious accident, sudden demise of a loved one, violent personal assault such as rape da sauransu, terrorist incident, or other life-threatening events, you know! A lot of them....." Daga haka yayi shiru yana kallon Junaid da ya kafa masa ido ko kiftawa bai yi, junaid ya sauke ajiyar xuciya ya shafa kansa a hankali yace "But! Is it treatable? I mean can it be cured?" El-Ameen yayi murmushi ya dafa sa yace "Of course yes! But it is difficult to predict how, when, or to what degree someone is going to get better, the major treatment for disorders are Medication, Rehabilation, psychotherapy, and brain surgery, but we are only going for Medication and psychotherapy yanxu, by Allah's own grace xa a dace in'sha Allah" d'an murmushi kawai junaid yayi, El-Ameen ma yayi murmushin yace "Sai dae kuma kudin da xaka kashe fa ba na wasa bane guy, daina murmushi" wani murmushin junaid yayi yace "Wannan ba matsala bane, Allah ya bata Lfya" El-Ameen ya d'aga kafada yace "Gud! But kudin treatment din nawa fa?" Junaid yace "Thought sai ka gama xaka amshi kudi" El-Ameen yyi murmushi yace "Ohk let leave it then"


*Haske writers association*




鈿� *Captain Ahmad Junaid*鈿�


_By Khaleesat Haiydar_鉁嶐煆�


15....


Mikewa junaid yayi yace "Ga abinci a parlor" El-Ameen ya d'an bude ido yace "ba kace tana parlorn ba" Junaid ya hararesa yace "Me xata xauna yi min, ta tafi tun daxu" daga haka ya shige bathroom ya bar sa xaune dakin, mikewa El-Ameen yayi ya isa kofa ya bude yana lekan parlorn, ganin bata nan ya fita, sae da ya kulle kofar parlon da key sannan ya dawo ya xauna gaban abincin, iya wanda xai ci ya diba, ya dauki remote yayi powering tv yana ci yana kallo, kwanciya yayi bayan ya gama cin abincin kan dogon sofa yana kallo, Junaid ya fito daga daki sanye da pyjamas, ya mika masa wayarsa yace "Ummi na kiran ka" mikewa El-Ameen yayi xaune da sauri ya karbi wayar ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren tace "El-Ameen kana ina ne Abban ku duk ya ishe ni da kira, what's wrong with you this days baka xaman clinic, yace tun rana rabon ka da can kuma ni baka dawo min gida ba" Kallon agogo yayi yaga har goma da rabi ya kwantar da murya a hankali yace "Kiyi hakuri Ummi ina gidansu Junaid bai da lfya ne, so I have to stay over da naga dare yayi" Ummi tace "Karyar ka kenan kullum kana gidansu junaid, are you alright Ahmad?" Da sauri yace Ummi ga junaid din ma ki tambayesa ki ji, yana fadin haka ya mika ma Junaid wayar, junaid ya karba suka gaisa da Ummi, tace "Wai baka da lfya junaid" kallon El-Ameen yayi sannan yace "Um Ummi" tace "Toh Allah ya sauwake nayi xaton karya yake min, kace masa ku kira Abba kuyi masa bayani don yana can ya cika" junaid yayi murmushi yace "Toh Ummi" daga haka suka yi sallama ya ajiye wayar, El-Ameen yace "Kaga situation din da ka jefa ni ciki yanxu kai da patient din nan taka ko Captain, kai kullum baka fashin aiki, sannan baka kai wa bayan magrib baka shiga gida ba ni ko ka barni ina ta gantali a titi ko da yaushe, na ma daina aikina a clinic kullum safe dare ina hanyar duba mahaukaciyar ka, look am not taken less than 500k idan na gama treating din mahaukaciyar nan" Junaid yayi murmushi yace "Sure! Wannan ba matsala bane I will pay you."
Da asuba tare Junaid da El-Ameen suka fita xuwa masallaci, suna dawowa El-Ameen ya koma yayi kwanciyarsa ya ci gaba da bacci, Junaid yayi murmushi ganin haka, a xuciyarsa yace lallai kam sleep well, toilet ya shiga cikin minti ashirin yayi wanka ya fito ya shirya cikin khakin sa, kamshin turarrukansa ne ya tada El-Ameen, ya mike xaune yana kallon agogo yace "Wai kai barin gari xaka yi haka da asuba ne da baxa ka bar mutum yayi baccin safe ba captain, duk ka ishe ni ka hana ni bacci don xaka aiki" Junaid na saka wristwatch dinsa yace "sorry, go back to ur sleep, ni yanxu ma xan bar maka dakin" Yana fadin haka ya dauki wayarsa da hularsa ya nufi kofa, El-Ameen yace "Wait, wai Karfe nawa yanxu?" Junaid yace "6:40" daga haka yace "May be ka same ni part din Mumy in ka fito da wuri" El-Ameen yayi tsaki shi kuma yayi ficewarsa. Har El-Ameen ya koma ya kwanta ya mike da sauri tunawa da yayi akwae alluran da yake ma patient dinsa bakwai da rabi. Toilet ya shiga yayi wanka a gurguje ya fito, cikin mintunan da basu wuce goma ba ya kintsa cikin blue shirt da black jeans a closet din junaid, ya feshe jikinsa da turare ya dau wayarsa ya fice daga dakin, yana isa part din Mumy suka kusa cin karo da Humainah xata fito, ae da sauri ya sunkuyar da kai ya bata hanya ta bi ta gefensa tayi gaba abunta, ya sauke ajiyar xuciya ya shiga parlon, ko kallon Junaid dake xaune yana shan tea bai yi ba, ya gaida Mumy ta amsa tace "ga breakfast dinka can a dinning" yace "A'a Mumy sauri nake wlh, idan naje office xan yi" Mumy tace "Kan ka daya kuwa, Karfe nawa yanxu da baxa ka tsaya kayi break ba" kallon agogo yayi yace "Mumy wllh am in a haste ne..." junaid dake kallonsa yace "Da wannan surutun da yanxu ka gama hada tea" hararan sa yayi sannan ya karasa kusa da shi yayi kasa da murya yace "look akwae wani injection da xan ma patient dinka ne b4 7:30, shi yasa nake sauri," da sauri Junaid ya kalli Mumy dake kallonsu yace " Ohh Mumy ashe emergency aka kira sa ne fa" Mumy ta tabe baki tace "Kwa ji da gulmar ku ba ruwana" El-Ameen ya d'an yi murmushi yace "Ko xuwa Karfe goma xan dawo inyi wllh Mumy" Mumy tace "Ka fa rantse" dariya yayi yace "in'sha Allah Mum" mikewa Junaid ma yayi ya shiga bedroom din mumy ya dauki kardigan dinsa yasa don garin da d'an sanyi, ya fito yace "Mumy sai na dawo" ta bisa da kallo kafin ta tabe baki tace "Toh dai kar ka manta ku shiga kuyi wa Hajja sallama don yau xata tafi, ko Abba ma baku shiga kun gaida ba bare mutan gidan" Junaid yace "Xamu shiga" daga haka suka fita daga parlon, sae da suka fara shiga part din Abba suka gaida shi sannan suka yi part din Hajja, tana ta hada kaya, Humainah na xaune gefenta sai rusa kuka take ita ma da tata jakar a gefenta, Hajja na mata ruwan bala'i tana cewa tayi kadan ta koma da ita tunda dama ba ita tace ta biyo ta, xamanta daram a gidan ko suma take, Junaid ya fashe da dariya yana kallon Humainah, ita ko tana ganinsu ta hadiye kukan ta sunkuyar da Kai kasa, Hajja tace "Atoh, ka dai gan ni da gantalalliyar nan wae sae ta bi ni Amadi, sae kace ance mata wahalalla nake kamar irin ni na ce ta biyo ni din nan shegiya, nufin ta in koma da ita muna galallawa a titi, to dadin abun dai ba kudin banxa gare Muhammad ba, kuma ubansa Ahmad bae ce yaje xae gani ba bare ya biya kujeru biyu na jirgi" Junaid ya dinga dariya yana kallon Humainah, El-Ameen yyi murmushi ya gaida ta, ta kallesa ta gefen ido ta ci gaba da abinda take ba tare da ta amsa ba tana ci gaba da yi ma Humainah masifa, dariya yayi yana shafa kansa don yasan me yasa bata amsa ba, Junaid ya ciro dubu talatin da ya tanadar mata dama ya ajiye gabanta yace "Gashi ni da El-Ameen ki sha ruwa da dabbino a hanya kar ki je kina masu amai a jirgi" ta washe hakora tana kallon El-Ameen tace "Toh Allah maku albarka, ga kuma amanar jikata a hannun ku, don mayu sun yi yawa gidan, Amina na damka ma ita, tamkar yanda xata yi ma fatima xata yi mata" Junaid yayi murmushi yace "In'sha Allah" Hajja ta kara da cewa "Kuma ga maganin tsari kala kala can na kai ma uwarka idan taga dama ta baka, ka kuma sanma marowacin abokin nan naka don duniya bbu gaskiya yanxu, barin kai da kiri kiri matan ubanka ke nuna basa sonka" shi dai El-Ameen sae kallon agogo yake don bai son lkcn nan ya wuce duk hankalinsa yayi gun patient dinsa, Junaid yace "Toh Hajja" kallon Humainah yyi ya mike yace "Ae sae ki dauki jakar ki kai bangaren Mumy" ta fashe da kuka, Hajja tace "Tashi ki ban waje yar wahala, bbu inda xani da ke ki xauna gidan wan ubanki don shi xaki gani ranan gobe kiyama" Humainah na kallon Junaid cikin kuka tace "Ya Ahmad kace mata don Allah ta tafi dani wllh bana son in xauna gidan nan kullum fada ake yi" Hajja tace "A haka xaki saba ki koya ki iya kema" Junaid ya fice yana dariya ta bi bayansa da sauri, El-Ameen ya kuma yi ma Hajja sallama ya fice shi ma yana danne dariyarsa wai kullum fada, sae da suka fito compound Junaid ya kama hannunta yace "kinga ki bari ta tafi sai in maida ke next week I promise" da haka ya lallabata tayi part din Mumy tana kuka, Umma na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login