Showing 69001 words to 72000 words out of 82053 words
Chapter 24 - Ni Da Shugaban Kasa Complete Book Reefat Yahya .txt
har kina xancen wani bako a gaban idona"
Ta marairaice fuska
"Bb is risky fah..idan daddy yaje nemana bai sameni ba fah ?
" sai yazo nan ya sameki ..kinga daga nan xai San lallai baki son auren n am sure baxai miki auren dole bah"
Haka dai bash da umaima Suka kasance daga karshe ma xama sukayi suna ta hirarsu irin ta masoya sun manta da wani ismaeel a can.
Ismaeel yana xaune yana danne2* a wayarsa bayan yan mintuna ya duba agogan dake daure a hannunsa ta share 30 mins bayan kuma tace 10 mins anyways.. Ya gyara kwanciyarsa a kujera ya cigaba da danna wayarsa.a can falo kuwa suna hira ckn faraa , wayar baban ismaeel ne yayi ruri daga nan ya daga ya fita waje shuairat ta gyara xama tace
"Daddy wata alfarma nake nema"
"Fadi bukatarki ya'ta"
"Daddy xancen auren nan da xaayi ina ganin gara a hakura "
"Sabida me?
"Umm..umaima bata son auren tana da wani Wanda take so"
Dariya yayi sannan ya juya yana kallon mr president Wanda tun da Suka fara maganar bai sanya bakinsa a cki bah..daddy yayi murmushi yace
"Wato mijin naki ne ya turaki koh"
Shuairat tayi saurin girgiza kai tace
"Bahaka bane daddy, kawai gani nayi umaima...
"Aysha!
"Naam daddy"
[2/21, 2:42 PM] Reefat: πNI DA SHUGABAN KASAπ
*90*
By *Reefat yahya*
Daddy ya cigaba da maganarsa
"Aysha kada ki biye ma mijinki , shi boko yasa a gaba idan na biye masa cewa xaiyi sai ta gama masters b4 ya aurar da ita"
"Daddy bahaka bane..dama
Hannu ya daga mata nan tayi shiru da bakinta..yace
"Zancen aure babu fashi , kuma na fasa jiran ta gama makarantar ma..bari Alhajin ya shigo"
Shuairat xata CE wani Abu baban ismaeel ya shigo tare da sallama daddy yace a kira ismaeel a waya su taho da umaima.
Yana can xaune a falon har ynxu babu umaima babu labarinta wayarsa ta hau ruri mahaifinsa ne ya daga yace
"Ku samesu a falo"
Daga nan ya kashe wayar ta tashi ya wuce falon da suke.ya karasa cki tare da sallama bayan ya xauna daddy yace
"Ina umaima?
"Uhm..tun dazu ta tafi, wani uncle waye..uhmm
Shuairat tayi carab tace
"Lahh..har ynxu basu dawo bah..dama ni nace suje ta xabi kalan furniture's da take so ita da uncle bash"
Idanunta Suka fada ckn na mr president ya harareta tayi Sauri ta tashi tsaye tace
"Bari na kirasu daddy ina zuwa"
Daga nan ta fice bata jira jin amsar su bah.
Bangaren baki ta fara xuwa tana nemansu taji murya kasa2* a dayan dakin nan ta tura kofar fuska a murtuke ta samesu suna xaune suna hira ckn kwanciyar hankali harara ta watsa musu tare da cewa
"Sai ku nuna ma duniya akanku aka fara soyayya"
Umaima ta tashi ta karasa kusa da ita
"Lfy mom sultan"kwafa tayi tare da cewa
" zaku gane ai ..kixo ana Neman ki"
Jikinsu yyi sanyi bash yace
"Sisy any progress?
"Wane irin progress..Abu yana Neman tabar barewa"
"Wat hpn"
"Muje dai kuji da kunnenku"
Daga nan ta juya tayi tafiyar ta umaima da bash kuwa sunyi jugum kowannensu yana tunani daga bisani Suka wuce falon.
Bayan kowa ya xauna daddy ya fara magana
"Ismaeel ina fatan babu matsala"
"Ba komai Abba mun daidaita mun amince da juna"
Ckn Sauri umaima ta daga kanta sukayi ido 2 dashi ta sake sunkuyar da kan, daddy ya cigaba
"Masha Allah..dama haka muke son ji Allah ya muku albarka"
"Ameen" kowa ya amsa banda bash da umaima
"Ynxu tunda sun fahimci juna ni na saka rana nan da wata 1 "
Tare Suka hada daga kai suna kallon juna babu Wanda ya lura dasu sai mr president ya kawar da fuskarsa tamkar baisan meke faruwa bah..hawayene Suka fara gangarowa a fuskar umaima ba shiri ta tashi tabar falon baban ismaeel yace
"Meyake damunta Alhaji naga kamar kuka take yi"
Murmushi daddy yake w
Sannan yace
"Babu komai nasan ta tuna da mahaifiyarta ce"
"Ka tabbata..? Kodai bata son auren ne"
"Ko kadan ..nasan tunowa tayi da marigayiya zainab Allah yajikan ta yasa ta huta"
"Ameen"
Haka Suka cigaba da hira bash ma barin falon yayi ya koma bangaren baki ya xauna ya buga uban tagumi yana Neman mafita.
Jirgin yamma su daddy Suka bi Suka koma Lagos mr president ma hankalinsa yaki kwanciya sai ynxu ya fara jin tausayin Ya'r tasa shi da kansa yaje har daki ya sameta yana bata hakuri dakyar ta daina kukan da take.
****bayan kwana 2 bash ya kwanta zazzabi ya rufeshi ya tare a gidansu yaki komawa gidansa , kullum shukrah tana xuwa dubansa ko kallo bata ishe sa bah.gashi umaima ta kashe wayoyinta gaba daya hnklinsa a tashe yake mama tana masa nasiha akan ya rungumi kaddaara Amma Sam baya sauraronta ya xama kamar wani xautacce daga karshe ya tashi ya shirya ckn kananan kaya yayi kyau sosai duk da ramar d yayi ya fada sosai , mama ta shigo dakin rike da magungunasa ckn mmki ganin yana fesa turare da alama fita xaiyi tace
"Babana ina kuma xaka je ..kaida baka da lfy"
"Na warke mama.."
"Toh ina xa ka?
"Zanje ganin umaima domin wayoyinta a kashe suke, xan duba ko lfy"
"Lfy kalau suke dazu munyi waya da Ya'r uwarka da akwai wani Abu ai kasan xata gaya min"
"Naji...Amma nikam sai naje"
Daga nan ya xare makullin mota yyi ficewarsa.
Umaima tana xaune a dai2* windon dakinta taga shigowar motar bash nan kuwa da gudu ta fito har tana tuntube masu aiki sai kallonta suke bata kulasu bah tayi hanyar last floor na kasa a bakin kofa Suka ci karo turus yaja ya tsaya...sun Dade sun kurawa juna ido daga bisani yayi karfin hali yace
"Meyasa zaki kashe min waya?
"Uhmm...dama
dama me? Just tell me dat baki damu da halin da muke cki bah, kina nan ckn kwanciyar hnkli ni ko ina fama da jinya"
Wato Kalmar da tafi tsana kenan a ce duk son da take masa Amma se ya goranta akan shiyafi damuwa da ita....
Idanunsa sun kada sunyi ja yace
"Umaima nasan kina sona Amma tsoronki ya hana ki fito fili ki nuna musu cewa baki son auren ni kike so ki aura y??
Kuka ta fara Mara sauti ya harde hannunsa a kirji ya tsaya yana kallonta daga bisani yace
"Mafita xaki kawo ba kuka bah pls"
ta cigaba da kukan
"Haba mana bby u knw I hate doz tears ki bari pls bana son ganin ki ckn wannan hali"
Ckn Muryar kuka tace
"Toh Bb ya xanyi..wane mafita xan kawo ? Ni gaba daya kwakwalwata ta toshe na rasa samun mafita kuma next week ance xaa kawo lefe"
"Wat???π³π³ next week? U know wat umaima kawai ki kira yaron ki CE masa baki sonsa kina da wani daban , daz d only solution"
"Bb ar u sure it'll work?
"Am very sure baby Nah try it"
"Ok muje na dauki phn dina yana can daki"
"Ok lets go"
Daga nan ta shiga gaba yana biye da ita a baya Suka haura xuwa sama don daukar wayarta.
Shin xata kira ismaeel kuwa??
Zai amince da bukatar tata??
Hmmm...muje xuwa
Lov u allππ
[2/21, 2:42 PM] Reefat: π NI DA SHUGABAN KASAπ
*91*
By *Reefat yahya*
A hanyarsu ta xuwa daukar waya Suka ci karo da shuairat tabi su da wani irin kallo sannan tace
" dad naki yana son ganinki ynxu"
Gaisawa sukayi da yayan nata sannan tayi wucewarta sum sum umaima ta tafi falon baban nata yana xaune da jarida a hannusa ta shigo tare da sallama ta nemi waje ta xauna
"Gani nan dad"
"Ki shirya gobe zaku wuce Dubai shopping Ke da Aysha"
A hnkli ta daga kanta tana kallonsa sannan tace
"Dad...
"Bana bukatar jin komai daga gareki tashi ki tafi Allah ya Baku xaman lfy"
Kuka ne ya kubce mata da gudu tabar falon a hanya ta hadu da bash yana tsaye ya jingina da bango da alama ita yake jira..
"Lfy my bby "
bata iya furta masa komai bah ta wuce bangarensu a kujera ta fada tana kuka mai ban tausayi bash ya shigo ckn tashin hnkli ya xauna kusa da ita ya fara magana ckn kwantar da murya
"Bby kullum ina gaya miki bana son wannan kukan naki amma baki ji pls stop it"
Haka ya cigaba da bata baki dakyar ta sagaita kukan ta sanar masa abunda yake faruwa shiru basheer yayi yana jin wani radadi a ckn xuciyarsa ya rasa ma wani mataki xe dauka daga nan ya tashi ya fita ba tare da ya furta ko kalma daya bah.
Umaima ta cigaba da kukan da take bash kuwa bai tsaya ko ina bah sai gun mahaifinsa wani sabon hauka ya tada musu mama kam se kuka take tana tausayawa dan nata , suna lallabashi tamkar kara tunxura shi suke baba ya rasa ya zayyi kawai ya fice ya koma dakinsa ya xauna. Mama ce ta cigaba da rarrashinsa dakyar ya tashi ya ci abinci.
***washe garin...mr president ya raka shuairat da umaima airport jirginsu ya daga xuwa Dubai ya rage dashi da sultan kadai a gida. Umaima se kuka take shuairat tana rarrashinta a haka Suka kasance a ckn jirgin ma babu abunda take sai kuka.
Bash yana xaune a ofishinsa yayi jugum..tunanin duniya ya addabesa ynxu shikenan an rabashi da umaima ?? Yau saura 3weeks auren ta da wani bashi bah ..kwankwasa kofa akayi sectry dinsa ne ya shigo ya shaida masa yayi bakuwa ba tare da wani dogon tunani bah yace a shigo da ita.yana xaune ta shigo qamshin turarenta ya gauraye ofishin gaba daya ba shiri basheer ya daga kansa fara ce Sol daga ganin hasken nata na mai ne tana tauna cingam ji kake kas! Kas!! Wata shaidaniyar doguwar Riga ce a jikinta Wanda ya matseta gam Rabin kirjinta duka a bayyane fatee kenan...hannu ta daga masa ckn salon Jan hankali tare da cewa
"Hi basheer am fateemah "
"Aw daz gud..fateema me Ke tafe dake ?
"Well..actually ba wani Abu bah illa so da kauna"
Ckn Sauri ya daga idonsa ya jefa mata wani mugun kallo bata ji ko darr ba ta cigaba da cewa
"Na Dade ina kaunar ka baaheer, a rayuwata ban taba son wani namiji bah sai kai..pls ka amince muyi aure"
Wani murmushi yayi sannan yace
"Wai ba kece Ya'r uwar shukrah da ta kawo mata ziyara kwanakin baya bah"
"Yeah...u r right anyi haka Ashe dai baka manta dani bah"
Ya juya idanunsa tamkar mai shirin yin bacci ya nuna kofa tare da cewa
"U can leave pls..
"C'mon basheer kasan nafi matar ka da komai kuma ynxu ita bata da wani amfani tunda ba haihuwa xatayi bah"
Ya bude ido sosai yana mamakin kalamanta ya akayi tasan shukrah baxata kara haihuwa bah??...wato shi ya rike maganar as sirri bai sanarwa kowa bah amma ita tana can tana yada kanta tana tona masa asiri..tirr da halaye irin nata.
"Kayi shiru my love, ko kana bukatan lokacin tunani?
Ya watsa mata wani mugun kallo tare da cewa
"Tunani? Koda a ce matan duniya sun kare kece autar mata , wllhi na hakura gara na mutu banyi aure bah akan na aure ki fateema"
Daga nan ya tashi ya bude kofa yace
"Out..now"
Ta gyara xama tana wani juya idanu taji saukan mari tass! Sai da taga taurari..ya nuna ta da dan yatsa yace
"Ki lura da inda zakiyi iskancinki ni ba sa'ar yin ki bane , ki kula..kada na kara ganinki fita ki ban waje "
Ya karasa maganar ckn tsawa nan take ta fisge Jakarta tayi waje hawaye na bin kuncinta Marin ya shiga sosaiπππ tunda take a rayuwar ta babu Wanda ya taba cin xarafinta irin na yau, taxi ta tare ta gaya masa inda xata je ta biya kudin Suka dau hanya.
Shukrah tana xaune tayi nisa ckn tunani hawayene Ke sauka daga idanunta taji kamar motsi nan ta tashi Suka yi ido 4 da fatee ta rike kugu tana murmusawa ckn xafin nama shukrah ta cafke wuyar rigar ta
"Azzaluma me kike nema a gidana"
Wani irin dariya fatee take sannan tace
"Haba sahibar ki ce fah"
"Zan kasheki fatee kowa ya huta"
"Allah sarki yarinya har kisa kika koya..abun yayi sosai idan kin kasheni se ki karasa rayuwarki a gidan kurkuku umaima kuwa ta aure mijinki suyi rayuwarsu ckn so da kauna"
Shukrah ta sassauta rikon tana kallonta murmushi fatee tayi a karo na 2 daga bisani ta cigaba da cewa
"Oh...Ashe dai kinyi tunani mai kyau, ina son kisan cewa ba wai naxo Neman gafara kan abubuwan da na saki aikatawa bah ah 'ah..nazo ne don sanar dake cewa burina na son auren mijinki bai cika bah, kuma mijinki yana yan yana shirin kara aure nan da sati 3 xai auri umaima Ya'r gidan shugabankasa na da.ynxu haka suna kasar waje tare da aminiyarki suna siyayyan aure kuma.....
Shukrah bata bari ta karasa maganar ba shaketa sosai tamkar xata kai fatee lahira ckn daga murya tace
"Karya kike bakar munafuka me bakar aniya..
"Wllhi da gaske nake , idan baki yarda bah ki kira aminiyar taki ki tambayeta suna ina xata gaya miki"
Shukrah ta xame ta xauna a kasa ta tallabo kanta dake faman tsarawa a hnkli ta CE
"Fatee da gaske baban waleed zai auri umaima ? Kuma har ansa rana shine baxai sanar dani bah"
"Ehh..dama ina da masu bani labarin duk wani movement din mijinki su Suka gaya min abunda yake shirin faruwa"
Shukrah ta fashe da kuka mai ban tausayi fatee kam ta warce Jakarta tace
"Toh shukrah sahiba! A rungumi kaddara a kiyaye gaba kinga tafiyata sai wata rana tunda ma Allah yaso ki mijin naki yaki amincewa da aurena da kukan zaifi na ynxu don haka ki godewa Allah umaima xaa kawo miki ba niba"
Daga na tasa kai tayi ficewarta tana faman gyara gaban rigarta tana kunkuni tana cewa
"Boka kuwa xeci uwarsa ba ni xai yiwa karya bah...hmm gashi bukata bata biya bah wllhi xai gwammace kida da kara2"
πππ
Muje xuwa
[2/21, 2:42 PM] Reefat: πNI DA SHUGABAN KASAπ
*92*
By *Reefat yahya*
*sorry fans bana yawan posting dese days pls bear wit me kunsan duniya up n down ππ just busy hre n dre ne kawai..Lov u all, godiya gareku masoyana masu turamin mssgs ta private da masu kirana a waya tnx a lot Lov u all*
Fatee tana son raba tsakanin shuairat da shukrah shiyasa ta sanar da ita cewa basheer zai auri umaima..tana barin gidan ta xarce filin jirgin kasa don komawa kd.
Shukrah kuwa babu abinda take sai aikin kuka tana jin xuciyarta tamkar xata fito fili wani haushin shuairat take ji tasan tabbas aikinta ne hada auren bash da umaima lallai sai ta dauki mataki akansu duka xata nuna musu kuskuren da Suka tafka..umaima kuwa xatayi regret.
A can UAE wato birnin Dubai shuairat ce take shiga da fita xuwa kasuwanni daban2* umaima dai se kallo don bata xabi ko cokali bah haka nan shuairat ta fita sabgarta kullum a kasuwa suke yini idan sun koma masaukinsu kuma shuairat xata kira masu gyaran jiki a gyarata duk da bata so.
Haka Suka kasance har tsawon sati 2 sannan sukayi haramar dawowa 9ja.
Bayan dawowarsu da 2days aka kawo lefe akwati set3 da tulin kaya masu kyau da sada, daga nan aka soma shirye2*n biki yau saura 1 week ciff.duk yadda bash yaso ganin umaima abun ya faskara saboda shuairat ta gindaya mata sharuda sosai bata xuwan ko ina kullum tana ckn dakin baccinta gashi an kwace wayarta bata aiki se kuka, ga yan uwa sun fara xuwa shuairat se shiga da fita take Sam bata da lokacin xama ita ta kira tela yaxo har gida ya karbi dinkunan da xaa yi, mr president ya bude bakin aljihu ya xuba kudi sosai duk abunda ake bukata sun rigada sun siya ..
Shuairat ce kwance a dakinta salman yana gefe yaron ya girma yayi wayo sosai gashi da girman jiki tamkar ya'yan turawa ga fara'a ga kyau tubarakallah..mr president ya shigo yana waya bayan ya gama ya juya gun matarsa suna fuskantar juna
" sorry my Lady gskiya kina kokari Allah ya miki albarka"
"Ameen my man"
tana murmushi ta koma kusa dashi ta xauna tare da cewa
"Nasan ka gaji kwanta na maka tausa"
Babu gardama ya mike akan gado kwanciya yayi rub da cki nan ta fara masa tausa har wani lumshe ido yake tamkar mai shirin bacci shuairat tace
"Dad umaima"
"Uhmm..
"Pls gida nake son xuwa "
"Yaushe?
"Ko xuwa anjima "
"Ba damuwa ki shirya driver ya kai ki"
"Tnx swt hrt"
Ta manna masa peck a kumatu murmushi yake haka ta cigaba da masa tausa har bacci yayi awon gaba dashi.
Ta gama shirinta tsab ta shirya salman sun yi kyau sosai ta sanar da masu aiki kan cewa su kula da umaima xata je gidansu baxata Dade bah, daga nan ta wuce gun mota driver ya ja Suka dau hanyar xuwan gidan su.
Falon babanta ta fara xuwa yana xaune da carbi a hannu dayake baa dde da yin sallar axahar bah..yana ganinta fuskarsa ya fadada da murmushi yace
"Ya'r baba..Barka da xuwa"
"Yawwa..
Waje ta nema kusa dashi ta xauna yasa hannu ya karbi salman yana cewa
"Waii...haka kike fama da wannan lukutin Alhajin yana wahalar min dake"
Dariya kawai take musu gskiya salman akwai nauyi kamar my boy *haneef*ππ.
Mama ta shigo tare da sallama ta tabe baki da ganin shuairat tace
"Oh..ni Fatima wato kedai kin nuna kinfi son mahaifin naki a kaina ..ah yayi kyau"
"Fateema wai kishi kike dani"
Baba ya fada yana dariya shuairat ta tashi ta fada jikin mama
"Mamana I miss u"
"Ba wani nan kin nuna kinfi damuwa akan mahaifinki"
"A'a mama kema kinsan ina sonku gaba daya"
Suna dariya mama ta dauki salman tana cewa
"Maigida nasan kai kam kafi sona koh"
Salman se wage baki yake kamar yana jin abunda take cewa baba ya karbe maganar yana cewa
"Wannan Dan lukutin maigidan naki yana ramar min da