Showing 96001 words to 99000 words out of 123594 words
Chapter 33 - ALKIBLA COMPLETE BOOK By Safiyya Abdullahi Huguma .txt
ta rasa meye abunda zatayi,tana tunanin ta koma idan yaso hajjan tayi kwadonta ta cinye,idan kuma ta zauna din kamar ta zubda kanta ne,zaiga ita ta kawo kanta ma kenan,kamar tadda yayi mata sharri a abuja.
Sake daga kai yayi ya dubeta,idanunta nacan wani sashen daban,don ta jima bata iya hada idanu dashi,tun lokacin da wancan abun ya faru,duk yadda yakai ga qwaqwqwafi da qwaqwar su hada idanun bata yarda
"Have a sit please.....bana son tsaiwa" ta jishin,saita samu waje tana zama din,cikin ranta tana mitar har a gayawa soja tsaiwa zaice wani baison tsaiwa,takaicinsa ya sake cikata,ta rasa me zata masa ta fanshe haushin da hajjan ke cusa mata a kanshi,don haka ta tsiri zuba mishi abinci,kowanne plate saita cikashi ta tura gabanshi,shi sam baisan ma me ake ba,harta gama zubawar,saita miqe ta nufi dan qaramin fridge dinsa dake dakin ta bude.
Jere yake da hadaddun zobo,wanda da alama jin zuwansa yasa umminta tayi masa,tunda dama itake masa,saboda din mutum ne da idan ba dole ba bai fiya son lemon kwali roba kona kwalba ba,yafi gabe gagajiya,zobo ginger ko kunun aya,su yafi sha indai yana gida.
Murmushin mugunta ta saki,babu abinda zai dace da tsarin ta irin zobon,ta ciroshi cikin wata kwalba me kyau da ummin ke aikawa can wani store ana siyo mata ita,tana yanayi da jug amma ba jug bane,dan tsukakken bakine da ita,sata hada da cup din data gani saman fridge din ta taka a hankali ta koma wajensa.
Sai data iso dab dashi ta soma tsiyaya zobon,taf ta cika kofi,sai kawai ta saki cup din ya sullube daga hannunta,ya kuwa fada saman cinyarsa,take ya masa wanka a fararen kayan dake jikinsa,ya kuma fantsame har screen na system din da yaketa faman latsawa.
Cikin ba zatar zubar abu mai sanyi daya ji a jikinsa ya daga kai yana dubanta,tana tsaye a kansa,saidai tayi narai narai da idanu alamun rashin gaskiya,baice mata komai ba sai qoqarin kashe system din da yake saboda karya shiga ciki.
Sai data fara shutting down sannan ta tsinci muryarsa
"Kin saba ai" tayi mamaki da taji iya abinda ya fada kenan,saboda ita da gaske fusatashi takeson yi,saidai batasan lamfo yayi mata ba,sai daya gama kashe system din,ya janye dukka takaddun da yaga zasu baci sannan ya miqe.
Idanu ta zura masa qirjinta na bugun uku uku sanda taga ya nufota,hannusa guda daya cikin aljihun wandonsa fari daya baci face face da zobo,wani taku yake slowly,saidai ya aza qwayar idanunsa cikin nata sosai,wanda hakan taji ya mata nauyi matuqa,ya kuma qara mata fargaba,duk da haka ta kasa dauke qafarta ta É—ara daga inda take tsayen harya cimmata.
Wata iriyar tsaiwa gab da juna sosai,har yatsun qafarsa na dungurin nata,har yanzu kallon qwayar idanunta yake data kasa janyewa daga cikin tasa,hannayensa ya daga sama gaba daya,kamar wanda yayi laifi aka kamashi yayi surrender
"Farashin da zaki biya wannan gangancin da kika yimin shine,ki cire kayan jikina ki daurayemin jikina da kika batamin haka kawai ina zaman zamana.....na yafe miki wankin kayan.....don yanzu dana saki ma waccar tsohuwar zata isheni da kwarorota da terere" kamar ya dauko guduma ya kwada mata haka taji,tsoro da firgici suka cikata,saboda daga yanayin yadda yake maganar ya tabbatar mata cewa da gaske yake bada wasa ba,ta kalli hagu da damarta,ko ina ya tare babu wajen kubuta,amma zata gwada,don kome zai mata ba zata iya abinda yace din ba,gwara ya mata duka da bulalarshi yafi mata sauqi.
"Am so sorry" ta samu kanta da furtawa cikin rawar murya,sake hade rai yayi tamau
"A soron gidanku nake kwana?" Yayi maganar yana dage mata dukka girarshi,saita kada kai
"Kayi haquri....banfa sani ba" kanshi ya kautar yana sake hade rai
"Sanda aka raba haquri bacci nakeyi" saita ware idanunta duka,wai dama ya haidar din ya iya magana haka,harda su baqar magana duka?
"To ka cire kayan....ka bani Allah xan wanke"
"Banaso,nima ina da hannu,and bakisan ni qazami bane....daqyar nake iya yin wanka?,kinga shine xaifi bani wahala ba wanki ba" sake zare ido tayi,tasan dai zaginta kawai yake,mutumin da idan heater din sassansa ta samu matsala kowa a gidan ya banu da dafa ruwan wanka.
Ta gama fahimtar bazai haqura ba dai din,don haka ta faki idanunsa,tayi wuff da niyyar guduwa,saidai taku uku kacal tayi taji an danqi hannunta
"Baki isa ba,ki batan jiki,ki batan kaya ki batamin guri kuma sannan ki gudu?,selfish girl".
Qafa ta soma bubbugawa tana tara qwalla ko zai tausaya mata,yadda dai takeqa hajja ta karya mata zuciya,saidai abinda bata sani ba,hakan da takeyi tsokano 'yan maza takeyi,saboda ko ina na jikinta dake rawa,idanunsa ya lumshe ya dora yatsansa saman labbansa bayan ya bude idon yace
"Shshshsh......ni banyi kuka ba saike?,zan baki another option.....koki wankemin jiki,ko na wanke da kaina,amma fa yadda kika jiqani kema saikin jiqe" da sauri ta gyada kanta,a tunaninta wannan shine zaifi mata sauqi,saboda tayi zato zaya dauko zobon ne ya kwara mata shikenan an wuce wajen,saidai ina,kafin takai ga wani tunanin sai ji tayi kawai ya dauketa gaba daya yayi bandaki da ita.
Cikin kwamin wankan daya cikashi da ruwan dumi ya jefata,wanda a niyyarsa dama idan ya gama cin abinci yayi wanka ya samu ya kwanta,tuni idanunta suka raina fata sanda ya salube hijabin jikinta,tuni rigarta ta lafe sosai a jikinta,ta bayyana duk wata halitta ta jikinta,gashin kanta da yasha ruwa shima yabi wuyanta ya kwanta,tuni ta dunqule waje daya,saboda ta fuskanci babu wata mafaka ko matsera.
Shi kuwa baya ya juya mata,haka kawai murmushin yadda tayin ya subuce masa,yakai geji,yana jin ya kamata ko yaya shima ya dana.
Batayi aune ba saijin mutum tayi tsulum cikin ruwan,da sauri ta daga kai don yin qorafi,amma suna hada idanu ta maida kanta qasa,qirjinta na wani irin bugawa,zuciyarta kamar xata fito,bata raina kanta ba sai daya dauketa gaba daya yayi mata masauki a qirjinsa,cikin hanzari ya ware hannayensa ya soma yawo dasu ko wane sashe na jikinsa,duk wani waje da yasan yana tsole masa idanu.
Cikin lokaci qanqani ta gigice,tana tuna abinda ya faru kwanaki uku ko hudu baya kada ya sake maimaita kansa,shikam ko a jikinsa,sai da yaga dama a qashin kansa sannan ya saurara.
Wankansa yayi har a sannan bata iya kallonshi ba,sai daya gama ya daura babban towel a qugunsa,saiya bude rariyar ruwan ya fita ya tara mata wani
"Zaki iya wanka" daga haka ya taka ya fice.
Tana qananun qwalla tana wankan,a haka harta kammala,sai kuma ta rasa me zata sanya ta fito?,idan ma ta fito din wanne kayan zata sanya tunda wanda tazo dasu sun jiqe?,towel ta hanga don haka dole shi ta daura,Allah yasa ya cire mata hijabin bai jiqe ba,saita saka shi ta fito daga toilet din a hankali kamar wadda ta yiwa sarki qarya kanta a qasa.
Waje daya ta samu ta zauna sanda ta fito din,yayin da yake gaban mudubi yana shafa mai,wani wasai yakejin ranshi da gangar jikinsa,wani shauqi da baisan daga ina ya taso ba yana ratsashi,itadai batasan me ake ciki ba sai taji sautin muryarsa yana cewa
"Hello hajja.....a samu yaro ya kawo mata kayan sawarta" shuru ya danyi da alama silleshi hajjan take,don murmusawa yayi kadan sannan yace
"Gani nan....zanzo na dauka da kaina" da haka ya kife wayar,ya qarasa shiryawa a gurguje ya fice,saita bishi da kallo tana dora hannu saman ka,shikenan ya janyo mata,ta shiga uku wajen hajja,tasan wallahi watan yi mata tijara ne ya kama,yanzu duk wanda yaga yaje dauka mata kaya saiya dauka wani abunne ya faru,kawai sai taji hawaye yana sauko mata.
Ya kusa minti goma sannan ya dawo,ya zube mata kayan wajen kala uku,abun kunyar ma data daga harda undies dinta da bra,ji tayi kaman qasa ta tsage mata ta shige,sauqinta daya ma daya dan fita ya bata waje ta shirya,bayan ya dawo yana daga zaune yasa tayi serving nasa,saita samu waje ta zauna bayan ta gama,lokaci lokaci yana satar kallonta,murmushi na subuce masa,can qasan ransa ya furta
"Silly girl,zanyi maganin wannan tsiwar taki" yana kallonta tayi kwanciyarta saman kujera,baice da ita komai ba,saida baccinta yayi nisa kawai ta tsinci kanta saman gadonshi,ta motsa yace da ita
"Kina tashi akwai punishment,just sleep" saita maida kanta ta kwantar tana irga qarfin hali da iya qarfa qarfa na ya haidar din,ita gaba daya kwance mata kai yakeyi,dukka halayen da take gani yanzu tattare dashi mugun baqin halaye ne da babu wanda ya zaceshi dasu
(Ni kuwa nace matar mutum ai ba wasa ba,duk wanda ke cika baki akan mace ba'a biyo ta kansa bane),ta qasan ido take hango duk motsinsa,saboda bayan yaci abincin aikinsa yaci gaba dayi,saidai wannan karon rubuce rubuce ne yaketa yi wanda batasan na meye ba.
A hankali qamshinsa daya kama zanin gadon da abun rufarsa ke ratsa qafofin hancinta,wani tattausan qamshi data kasa banbance na meye da meye,tun da can kusan lambarsa kenan,dashi ake gane yana waje,har zuwa yanzu kuwa duk wanda ya sanshi ya sanshi da qamshi,sannu sannu take shaqar iska zuwa hunhunta har wani bacci mai cike da nutsuwa yayi awon gaba da ita.
*_WASHEGARI_*
Tun bayan sallar asuba bacci ya sake daukarta me nauyi,ita da tayi niyyar zata gudu tunda duku duku,don ba zata iya hada idanu da jama'ar gidan ba,sai gashi bacci ya kwafsa mata,ba ita ta farka ba sai goma saura.
A rude ta sauka daga gadon,saita hau juye juye,babu kowa cikin dakin sai ita,don haka ta nufi qofa da hanzarinta tana addu'ar kar ya shigo har sai ta fice,don babu abinda taqi jini irin su hadu a yanzun,idan ta tuna abinda ya faru jiya ji take kamar qasa ta tsage mata ta shige.
Saidai ta makara,addu'arta bata ci ba,tana murda handle din shima yana murdawa,sai sukayi kacibus bakin qofa,yadda ya sako kai gaba daya yana tsareta da idanu ya sanyata ja baya ta bashi hanya ya shigo.
"Ina kwana" ta gaidashi tana kauda idanu,ya amsa mata da
"Kin tashi lafiya?" Saita kasa maida masa amsa,bai damu ba yace
"Muje....ciki nima zan shiga" da sauri tayi gaba,kamar wadda ake tsunkuli
"Easy mana" ya fada yana taddota,suka jera kafada shi da ita
"Ko sau daya mana,yau kawai hajja ta yaba mana" da xata iya juyawa zatayi ta maka masa harara,wanne yabon hajja ita takeso,bayan ta kaita ta barota,babu wani abu a jikinta a yanzu da baisan wajen zamansa da size dinsa ba,itakam ai sun gama da ita shida hajjan,bai sake cewa komai ba itama haka,haka suka ci gaba da takawa har zuwa cikin gidan.
Duk wanda suka gamu dashi sai taji kunya ta kamata kamar ta shige qarqashin qasa,musamman da sukaci karo da abba babba,cikin farinciki yake dubansu sanda suke gaidashi,harda yi musu addu'a sannan suka wuce.
"Muje ki fara gaida ummi" yace da ita yana tareta daga yin sassan hajja,saita bishi suka wuce sassan ummin tata.
Tana cikin yin breakfast suka shiga,saita ture kwanon,fuskarta itama cikeda jin dadin daya kasa boyuwa take amsa gaisuwarsu,haka taci gaba da binsu da kallo har suka fito daga sassan
"Kinsan girman ladan sanya farinciki a zuciyar iyaye?,muje ki gaida mama itama" ya fadi yana nuna mata hanya,bata ce masa uffan ba ta bishi suka isa sassan maman,ita dinma kamar sauran,farincikinta bai boyu ba,hatta da momy da suka gaisar,sai jikinta yayi sanyi,dukka wannan farincikin na meye?,na ganinsu ne tare da Aliyyun kawai?,da wannan tunanin suka wuce sassan mai gayya mai aiki hajja.
Dukkansu suna falo harda me jego,suwaiba da badi'a,saisu anty aliya da suka zo suyar nama,idanun da sukayo kansu gaba daya sai taji kamar zata zube a qasa,kunya kamar ta kasheta,saita dinga mammazewa,ta qarasa cikinsu ta gaidasu,hajja ce dai sai data tura mata qeya sannan ta amsa.
Bayan sun gaisa haidar din yadan zauna a cikinsu anty aliyan,abinda yakan jima baiyi ba kenan,ba kasafai suke samun damar zamansa cikinsu ayi hira sosai ba,sai lokaci lokaci,hakan ya sanya zahra barin falon ta shige dakin hajja,don nata dakin su suwaiba su shige ciki.
Tana nan kwance hajja ta shigo dakin yakai sau uku,a fakaice take mata habaici a waqe anaso ana kaiwa kasuwa,irin salon waqoqin mutan da din nan,dadai ta gaji da habaicin hajja saita miqe ta fice tabar mata dakin.
Har yanzu yana falon shida anty aliya da anty nusaiba,zata wuce kitchen ta samu abinda zataci taji suna masa godiya,da alama ya musu irin alkhairin daya saba ne.
Inna gaje ce kawai a kitchen din,sai tayi zamanta kawai a ciki,ta hada mata abincin ta soma ci suna hira,ita dinma zancan haidar din take mata
"Ai gaskiya uwar masu gida kin dace,kinyi dace da mijin qwarai mai hannun alkhairi,inda ace shidin wani hamshaqin attajiri ne Allah ne yasan mutum nawa me zasuyi kudi ta sanadinsa,ko a yanzun ma ya zama inuwa ga mutane da yawa,saidai addu'ar Allah ya qara arziqi" murmushi ta yiwa inna gajen kawai,ta can qasan ranta sai taji zuciyarta na amsawa da amin............
10/17/21, 10:25 PM - Jummi Hanya: 38
Wani mugun shewa taji sanda ta shiga dakin kwanansu,dama tun cikin aji ta fuskanci suna gulmarta da ido,don dai da malami a ajin,babu damar suyi mata magana ne.
Da ido ta bisu ganin yadda suketa mata dariya
"Dalla malamai,banason iskanci,meye abun dariya a jikina?,koni mahaukaciya ce?" Sai sannan hindatu tace
"Mahaukaciya tuburan kuwa......ah,ya haidar din da bashi da mutunci,ya zakin da babu ruwanki dashi,aka hanani neman soyayyar dan bawan Allahn nan,ash kinsan cewa qarshe ne shi a soyayya,ya gama haduwa tako ina,sai gashi ya kasheki da soyayya agun ajiyar motoci,har jama'a suka wuceku ma baki sani ba...nidai gaskiya qawa kinmin yankan baya ba kadan ba" ta fada tana hade fuska,janna tace
"Nifa banga laifinta ba,tsakani da Allah fa,waje zaiga guy irin wannan yana da dama ya bari ya wuceshi,wallahi ko nice sai inda maina ya qaremin,idan kuwa ina zaune yazo ya taya,ai babu wani kwane kwane zanyi wuff da abina".
Babi babi na tsiya suka bude suka dinga yi mata,ita dai ci kanku bata ce musu ba,hakanan ta samu kanta da kasa tanka musu,sai data tafi bandaki sannan suka saurara mata,data dawo kuma aka shiga hirar yaushe gamo,nan ma sai da suka tsokaneta
"Daga yanzu zanje na dawo qawa kuma sai mukaji dif" tsaki taja tana nade abun sallarta
"Wallahi hajja ce,ashe ta timer min" dariya duka suka saka,janna tace
"Allah dai ya biya hajja,wallahi ta kyauta min" harara ta jefa mata,hindatu ta cafke
"Ta taimakeki kuwa,don bakiga kyan da kika qara ba,Allah yasa anyi me gaba daya" ta fada suna tafawa,dadai ta fuskanci iskanci da tsiya suka tanadar mata buhu buhu,saita miqe tabar musu dakin,saidai zancan hindatu ya tuna mata da abinda ya faru a wancan ranar,ranar da yaso yayi mai gaba daya din,sai wani qaramin murmushi ya sube mata,ita kadai taja hijabinta zuwa qasan hancinta tana jin kunyar kanta da kanta.
Dawowarta ba jimawa aka soma jarrabawa,wanda daga ita din watanni kadan suka rage musu suyi jarabawar kammala makarantar,kamar kowanne lokaci dai bata daga qafa ba,ta bada himma wajen karatunta sosai,duk da cewa lokaci zuwa lokaci tunaninsa yakan fado mata a rai,har yakan tsaidata na wasu mintuna kafin ta dora,tun tana yaqin ture zuwan tunanin kwanyarta harta haqura ta bashi dama,saiya zame mata jiki,don kusan duk sanda tazo kwanciya bacci shine abu na qarshe da zatayi kafin baccin ya dauketa,kaf xamansu na abuja sai tayi bitarsa,ranar da zasuyi sallama na qarshe da sauran moments nasu.
Batasan me yasa a kwanakin take yawan duba wayarta ba,koda yaushe tana kan cheaking sms da watsapp massages fiye da yadda ta saba,batasan dalili ba,sai randa zuciyarta tayi mata wata tambaya,wanda a take ta girgiza kai alamar a'ah
"Kina tsammanin samun kira da gareshi ne?" Wannan itace tambayar data yiwa kanta,wanda ko sau daya bata taba yarda da hakan ba.
Jarabawar wannan karon suna samun intervals sosai,don haka duk sanda taga akwai interval mai yawa saita tafi gida,tafiya gidan yakan sa mata nutsuwa,kuma yakan sanya taji kamar tadan rage nisan dake tsakaninta da wani abu wanda ada yake nesa da ita.
Sannu a hankali ta tabbatarwa da kanta damuwa ce,damuwa ce ta rashin ganinsa ko rashin jin muryarsa na tsahon tagwayen sati,har ana neman shiga sati na uku,hatta a gida hajja ta fara qorafin shuru haidar,bai kira ba,koda an kira ba'a samunsa,to Allah yasa dai lafiya,addu'ar data sanya gaban zahran mugun faduwa,saboda tuna maganar daya gaya mata
_"zanyi tafiya me nisa.....waje me hadari,zan iya dawowa....zan iya salwanta a can.....ki yafemin idan na saba miki a tarayyarmu"_,kawai sai taji kuka ya subuce mata,ta danneshi har sai data kai daki sannan ta sakeshi.
Kuka tayi sosai wanda ta kasa yarda da dalilin kukan nata da zuciyarta keta bata,saidai ko ba komai ta danji nauyin dake qirjinta ya ragu,ranar sama sama tayi karatun jarrabawar da zata zana a jibi,washegari ta hada kayanta ta koma makaranta,wanda jarabawar kawaidai tasan saidai Allah ya tsallakar da ita,amma ita kanta bata gama tantance abinda take rubutawar haka yake ba,ko akwai kusakurai da gyararraki ba.
Hajja kuwa bin