Showing 33001 words to 36000 words out of 38921 words

Chapter 12 - IMRANFAD By Maman Noorul Hudah-1-1.txt

23 Jan 2025

4038

bayan anty rukkaya yace"oh nasan tana gidan ki"zuwa yayi zai amshi kausar sai taki zuwa yace"that strange "




Kukan da anty rukkaya ta fashe dashi ne yasa ya kalleta yace"lafiya? "


Cikin kuka tace"fadila ta bata"a fusace ya juyo yace "what?"


Tace"ka kore ta"


Yace"kina da hankali kuwa?me zansa in kori IMRANFAD? "


Cikin kuka ta bashi labarin komai yace"karya kike yi,hauka nike da zanyi wa IMRANFAD kishiya?"


Ummi tace"gaskiya ne kuma ka shirya fadila na dawowa saka sake ta"


Shidai Mahmud shiru yayi yana kallon ikon Allah


IMRAN yace"ummi wallahi karya ne ni ba kori FAD ba ai akwai camera a gidan nan"


Zuwa yayi ya Ciro secret cameras din gidan tare da d'auko laptop connecting yayi


Ya fara forwarding yana kaiwa wani wuri ya gan kamar ya duke fadila da sauri ya tsayar da shi


Kallo yake yi yana kuka ummi ma kukan takeyi Abba idanun shi sun kada sunyi jajur,


Dai-dai inda ya saki fadila ya rike kirji ai sai ya sume da sauri daddy ya karasa wurin shi Abba ko barin falon yayi


Daddy da Mahmud ne suka kaishi asibiti Abba ya salami malam da alkawarin zasu zo su ganshi kafin su bar garin


Anty rukkaya na komawa gida mummy tace" ya akayi ne,ina hajiya nan anty rukkaya ta sanar da ita halin da ake ciki


Bangaren fadila kuwa






Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IMRANFAD
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers we are the best among the rest.


πŸ…Ώ8⃣9⃣&9⃣0⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


'Bangaren fadila kuwa ta fara motsa hannayenta amma bata motsi


Shiko Dr sageer haka kawai yaji ya fara sonta ganin kausar na kiranta mummy


Ana kai IMRAN asibiti Dr suka fara aikin su,bayan wasu lokota Dr ya fito yace"daddy subi shi office"


Suna kaiwa Dr yace"a gaskiya akwai matsala saura kadan zuciyar shi ta buga in ya cigaba da sa damuwa a ranshi za a iya rasa shi,amma muyi nasara ceto rayuwar shi"


Daddy yace"zamu iya ganin shi?"


Yace"eh"


Ummi tace "mun gode"


Mummy ko cewa"tayi sai kaita asibiti ta gan IMRAN"


Anty rukkaya tace"ta bari ta gama girki"


Bayan minti talatin ta gama suka tafi hospital


IMRAN na ganin ummi ya fashe da kuka yace"ummi ya akayi nayi aure baku hanani ba?ummi na wulakanta IMRANFAD"


Ummi tace"nima ban sani ba dan nayi tafiya kafin in dawo anyi auren"


Yace"amma meyasa mummy bata hana ba?"


Nan fa ummi ta bashi labarin abin da ya faru dan ta tausaya me


Yace"amma daddy be kyauta min ba"


Suna cikin magana sai ga mummy ta shigo IMRAN na ganin ta ya dauke kan shi


Karasawa yayi tayi tace"kai ma fushin kake dani?ka tausayawa mummy ka,nayi nadama"


Kokarin tashi yayi mummy tace"son akwai ruwa jikin ka kuma jikin ka be gama karfi ba
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IMRANFAD
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


πŸ…Ώ9⃣1⃣&9⃣2⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Yi yayi kamar be jita ba,ya mike


Ummi tace"ina zuwa?"


Yace"gida zanje in nimo IMRANFAD"tari ya fara yi sai ga gudan jini,mummy na gani ta fara kuka


Cikin tashin hankali ummi tace"koma ka zauna baka gani kana amai jini"


Batare da yayi magana ba ya fita ya bar dakin


Daddy ne ya shigo da ledar magani yace"ina IMRAN yake"


Ummi tace"ya tafi kasan shi da zafin zuciya yanzu haka fushi yake da kowa"


Daddy yace"toh mu tafi gida tunda Wanda aka zo domin shi ya tafi"


Suna kaiwa gida suka tarar da shi zaune a falo yana kuka kamar yaro yana ganin kausar a hanun ummi ya taso da gudu ya anshe ta ya rungume yana kuka


Mummy ma kukan take yi,ummi tace"hajiya ya kamata ki bar kukan nan haka kin San ba ishashen lafiya ne dake ba"


Tace"dole in yi kuka dana saurari ya'ta da hakan bata faru ba gashi sanadiyar kunya da kawaici da kara na wargaza rayuwa ya'ya na"


Suna zaune sai ga zubys ta shigo gidan,ciki riga da wando jeans kan nan yasha attachment


Ai a fusace IMRAN ya mike ya shako wuyar ta da karfi


zare ido ta fara yi alamun tana jin jiki


Daddy ne ya karasa inda suke yace"sake ta"


Kin sakin ta yayi,daddy yace"ba da kai nike magana ba zakayi kisa ne?"


Muryar Abba suka ji yace"kyaleshi ya koya mata hankali


Duka IMRAN yayi wa zubys sanda ya tabbatar ya had'a mata jini da majina


Yace"zubys kin cuce ni, kin raba ni da matata ke je na sake ki saki uku dama bansan ya akayi na aure ki ba


Ihu zubys take yi domin ba karamin duka tasha ba,kasa tashi tayi


IMRAN ya kira salisu mai gadi ya zo ya dauke ta kamar kwadon shara ya worgar a waje


'Bangaren fadila kuwa ganin bata motsi yasa Dr sageer fara yi karanta mata ayatul kursiyu a ruwa Amina na shafa mata a jiki


A cikin kwana bakwai kacal da fara yi mata topi fadila ta farka sai dai tana abubuwa kamar me tabin hankali


Amina tace"yaya kamar ta samu matsala a kwakwalwa ko?"


Yace"hakan nike gani amma a bincike dana yi babu matsala,yau inshaallah zamu koma gida,ina kika bar kausar?"


Tace"tana wajen nanny"


Ai fadila najin sunan kausar ta fara dariya tana kiran sunan kausar


Amina tace"yaya na lura duk lokacin da aka kira sunan kausar sai ta yi wani abu"


Dr sageer yace"may be sunan yan uwata ne?gashi har yanzu ba samo su ba"


Mai gadi na barin fitar da zubys gida tayi, umma na gani ta tace"ya haka?"


Tace"wallahi ummi asirin ya karye shi yayi min wanan duka tare da saki na"


Umma tace"toh ina kudaden da muka tara?"


Muku muku zubys ta fara yi dan duk tj tabawa kudin kuma ya gudu shi taje nima har aka kawo malam bata nan


Umma tace"ina kudin dan ubanki?"


Tace"umma kiyi hakuri wanda nabawa ajiyar kudin ya bar gari"


Ihu umma tayi tace"zubaida kin cuce ni yanzu duk wahalan da muka sha bata sinana mana komai ba ki duba fa har kwanciya nayi da kazamin bokan nan shine kika bawa wani qato kudin ya cinye?"


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya babu labarin fadila,IMRAN ko ya rame yayi baki wasu lokota ma sai yayi ta abubuwa kamar zarare,kullum yana tare da kausar


Mummy ma kullum addu'a ta bai wuce Allah ya dawo da fadila yanzu kam basa wasa da addu'oi


Yanzu watan fadila 8 da bata kuma cikin ta yayi girma,ba laifi ta fara samun lafiya sai dai bata tuna gida ba


Dr sageer ko jin sonta yake har cikin jinin shi jira yake ta haihu a daura masu sure


Kuyi hakuri battery low


Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IMRANFAD
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interllingent,and expert writers,we are the best among the rest.


πŸ…Ώ9⃣3⃣&9⃣4⃣


Bismillahir Ramanir Rahim


Fadila ne zaune da amina suna hira


Amina tace"anty farida yaushe zamu shopping din kayar baby?"dan haka suke kiranta yanzu


Fadila tace"bari gobe muje"


Amina tace"anty kamar kina cikin damuwa"


Fadila tace"amina wallahi na rasa gane kaina,ki duba fa ko ran auren mu ban tuna ba,kuma zuciyata taki yarda Dr sageer ne mijina,domin ji nake kamar I don't belong here "


Amina tace"ki bari in kin gama samun lafiya yaya zai fad'a miki amma please kar ki guje shi wallahi yana sonki"


Tace"me zai sa in guje shi bayan shi mijina ne?ya zan guje uban ya'ya na?ni dai abin da ke d'aure min kai shine meyasa bamu kwana daki daya? "


Tace"ki bari zai amsa miki tambayoyin ki in lokaci yayi"


'Bangaren IMRAN kuwa yana cikin tashin hankali kullum cikin kuka tun kausar na gudu shi har ta fara yarda dashi kullum yana makale da ita yanzu ko tari yayi sai ya gan jini kuma yaki zuwa asibiti,ko aski bayayi duk wanda ya ganshi sai ya tausaya me,kuma ya daina kula mummy Dan fushi yake da ita sosai har da daddy


Mummy ko kullum cikin azumin da nafila,burin ta kawai Allah ya bayyana mata yar'ta,feena ma ta dawo wajen ta da zama dan yanzu ta gama school


Ummi ne zaune a falon ta sai ga IMRAN ya sauko rike da hanun kausar dan tun bayan rabuwa IMRAN da zubys suka tattara suka dawo kano tare da kulla zumunci mai karfi da anty rukkaya da mijinta Mahmud


Ummi tace"ina zuwa ne haka?"


Yace"zani cikin gari ne ko zan gan IMRANFAD"tausayi ya bata dan kullum sai ya fita niman ta,gashi ba inda ba a duba ba har yan sanda an bawa hoton ta amma ba labari


Cikin tausayawa tace"IMRAN ya kamata kayi aski ka daina yawo kamar mahaukaci"


Shiru yayi,suna cikin magana sai ga mummy tayi salama


Ummi ne ta amsa ,shiko yana ganin ta shigo yace" ummi sai na dawo kenan ko"


Ummi tace"toh Allah yasa a dace"


Mummy tace"IMRAN har yanzu baza ka yafe min ba?nima fa ya'tace"


Tafiya yayi ya barta tsaye,


Abba daddy ne tsaye a bakin matsalaci bayan sallah isha'i




Daddy yace"a gaskiya ya kamata ayi wa yaron nan aure ko zai rage damuwar nan abin nashi ya fara damuna"


Abba yace"aure kuma?"


Yace"eh gobe zan tara su na fad'a me matar da na zaba me"


Abba yace"toh Allah ya kaimu zan sanar da hajiya"


Bayan Abba ya koma gida ya sanar da ummi inda suka yi


Ai a fusace ummi tace"wallahi IMRAN ba zai Kara aure ba,bari alhajin ya zo,wallahi ko shakara goma fadila zatayi sai ya jirata"


Abba yace"nima haka na gani amma ban me musu ba kar ya dau ina nuna me iko ne saboda IMRAN d'ana ne"


Ummi tace"toh Allah ya kai mu gobe"sai masifa take tayi


'Bangaren zubys kuwa bayan ta koma gida da ummata ta fara sayar da kayan d'akin ta,dan komawa wajen boka wasa-wasa har suka sayar da gidan gado da mahaifin zubys ya bar musu,amma ba biyan bukata,yanzu ma babu kudin komawa wajen bokan,zubys ko ta kamu da cutar sanyi kullum cikin sosa gaba take ko gaban jama'a ga wani ruwa mai wari dake fita


Yau ma kamar kullum ta fito da mahaifiyarta bara bakin hanya sai ga wani arniyar morta ya parker,da gudu zubys taje,wa zara gani TJ da zee


Cikin mamaki tace"TJ dama kana gari me kakeyi da zee


Yace"zee kike nufi?ai matata ce"


Kallon zee tayi tace"zee ashe zaki iya cin amanata?"


Dariyar rain in hankali zee tayi tace"da kin dau ni wawiya ce da zan taimaka miki a banza?ai tun da na gan kin fara samun kudi na turo saurayi na tj ya yaudare ki"


Sadaka suka bata sanar suka bar gurin


Hanun suka zubys tasa a kai ta fara kuka kamar ranta zai fita


Misalin karfe 5' pm daddy ya tara kowa a falon Abba


Bayan yayi sallama ya fara da cewa"nasan zaku yi mamakin tara Ku da nayi a wanan lokacin,toh ba komai bane illa na yanke hukuncin aurawa IMRAN nafeesa nan da sati biyu"


Ai mikewa mummy tayi tace"babu Wanda IMRAN zai aura,bazan kara wanan kuskuren ba"


Ummi tace"nima ina bayanta"


Feena tace"gaskiya daddy bazan iya auren mijin fadila ba,kayi hakuri"


Zahra ko kuka takeyi,shiko IMRAN tari ya fara yi jini na fita sai yayi saurin gogewa,dafe kirjin shi yayi


Daddy yace"IMRAN umurni zan baka, zaka bi?"




Shiru yayi Abba yace"kayi magana mana"


Kawai sai ya fashe da kuka ya rike kafar daddy yace"daddy ka min rai ni bazan iya auren wata mace ba in ba IMRANFAD ba"


Mummy tace"bama zan bari ba tashi muje haka kawai yariya ta dawo ta ji an ma mijinta aure"


Jan hanun shi mummy tayi suka bar d'akin


Ummi tace"alhaji ka janye maganar auren nan dan ba yarda zamuyi ba"


Yace"ya na iya tunda kun hade min kai"


Ummi naso tayi magana wayarta tayi kara anty rukkaya ne


Bayan sun gaisa anty ruklaya tace"gobe zani cameroo ganin gida"


Ummi tace"toh Allah ya kaiki lafiya ki gaida mutanen gida,amma banji dadi da baki sanar dani da wuri ba ai Dana musu saraba


IMRAN ko zama suka yi da mummy suna kuka kamar yarda


Cikin kuka mummy tace"ka yafe min na tuba"


Goge mata hawaye yayi yace"na yafe miki mummy na"a haka daddy ya shigo ya same su yace"subhanallah miye haka?"




Cameroon






Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IMRANFAD
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interlingent,and expert writers we are the best among the rest.


πŸ…Ώ9⃣5⃣&9⃣6⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Cameroon


Da misalin karfe 12:pm anty rukkayya ta sauka garin Cameroon gida taje direct inda yan uwanta suka yi murnan ganin ta


Bayan ta huta da misalin karfe 5:pm na yamma tace"mami zanje nan store siyar man shafawa na manta nawa gida"


Mahaifiyarta tace"ki bari in Abbas ya dawo ya siyo miki"


Anty rukkaya tace"a'a mami bari in siyo da kaina ai ina naga gari"


Mami tace"toh amma ki dawo da wuri"


'Bangaren su fadila ko sun shiya zuwa super store siyan kaya,Dr sageer yace"hanya kuwa zaki iya zuwa naga da k'yar kike tafiya maman baby"


Tace"eh zan iya"kafin yayi magana wayar shi tayi kara yana d'agawa yace"IMRANFAD ya kake ne ya jikin"da sauri fadila ta rike kai bugun zuciyarta na karuwa


Amin tace"subhanaallah anty farida lafiya?"


Shiru fadila tayi,tana son tuna inda ta taba jin sunan,hotuna take gani a fuskar amma negative is not clear


Dr sageer ya karasa inda take yace"lafiya habibty?"


Kallonshi tayi tace"lafiya just headache "


Yace"sorry"


Mayar da wayar yayi kunni yace"hello"


IMRAN yace"dawa kake magana haka he?"


Dr sageer yace "da matata ce"


Zaro ido IMRAN yayi yace"mata yaushe kayi aure?"


Dr sageer yace "dogon labari ne, amma yanzu ma tana tsohon ciki haihuwa yau ko gobe ina fatan zaka zo suna?"


IMRAN yace"Allah ya kaimu,allah yasa kafin lokacin fad ta dawo"


Dr sageer yace"kana nufi har yanzu ba a samun labarin ta va?"


IMRAN yace"eh wallahi"sun yi hira kafi suyi sallama


Dr sageer na gama waya da IMRAN ya kalli fadila yace"habibty zaki iya zuwa ko mu tafi da Amina?"


Tace "zan iya"


Yace"toh tashi,muje"


Tashi tayi ta rike kausar amina tace"kausar zo in rike ki,ki bar mummy ta,huta"


Kin zuwa kausar tayi,fadila tace"barta kawai"


Suna isa store suka da fara dibar kaya wanda mafi yawanci na baby ne"


Anty rukkaya ne ta fito a taxi ta shiga store din ta fara duba kaya ta glass ta hango wata kamar fadila saurin juyawa tayi aiko sai suka yi ido hudu,dauke ido fadila tayi dan bata gane tana


Anty rukkaya ko tace"wanan ai fadila ce,amma ina ta samu ciki?"


Sauri take ta karasa inda take amma kafin ta kai tayi karo da wata mata kayar ta ya zube kasa sauri sungunawa tayi ta fara kwashewa da sauri har ta gama


Sai dai kafin ta dago su fadila sun bar wurin


Da gudu ta fita waje dai-dai nan motar su fadila ya tashi


Ihu ta fara yi tana kiran sunan fadila amma ina basu jita ba


Komawa tayi ta dauki abinda take so a store din ta bar gurin


Tana kaiwa gida ta kira ummi a waya tace"ummi wallahi naga fadila da tsohon ciki a Cameroon "


Zubur ummi ta mike tace"fadilata?"


Da sauri mutanen dake falon suka kalleta


IMRAN yace"ummi waye ne?"


Ummi tace"yanzu ina fadilal take?"


Anty rukkaya tace " ummi kafin nayi mata magana sun bar wajen"


Kwace wayar IMRAN yayi yace,,"a ina ne?"


Tace"a Cameroon "


Yace"gobe zan shigo Cameroon "


Tace"sai kazo"


Yana gama magana da anty rukkaya ya kira Dr sageer yace" hello Dr sageer"


Dr sageer yace"ya dai ?"


Yace"gobe zan shigo Cameroon ance anga FAD a Cameroon "


Dr sageer yace "sai kazo"


Yace "in na sauka a hotel zan kira ka"


Dr sageer yace"ga gidana miye na saukar hotel, kai dai sai ka zo"


IMRAN yace "toh nagode"


'Bangaren zee kuwa TJ na durka mata ciki ya kwashi ina shi ina shi ya bar gari tare da kwashe kudin account Ta's dan dama account daya suke using


A hanyar shi na barin gari yan fashi suka tare shi suka kwashi kudin tare da halbin shi a kafa sakamakon musu da ya so yayi musu




Zee ko gida ta koma amma sai baban ya koreta yace"shi babu ruwan shi da ita tunda ya hanata aure tj Dan iska amma taki sauraron shi"


Zubys ko bara sukeyi abinci da zasu ci ma gagarar su take kullum sai umma ta sine mata na bawa tj kudi da tayi,itama laifin umma take gani na sata bin bokaye




Washe gari da asuba IMRAN ya shirya zuwa Cameroon mummy taso binshi amma sai daddy ya hana


Misalin 4: pm ya saka a Cameron kasancewar bai samu ticket da wuri ba


A airport Dr sageer ya dauke shi,suna kaiwa gida Dr sageer ya bude me flat a waje yace"shiga ka huta inya so anjima Ku gaisa da madam tana ciki bata jin dadin jikinta"


Yace"alright,sageer na yarda FAD na kasan nan ji nake kamar tana kusa dani"


Dr sageer yace "Allah ya bayyana ta"


Shiga yayi yayi wanka ya kwanta yana tunani FAD mummy ko sai kiranshi take a waya ko akwai labari




Misalin karfe 6:pm ya shiga part din Dr sageer a falo ya same shi zaune yace"ina madam mu gaisa"




Dr sageer yace"wallahi tana ciki bata jin dadi,bari gobe sai Ku gaisa"


Yace"OK"


Fita suka yi cikin gari sai dube dube suke Dr sageer yace "ina hoton ta"


Yace"ai namanta shi gida"


Yace"toh mu koma gobe mu dawo "


Yace"OK"


Da misalin karfe 10:pm nakuda ya zo wa fadila ihu take ta na kuka


Da gudu amina take dakin Dr sageer ta sanar dashi ai rude ya tashi yaje ya kikimeta sai mota ko ta kan IMRAN be bi ba ya kaita asibiti


Dr Rabi ce a duty so ita ta amshi haihuwar


Ba karamin wahala fadila tasha ba amma har awa uku babu labarin haihuwa


IMRAN na barci yayi mafalki FAD na kuka tana niman taimako


Tashi yayi ya shiga bayi ya dauro alwala ya fara nafila


Cikin ikon Allah fadila ta haifo yan biyu mace da namiji amma tasha wuya sosai




Misalin karfe 8:am Dr Rabi ta sallame su




Da farin ciki Dr sageer ya kwankwasa kofan dakin IMRAN yace......




Maman
Noorul
Hudah✍✍
Luv u my fans
Pls share
πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„πŸ‘„
IMRANFAD
πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹πŸ’‹
By maman noorul
Hudah


🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟


🌟G.W.F.🌟


Home of gorgeous,interlingent,and expert writers we are the best among the rest




πŸ…Ώ9⃣7⃣&9⃣8⃣


Bismillahir Rahmanir Rahim


Yace"madam ta haihu yan biyu a boy and a girl"


IMRAN yace"wow congrat"


Bari in yi wanka yanzu zan shigo in gan baby's da mamar su


Dr sageer yace "toh muna jira amma pls ka aske wanan kasumba"


Dariya yayi yace'ni bana ra'ayin gayu yanzu"


Bayan yayi wanka ya shirya ya nufi babban flat din gidan yana zuwa ya gan Amina zaune da baby's a hanun ga kausar a gefenta


Yace"barka madam"


Dariya tayi tace"ba madam bane Amina ne,baka gane ni ba?"


Yace"amina ke kikayi girma haka?"


Dariya tayi,ta rufe ido


Dr sageer ne ya sauko yace"toh bashi babyn kana haka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login