Showing 1 words to 3000 words out of 60293 words

Chapter 1 - WATA BAKWAI BOOK COMPLETE by Lubna Sufyan.txt

19 Feb 2025

9154

 💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣1⃣


I dedicated this page to the jerk that broke my heart into thousands pieces and hand them to me on a plate.


Thank you for teaching me how to be strong and never give my scarred heart easily.


Shout out to the young writers out there.


Tunda abokansa suka rakoshi suka gama surutunsu da kawayen amarya bai ce uffan ba.


Asalima bazai iya maimaita magana daya da suka fada ba dan hankalinsa ba akansu yake ba.


Kallan yarinyar da take zaune kan gadon ya keyi baima san me zai soma fada mata ba.Ko kalar fuskarta bai sani ba tana zaune kan gadon lullube da mayafin da bashi da niyyar bude mata.


A hankali kaman mai koyon magana yace mata.


"Sannunki"


Tafi mintina biyar a zatansa ma bataji ba sannan cikin rawar murya tace masa.


"Nagode"


Hannunta tasa tana sake gyara mayafinta dai-dai lokacin da idanuwansa suka sauka kan hannayen nata da suka sha kunshi.


A gefe guda kuma zuciyarsa ta dauke shi ta watsa shi wani lokaci can baya.


*** ***


Da gudunta ta karaso inda yake.


"Yayana kaga kunshina yayi kyau?"


ta fadi da murmushi a fuskarta.


Shima murmushin yai mata yana fadin.


"Kai kai gaskiya baiyi kyau ba"


Fito masa da idanuwanta tayi lokaci daya ta tabare fuska tana shirin yin kuka.


Yana dariya yace.


"I am sorry. Just kidding, yayi kyau sosai. Waye yai maki?"


Juya bayanta tai alamar tayi fushi.


Rufe idanuwansa yai ya bude su a hankali in ba itaba bai fiye son yawan magana ba.


"kinga bara nai tafiyata since fushi kikeyi"


ya fadi yana mikewa. Riqo masa hannu tai sai da yaji wani abu har cikin kansa.


Bayaso tana rike masa jiki musamman in babu tsammani yaji hannayenta a jikinsa. Muryarsa can kasa yace.


"let go of my hand huddy"


Sake makalo shi tai. Saida yai mata tsawa sannan ta sake shi ta ruga kuma.


Yasan tabarar huddy kamar yunwar cikinsa. Kuka zatai kuma bashida zuciyar binta ya lallabata dan tana rikita masa kai da yawa.


*** ***


Idanuwansa da suke rufe ya bude. Hakan yasa zuciyarsa dakatar da inda ta dauke shi takaishi.


Sauke su yai kan yarinyar da take zaune kan tanqamemen gadon dakin.


Wani abu yaji ya soke masa zuciya. Jiyai sam bazai iya jurewa ba ya fice daga dakin yaja mata kofar a hankali.


*


Taji fitarsa. Kwantawa tai kan gadon ko kaya bata da kwarin tashi ta sake.


Kuka ne tayi shi har bata zatan tana da sauran hawayen da suka rage mata.


"Sannunki"


shine kalmar da tunaninsa ya bashi ya furta mata a darenta na farko a matsayin matarsa.


Wato kaddara dabance. Bata taba zatan auren wani bayan Ammar ba.


Fadar sunansa kawai a tunaninta yasa zuciyarta wani tafasa.


Ta gama tsanar mutumin nan tun kamin ma taganshi. Ya rabata da ammar dinta. Wai duk ma matan kano ya rasa wa zai aura sai ita.


Dan tsabar rashin adalci da rashin sanin darajar SO.


Kunshin hannunta ta kalla da bata ga amfaninsa ba can gefen zuciyarta ta tuno wani lokaci tayi kunshin jan lalle suna zaune da ammar.


*** ***


"Babyna ina son kunshi sosai. In munyi aure zaki dinga yimin"


ya fadi cikin karamar muryarsa da take so.


Murmushi tai a kunyace hadi da fadin.


"Saika biya tukunna"


Dariyarsa yai mata ya wani juya idanuwansa da yasan duk idan yayi yana burgeta sannan yace.


"Karki samu damuwa lokaci ne zaki fadamin ma.anar wannan maganar"


"Yaushe kenan?" Ta fadi muryarta da alamar dariya.


"uhm zakiyi bayani ne yarinya"


ya karasa shima da dariya a muryarsa.


*** ***


Wani radadi taji zuciyarta nayi tasan ta rasa Ammar da soyayyar nan tashi mai tsaya mata a rai.


Yanzun duk kulawar nan da alkawurransu sun tashi a banza? A wata daya kacal wani yazo ya ruguza masu soyayyar da sukai shekaru suna ginawa?


Ya tarwatsa musu farin cikinsu saboda sonkai irin nasa. Ta tsani koma waye wannan.


Kanta taji yana mata wani irin ciwo ga zuciyarta da take mata zafi.


Haka tai kwance shiru tana duk wata addu.a datazo bakinta ko zata samu saukin radadin da takeji.


A hankali bacci ya dauketa cike da mafarkin Ammar.


IF YOU HAVE ANY CORRECTION FEEL FREE.


08074545149.


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣2⃣


This is dedicated to those reading this page. Without you guys i won't be writing this.


Much love to you guys at ummie jafar novels group. Your encouragement inspired me and give me the spark to go for chapter two.


Allah's blessing.


Ya rasa kwanciya zaiyi ko zama ko kuma tsayuwa. A duk yanda yai zuciyarsa sam babu dadi.


Auren nan ya sake fama masa ciwukansa yasa suna zubda jini.


Da su umma sunsan bashida sauran zuciya mai numfashi ta bangaren soyayya balle kuma aure da basu matsa masa ba.


ko da yake harda laifin yarinyar da bata gaya musu bata son shi ba.


Shi kam yayi iya kokarinsa na kaucewa auren fin karfinsa akai. Itama yasan kwadayin abin duniya ne yasa ta nace ma aurensa.


A wata dayan da akasa na bikinsu. Kin zuwansa yaga kalar fuskarta kawai ya isa ya tabbatar mata da bai amincewa aurenta ba.


Amman saboda naci da kwadayi irin na matan yanzun saida ta bari aka daura masa ita. Inda huddy ta sha banban da sauran kenan.


Zuciyarsa ta fada masa. Dafe kai yai. Baya son wannan matsayin nasa da wanda yasan yana shirin samunsa a lokaci na gaba.


Yasan bakomai bane zai zabarma kansa amman ya dauka cewar atleast matar dazai spending rayuwarshi da ita shi zai zaba.


Bawai daukarta za.ai a lika masa bada son ransa ba. Gaba daya kansa yai masa nauyi. Neman wanda zai likama laifin abinda yake faruwa dashi yake kuma a yanzun babu wadda tafi dacewa irin yarinyar can dako sunanta ma bai sani ba.


Inma an taba fada a gabanshi bai rike ba dan bata ransa. Baya mata kallan komai sai yar katsalandan da kara masa matsaloli fiye da wanda zuciyarsa take ciki.


Gani yai sai juye juye yake yi ya kasa bacci. Ga ciwon kai na damunshi yama manta cewar tun abincin safe ne a cikinshi da ummansa ta takura masa ya zauna yadan ci. Bacci sam yaki yazo. Dan haka ya tashi ya shiga bandakin shi ya dauro alwala.


Hakanne kawai zai masa maganin wannan tunanin da ya addabe shi. Kuma yasan zai samu nutsuwa ko yaya take.


*


Bude idanuwanta husna tai. Kanta ya wani sara mata. Lokaci daya komai ya dawo mata.


Dacin da take ji a zuciyarta yana nan daram. Wayarta ta lalubo kan gadon, jikinta ya mata wani irin nauyi.


Bata san ta makara ba saida ta duba agogon wayarta taga karge bakwai saura mintina sha biyar.


"Lallai nasha bacci"


ta fadi a hankali.


Sai da kanta yadan saki sannan ta mike zaune. Taja tsaki. Wata kofa ta bude daga cikin bedroom din taga hanya ce.


Ta rufe ta nufi wata ta sake budewa taga dakin canza kayane. Ta juya idanuwanta. Ta sake bude wata taci karo da tankamemen toilet.


Duk haduwa irin ta gidansu da gidajen yan uwa da take zuwa bata taba ganin kayataccen ban daki irin wannan ba. Duk da tsanar gidan da maishi da tai yawa a zuciyarta bai hana ban dakin burgeta ba.


Wanka ta fara yi sannan tai alwala. Sai bayan ta idar da sallah sannan yunwar da takeji ta soma addabarta. Rabon cikinta da wani abu tun safiyar jiya.


Sai da ta gama shiryawa cikin wani less ruwan toka duk da ba wata kwalliya tayi ba kayan sun karbi jikinta.


Fridge din da yake can gefen dakin ta nufa ta bude cike yake da kayan alatu. Fresh milk ta dauka da apple dan ba ma.abociyar cin abu mai nauyi bace. Musamman da sassafe haka.


Bayan ta kammala ta dauki katan mayafi kalar kayanta ta lulluba sannan ta koma kan gadon ta zauna.


Ta kudurta a ranta koda wannan Nataccen zai shigo kaman yanda ta yanke shawarar kiransa dashi tunda ba sunansa ta sani ba. Kuma ba damuwa tai da hakan ba. Bata shirya ya kare ma halittarta kallo ba.


Auren kaddara ne ta riga ta runguma ko da da hannu dayane. Bata san iya lokacin data dauka ba kamin taji an kwankwasa kofar a hankali.


Gabanta taji ya fadi a sanyaye tace shigo. Zuciyarta na dokawa ga mamakinta wata mata ce mai matsakaicin shekaru ta turo kofar hadi da sallama. Amsawa husna tayi.


Har kasa matar ta tsugunna ta ce.


"Ina kwana. Fatan kin tashi lafiya"


Wani irin nauyin matar ya kama husna. Ko bata haifeta ba zatayi kanwa da ita. A kunyace ta amsa.


"Ranki ya dade ko kina bukatar wani abu?"


matar ta tambaya wadda har lokacin tana tsugunne. Cikin sanyin murya tace mata.


"A.a bana bukatar komai nagode. Ya sunanki?"


"Sunana asabe ranki ya dade. An shirya abinci ko da kina bukata nazo ingani. Dan lokacin tashin yarima daga bacci baiyi ba."


Sai da tai jim sannan tace.


"A.a nagode da kulawarki malama asabe. Kije kawai"


"Hutawarki lafiya ranki ya dade "


Asabe ta fadi tana mikewa ta fita daga dakin.


Husna ta yamutsa fuska alamar komai yai confusing dinta.


Wannan girmamawar da matar take mata yai yawa. Duk idan tace ranki ya dade din nan sai taji wani iri.


"Yarima"


Ta nanata tana tabe baki.


"Wa abbana ya auramin ni husna?"


tai tambayar da batasan mai bata amsarta ba. Zuciyarta tace mata.


"da kin maida hankali lokacin da ake miki bayani ai da kinsan kowaye."


Girgiza kanta kawai tayi. Tagaji da komai ma. Tagaji da tunani kan wannan auren tunda an riga an daurashi.


Takuma gaji da tambayoyin da babu mai bata amsarsu.


Hade kai da gwiwarta tai tana sauke wani dogon numfashi......




💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣3⃣



This page is dedicated to those that ever love and loose. Those that know the pain of getting your hopes high and getting them shattered.


Those guys that gets hurt from those they trust. Because that hurt like a bitch.


I hope time heals it for you guys.


I feel you!!!


Bai fito ba sai qarfe Goma na safe. Jikinsa sanye da shadda fara ya dora baqar alkyabba data sake taimakawa wajen bayyana kyawunsa.


Kai kawai yake dagawa duk hadiman gidan da suketa zubewa suna gaishe dashi.


Yau sarautar yake ji fiye da kullum magana ma wahala take masa.


Dining room ya shiga komai a shirye yake. Ya samu waje ya zauna.


Kaman yanda suka san tsarin cin abincinsa haka aka shirya masa komai.


Kadan yadan tattaba dan kawai kar ya zauna cikinsa babu komai.


Amman zuciyarsa bata da wadatacciyar natsuwar dazai ji dadin wani abinci.


Baibi takan natacciyar da aka kawo masa jiya ba dan hakan ya yanke hukuncin kiranta.


Ya yanke shawara da zuciyarsa babu ruwansa da ita.


Tunda bata gabanshi inta gaji zata gane hanyar gidansu da kanta danshi bashida wajen da zai mata a rayuwarsa.


Rigimar da yake ciki ma ta ishe shi ba saiya kara da tata ba.


Yana kammalawa ya miqe ya fita.


Bayan mota ya zauna driver dinsa ya tuqa shi zuwa gida.


Tun kamin ya fito daga motar hadimai ke tsugunnawa suna kwasar gaisuwa.


Wasu ya dan daga musu kai wasu kuma ya share abinsa.


Kai tsaye bangarensu ya nufa ya samu ummansa tana babban falo a zaune.


Har qasa ya tsugunna ya gaishe da ita ta amsa masa cike da fara.a ta dora da


"Babana har an fito kenan?"


Haka take fada masa kasancewar sunan mahaifinta da yaci.


"Nazo gaishe dake ne umma"


ya fadi yana murmushi duk da zuciyarsa babu dadi ganin mahaifiyarsa kawai ya bayyanar da murmushi a fuskarsa.


"Ya kwanan amarya?"


Ta buqata sai da yai jim sannan yace


"tana lafiya."


Ajiyar zuciya tai tace.


" babana saika yi haquri komai na rayuwa Allah ya riga ya gama tsarama bawansa. Ka zama mai rungumar qaddara. Kabawa auren nan lokaci sannu a hankali itama zata shiga zuciyarka."


Kawai shiga zuciyar data fada saida yaji ranshi ya sosu. In ya saka wata a zuciyarshi ita kuma huddy ya dauketa ya mayar da ita ina?


"Nagode umma"


ya furta yana ji zuciyarsa na wani tafasa.


ya za.aima wannan natacciyar ta shiga zuciyarsa bayan auren kwadayi tayi.


Ita kanta yasan badon kudinsa da matsayinsa ba babu yanda za.ai tai wautar auren wanda bata taba gani ba.


"Bara na qarasa mu gaisa da mai martaba"


ya fadi yana miqewa.


"Tam Allah yai maka albarka."


"Amin umma."


Fada cike take lokacin daya qarasa.


Fadawa na ta zuba masa kirari.


Gaisuwa ya miqa bai jima ba ya taso abinsa.


*


Yama rasa ina zaije shi ba ma.abocin yawo bane ba.


Babu wata hidima a gabanshi tunda an bashi sati biyu cewarsu ya gama amarci.


Duk idan ya tuna wani takaici kara kamashi yake.


Yai tunanin zuwa lambu sai dai wajen babu abinda zai qara masa illa rashin huddy.


Ashe akwai lokacin da rayuwa zatai masa haka?


Lokacin da zai rasa farin ciki. Lokacin da zaiyi murmushi iya fuskarsa bai kai zuciyaba.


Akwai lokutta da dama da akan bata mishi rai sosai. Amman huddy tana kwantar mishi da hankali.


A haka ya daure aka mai dashi gida.


A can qasan ransa yana fatan Allah yasa natacciya na bangarenta dan bai shirya haduwarsu yanzun ba.


Bai shirya ganin fuskarta ba. Baiki suyita zama haka ba. Dan ba karamar matsala za.a samu ba inhar tace zatai kokarin shiga rayuwarsa fiye da yanda tai masa yanzun.


Yako yi sa.a bata babban falo.


Yai maza ya wuce bangarensa ya kwanta.


Ta danna wayarta tayi game din harta gaji sam komai baya mata dadi.


Ta kunna kayan kallon da suke cikin dakin. Saidai duk wani channel da zata kalla taji dadinshi inta kai kewar ammar zata kara addabarta.


Wasu programs din ita ta koya masa kallonsu. Duk idan yai missing ko yana makaranta ko wata hidima yana dawowa saita bashi labari.


Haka idan ita tai missing zai bata labari. Wasu lokuttan kuma tare suke kallo.


Wasu hawaye masu dumi suka zubo mata. Tasa hannu ta tarbesu zuciyarta na mata wani nauyi.


Yanke hukuncin fita ta dan zagaya gidan tayi amman ta kasa.


Duniyar ta hadu ta mata kunci.


Wayarta taji tana ringing. Ta dauka ta duba.


Da hanzari ta daga wayar ganin kausar ce take kiranta.


Bata san lokacin da kuka ya
qwace mata ba.


"Ya salam"


kausar ta fadi tana dorawa da
"lafiya kuwa? Husna meke ya faru?"


Har lokacin kukan bai tsaya ba daqyar ta sami muryar ce mata


"kausar bana son mutumin nan bana kaunar wannan auren.
Ammar nake so shi na tsara rayuwata dashi."


Cikin rawar murya kausar tace


"calm down husna please nasani amman kaddara babu yanda bata zuwama bawa dan Allah kiyi hakuri karki kara jan matsala tsakaninki da iyayenki."


"Hmm kausar bakisan yanda zuciyata take yiba ne shisa inama mutuwa nai na huta"


ta karasa cikin kuka.


"Dan Allah ki nutsu zan sake kiranki anjima inkin dan samu natsuwa kinajina?"


Jin bata da niyyar amsawa yasa kausar kashe wayar.


Ita kam husna jefar da tata wayar tai can gefen gado ta kife kan gadan tana wani irin kuka mai tsuma zuciya.


Sai da tai mai isarta sannan ta tashi ta shiga toilet wanka ta sake yi.


Lokacin uku harda rabi dan haka tai alwalar la.asar. Tai mamakin saurin jan lokaci haka. Duk yaushe tai azahar kodan tana jin duk girman dakin ya mata kankanta ne shisa lokaci yake tausaya mata yana gudu?


Inama ace yanda lokacin nan yake gudu haka kaddararta ta wannan auren ta nisanceta.


Ta jima kan dadduma tana addu.o.i kamin ta miqe.


Asabe ta shigo ta sake mata maganar abinci yanke shawarar fita tai kodan taga yanayin gidan da zata kira na aurenta.


Gidan da duk lumfashin da zatai a ciki saita fito dashi da wani nauyi a zuciyarta.


Asabe ta rakata har qayataccen dining room din.


Chips kawai taci tadan sha fruits ta fito zuwa wani tanqamemen falo ta zauna kan kujera.


Daya bayan daya hadiman gidan sukaita zuwa suna gaishe da ita.


Bata qirga su ba amman tana yaqinin zasu kai su goma sha biyar.


Aljazeera take kallo tana ganin yanda duniyar taketa qarewa ko ina yaqi.


Ita kanta hatsaniyar ce take faruwa akanta. Saidai su yawancinsu mutuwa suke suna samun hutu da nutsuwa ta har abada.


Sabanin ita da take tunanin laifin datai take karbar horonsa da riba haka.


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Wata Bakwai 7


💝💝💝💝 💝💝💝💝


Written by


Luβπα Sufyαπ


0⃣4⃣


This goes to those architects that stay up all night designing and drawing.


I know how you guys work so hard

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login