Showing 123001 words to 123594 words out of 123594 words

Chapter 42 - ALKIBLA COMPLETE BOOK By Safiyya Abdullahi Huguma .txt

22 Feb 2025

11872

gayawa mahaifin xahran sanda yana raye)" bata iya daurewa hawayen daya cika mata idanu ba saida suka zubo
"No....yau ba ranar kuka bace,ranar farinciki ce,muma mun zama iyali,mun fara aje iri,kimin alfarma karki bata mana ranarmu" yakai qarshen xancan yana rungumeta cikin jikinsa ita da jaririn gaba
"Allah ya faranta maka yadda ka faranta min,ubangijin al'arshi ya kula maka da rayuwarka yadda ka kula da tawa,ya zama jinka ya zama ganinka,ya kuma zama garkuwarka" idanunsa a lumshe yana jin wani yanayin mai cike da sa'a da nasarar rayuwa,gami da katari da macen aure ta gari yana tsumashi
"Ameen mace ta gari"
"Au koke koken rashin son auren dole kuke ko kuwa?" Suka tsinci muryar hajja na shigowa,saiya saketa,suka daga kai suna dubanta,ta wani hade rai da gaske taqi dariya
"Me kuka wani tsareni da ido....zuwa nayi karbar takardar zahra'u,don naga alama idan na qyale wata shekarar za'a maimaita abinda ya faru yanzu"
"Kamar ko kin sani,don saita haife mai sunanki ma.....nida hubby kuwa mutu ka raba.....mutuwa ce kawai zata shiga tsakaninmu,inma zaki murmushi Allah gwara kiyi" ya fada ko ajikinsa dariya ta subuce hajjan,don itama farinciki da take ciki tasan bazata iya boyeshi ba,duk sai suka tayata darawa suna tuna rigima irin tata
"Komai zanyi inayinsa ne saboda rayuwarku,na godewa Allah da ya nuna min hadin kan ahalina gabanin mutuwata".






Haidar na murmushi yace
"Bamu da abinda zamu saka miki dashi hajjanmu sai fatan gamawa da duniya lafiya,kije ki tadda mijinki cikin aljanna madaukakiya kuci gaba da rayuwa"addu'an fatan alkhairi sosai ya dinga jera mata zahra na amsawa da amin,zuciyar hajjan fari qal kamar tasu ta fita tabar dakin,bayan ta tunawa zahran ta shirya ta fito haidar din ya kaita a sake tabbatar da lafiyarta,ta fita tana sake godewa Allah kan tarin baiwa da ni'imomi da yayi mata.




*_TAMMAT BI HAMDILLAH_*




_Kada ki sake,kada ki bari damuwar wani d'a namiji ta hanaki sukuni,kada ki bari damuwar wani saurayi daya yaudareki tasa ki tsaida taki rayuwar cak,bayan shi yana can yana tashi rayuwar_


_rabu dashi,manta dashi,nuna masa bashi da muhimmanci cikin rayuwarki,kamar yadda ya nunawa duniya hakan a kanki_


_kada ki manta,idan dubu sun qika....dubu ke sonka suke kuma jiranka_


_sau tari abinda kake so saiya zamana ba shine alkhairi a tattare dakai ba,abinda kake gudu kuma shine alkhairi a tare dakai ba tare daka sani ba_


_zama mai hankali ta hanyar zurfafa tunaninka,kada ka yarda ka yankewa wani dan adam hukunci ba tare daka mu'amalanceshi ba,kada ka yarda ya fadi halin wane bayan baka zauna dashi zama na gaske ba_


_koda yaushe ka zama mai kyautata zatonka ga mutane,sai gobenka tayi kyau_


_MAZA kuji tsoron Allah,nasan bazan aureki ba,to bazan soma tsayawa zuwa zance wajenki ba,kona bata lokaci kan layin waya ina qona miki kati ko ina qona nawa katin ba,ina bata miki lokaci,ina dauke hankalinki daga kula maza 'yan gaske masu niyyar aurenki ba,KADA KU MANTA KAI YAYA NE,WATARAN KUMA UBA NE!,ZAKA HAIFA KO A HAIFA MAKA!,AKWAI KUMA HISABI,ALLAH BAYA QYAKE HAQQIN WANI AKAN WANI TUN NAN GIDAN DUNIYA_




*_muna miqa saqon godiya da jinjina a gareku masoya kuma makaranta litattafan zafafa,wadanda a kullum basa gajiya da sanya kudadensu su siya rubutunmu,ubangiji yabar qauna_*




*_muna neman afuwan wanda muka batawa,ko wanda muka yiwa ba dai dai ba,ko labarinmu ya batawa,ko bai masa yadda yaso ya kasance ba,dukkanmu ajizai ne,duk inda ajizi yake kuwa saiya nuna ajizancinsa_*��




*_kurakuran dake cikin rubutunmu muna fata Allah ya yafe mana,ya bamu ladan dake ciki_*


*_ubangijin ya sadamu a rubutu na gaba,ya bamu aron rai da lafiya,yaci gaba da riqo da hannyenmu,ya kuma bamu damar rubuta abinda al'ummar annabi muhammadu zasu amfana dashi_*


*SUBHANAKALLAHUMMA WABI HAMDIKA,ASHHADU AN LA'ILAHA ILLA ANTA,ASTAGFIRUKA WA'A TUBU ILAIKA*��������

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login