Showing 69001 words to 72000 words out of 123594 words

Chapter 24 - ALKIBLA COMPLETE BOOK By Safiyya Abdullahi Huguma .txt

22 Feb 2025

11864

matar babban yaya....Allah dai ya biya,matar soja marmari daga nesa" harara ta watsa masa
"Kaga ya musty bama haka dakai,dadai ya shamsu ne nasan zaiyi abinda yafi haka,don Allah ja muje,ni hakan ma yafimin dai dai" ta fada tana yatsina,yayin da mustapha ya qyalqyale da dariya.




Ko kadan hakan bai bata haushi ba,saboda tasan cewa inda shine zai kaita babu komai cikin tafiyar face zallar takura har su isa,wala'alla ma sai yayi ko ya gaya mata abinda ranta zai baci a banza.




Sanda ta shiga dakinsu kamar hadin baki duka roommate din nata suna nan,har da sauran ma,ihu suka saka suna kiran ga amarya ga amarya,bata tanka su ba saima harara data watsa musu
"Duk ku iya bakinku wallahi" don har ga Allah har cikin zuciyarta tana jin sune sila,su suka jaza mata komai,saidai ko kadan basuji gargadin nata ba,saima ci gaba da zolayarta da suke,hindu tace
"Erhmmm....erhmmm...ashe ashe dai....yayan dai da aketa nunamin sam baida kirki.....ashe dai kece zaki wufffff da abinki akemin hannunka me sanda" kicin kicin zahra tayi da ranta sanda take aje jakankunanta saman katifarta
"Kinga hindatu....idan baso kike aji kanmu ba ki aje wannan maganar....am seriouse bana sonta" saida suka gama kidansu da rawarsu sannan suka qyaleta.




Zuwa washegari ta gama gyara komai nata,batayi qasa a gwiwa ba ta koma lactures cike da hazaqa karsashi da qwarin gwiwa,saidai haka nan ta samu kanta da takatsantsan da mu'amalarta da mazan ajinsu,duk da cewa dama can duk wanda ya sa ta yasan tana da wannan zarrar,amma a yanzun takatsantsan da kamewan ya qaru,tunda ada issue din karatu yakan hadasu,amma a yanzun mawuyacine idan ba ya zama dolen dole ba.
10/17/21, 10:25 PM - Jummi Hanya: 25


_*LAVENDER RESTAURANT..*_
_(Palace of mouthwatering food/delicacies)_


_IDAN KUKAJI GANGAMI DA LABARI, INA MASU SON INDA ZASU SAMU INGATACCEN ABINCI MAI DADI DA LAGWADA? KAI BA ANAN MUKA TSAYA BA, INA SABBIN AMARE? MAMAs, YAYYU? DA KANNEN MU MASU SON KOYAN GIRKUNAN YAN GAYU NA KASAR NIJERIYA DA KETARE?_


_*TO KU MATSO...! AT LAVENDER RESTAURANT GOTS YOU COVERED. ABINCIN KASASHE DA DAMA MUKE KOYARWA,,COME LETS UPGRADE YOUR FOOD TIME TABLE, MATSO KUSA YAR UWA GA DAMA DA ZAKI CANZA YANAYIN ABINCIN GIDAN KI, KOWA YASAN IYA SARRAFA ABINCI NA TAKA RAWAR GANI A GIDAJEN AURE. KAI KO BUDURWA CE INDE KIN IYA GIRKI ZAKIGA KOWA YANA HABA HABE DAKE..*_


_*UNCLES, DADDIES, BROTHERS., NEWLYWED HUBBYS..! KU ZO KU YIWA ‘YAYAN KU, MATAN KU DA KANNEN KU RAJISTAR WANNAN HARKA TA KOYAN GIRKI.*._


_*Lavender catering school zamuyi practical class. zamuyi 30 dishes continental,snack & desserts, traditional dishes, drink. Fee din 40k NE. phone number WhatsApp and call 09080299283 akwai discount na 5% ga mutum uku farko wadanda sukai register aranakun independence 1/10/2021 to 3/10/2021 Nigeria @ 61*_


_*ZA’A FARA CLASSES RANAR 14/10/2021. WATO SHA HUDU GA WATAN OKTOBAR DA MUKA SHIGA YAU*._


_*GIRKE GIRKE GUDA 30😫😨AKAN DUBU 40 KAWAI, HARDA BONUS NA SNACKS, DESSERTS, TRADITIONAL AND MODERN DRINK, GARGALIYA DA ZAMANI🥂WATA DAYA CHAS ZA’AYI ANA KOYAN GIRKE GIRKEN.*_


_*KU SAKE KARANTA WANNAN BONUS DIN👇�RIGIJI GABJI*_


_*Nigeria @ 61 _*
_*COOKING COMPETITION!!!*_

_*from lavender Catering ina masu son koyon girki ga dama zaku shiga gasarmu ta girki bayan kunyi register damu akan 10k,wanda yazo na 1zai shiga ajin mu free hade da wasu prize din na 2 da na 3 kuma zasu bayar da rabin kudine da wasu prize suma saura kuwa zasu ayi musu ragin 5% da wasu prize wannan gasa zamu yita ranar lahadi ne 3/10/21 zamu rufe registration na gasar ranar asabar*_


_*LAVENDER RESTAURANT: NA GARIN KANO, CLASSES DIN AKWAI PRACTICAL AND ONLINE CLASS GA WANDA KE NESA*_
_____________________________




Tsayawa tayi a tsakanin dakunan da falo tana kalle kalle,tare da tunanin me ya kamata tayi,tabbas kome hajja zatayi mata saidai tayi mata amma ba zata taba yarda ta shiga dakinsa da sunan kwana ba,sai kace wadda ake neman kai da ita?,ko kuma itace mijin shine matar?,sam bazai yiwu ba,saita qarasa ficewa,ta isa wajen tvn da dazun musty ya kashe ta kunna,ta koma kan kujera ta zauna tana rungume pillow gami da sauya tasha.




Kusan a qalla awa daya ta kwashe a zauna,gidan ya dauki shuru,sai tsoro ya fara cikata,don haka ta kashe tvn ta miqe a hankali ta nufi dakin nasu.




Sadaf sadaf ta tura qofar dakin,yan nan da duhunsa da alama kashe qwan hajja ta sakeyi bayan fitarta,saita kunna fitilar wayarta ta haska a hankali ta isa bayan hajjan tayi kwanciyarta nesa kadan da ita,ta tofa addu'o'in baccinta ta rufe idanunta tana addu'ar kada Allah ya farkar da hajjan.




Washegari tana kallon yadda hajjan ke maka mata harara,saita maze ta kuma dauke kai kamar batasan abinda ke faruwa ba,tasan idan tayi fushinta ta gaji dole ta sauko,shirye shiryen tafiya wajen gabatar da taron ma saiya janye hankalinta zahran ta sake samun sukuni.




Fitowarta daga wanka sukaji ana kada qaraurawar qofar falon
"Kai wannan abu sam babu hikima a ciki,wai wannan iblishiyar abar ke gaya maka kayi baqo....ke zahra'u...jeki ki duba kiga waye" hijabinta ta zura saman zanin jikinta ta fita falon.




Samuel yaron gidan ne tsaye bakin qofar,gefansa wata matashiya ce wadda a qalla zasuyi sa'anni da zahran,saidai xata iya baiwa zahran shekara uku tazarar shekaru uku kenan a tsakaninsu,fara ce sol,hakanan a kallo daya zaka fahimci 'yar gayu ce,asalin gayu kuwa,ganin farko xaka fadi halinta na yawan fara'a,donko a yaxun ma fuskarta a washe take da fara'a,har haqorin makan dake bakinta yana bayyana,tayi ado sosai da wani irin lace,takalmi da jaka masu aji gami da mayafi daya dace da shigarta,hannu da wuyanta duka kayan qawa ne na mata,da alama bata wasa da kwalliya
"Madam....matar abokin yallabai ce,yace ayi mata iso" samuel ya fada da gurbatattar hausarsa,saita saki fuska tana matsawa gefe gami da cewa
"Bismillah,ki shigo,su hajjan suna ciki"
"To na gode"ta ambata cikin fara'a tana shigowa,zahran tayi gaba tana biye da ita a baya
"Bismillah....zauna,bari nayi musu magana" ta fada tana nuna mata wajen zama,cikin fara'a ta soma zama tana cewa
"Ok to....amma ba kece amaryar oga haidar ba?" Rasa amsar da zata bata tayi,bai kyautu tayi mata qarya ba tunda batasan matsayinta da kuma zancan da sukayi ba,sa'annan kuma hannu guda bata son amsa sunan matarsa sam,saita gyada kai cikin murmushi
"Eh"
"Ma sha Allah....hala kai ya dauki chargy bai gaya miki zuwa na ba....nazo ne zamu wuce tare daku can wajen taron,tare da yallabai zamu tafi,so kuma an kirasu babu damar su dawo gida su shirya din mu wuce tare,sai yace kawai nazo mu wuce tare daku....ni matar abokinsa ce kuma abokin aikinsa da za'a qara musu girma tare,sunana dr nasreen" dole ta dawo ta zauna cikin fara'a,tunda da alama su din basusan komai kan aurenta da haidar ba,bai kamata kuma ta nuna komai din ba
"Ni sunana zahra.....ya gida ya yara" murmushi ta sakeyi
"Gida lafiya lau,yara kuma tukunna"itama sai tayi murmushi
"To Allah ya kawo masu albarka"
"Amin summa amin na gode" dole ta miqe ta nufi kitchen da kanta,abinda bata gwada ba ko sau daya tunda sukazo gidan.




Tayi mamakin ganin kitchen din,ya hada komai da komai na buqatar girki,ta bude fridge ta debo ruwa da lemo ta hado da tea da aka dafa tun dazun a flask da sauran farfesun kayan ciki ta aje mata,sannan ta wuce ciki kiransu hajja.




Ta fito da kayan akwatinta duka tana duba wadanda zata saka,ranta a bace kawai yake,banda zuwan nasreen da kuma idanun hajja itafa babu inda zata je.




Hayaniya ta fara ji daga falon ta dadu,da kuma muryoyi kamar na 'yan gidansu,kafin tace wani abu hayaniyar taji ta doso dakin da take,hafsat ce kan gaba dauke da babynta,sai salma a bayanta itama da nata baby boy din da tuni ya soma tafiya sai yusra daga qarshe.




Rungume juna sukayi cike da murna,sosai taji dadin zuwansun,abinda yaso sasu su bata ma tsokanarta da suka fara yi,Allah ya yanke abun ta hanyar shigowar nasreen,wadda hajja tace taje wajensu sai tafi jin dadin zama.




Hira suka shiga yi inda ita kuma ta hau shiryawa cikin wani lace army green da yayi masifar haduwa,dinkin riga da skert daya zauna mata sosai a jiki,tana shiryawa tana sauraren hirar tasu,da alama itama dr nasreen 'yar hira ce,hakanan bata da wahalar sabo,don kuwa idan ka ganta a lokacin saika tsammaci ta dade da saninsu,cikin qanqanin lokaci suka saba da ita.




Tana gama shiryawa dukka suka rude da zolayarta kan irin kyan data yi,haushi ya cikata ta kasa magana,bugu da qari kuma ma da idanun nasreen dake wajen,wadda ke zaune gefe tana ta murmushi tana kallonsu,yanayin zamantakewarsu da hadin kansu,yadda suke haba haba da juna,da alama akwai saboda shaquwa mai qarfi a tsakaninsu.




Motoci uku masu tsananin kyau da tsari ne suka debesu daga gidan aliyyu haidar zuwa inda za'a gabatar da taron a babbar headquater sojoji dake garin abuja.




Tun daga waje xaka fahimta lallai babban taro ake,abu nasu maganin a kwabesu,ko ina jami'aine dake bawa wajen tsaro da kariya,tako ina komai na tafiya kan tsari,duk abun mutun idan yaga tsari da yanayin wajen sai yaji sun masa kwarjini,lallai soja ba wasa bane,dole ya haidar ya dinga yi mana kwarjini tanaji su salma suna fadin hakan,ita dai nata idanu ba tare da tace komai ba.




Babban wajene budadde wanda aka tanada saboda taro irin wannan,kujeru ne bisa tsari,wajen baqi da manyan baqi daban,wajen zaman sojojin dama wadanda za'a qarawa girma daban.




Suzo akan lokaci ne,hakan ya sanya suka samu waje mai kyau da zasu iya hangen dukkan yadda abubuwan zasu wakana,wanda hafsat ce ta haura ta hango musu ta jasu wajen suka zauna
"Da kyau hafsat,gaskiya kin iya zaben wajen xama,xanga dear da kyau wallahi" cewa dr nasreen tana gyara zaman hand bag dinta tare da gyara zamanta da kyau,wanda zamansu babu wuya wajen ya soma cika da jama'a,aka kuma fara gabatar da 'yan wasu abubuwan kafin a shiga muhimmin taron.




*_BAYAN SHUDEWAR WASU MINTUNA_*




Mai gabatarwa ne ya amsa abun magana ya tabbatar da wajen ya hau tsari bisa doka da yadda suke gabatar da tarukansu,take wajen ya dauki saiti,kowa ya bada hankalinsa kan abubuwan da aka soma gabatarwa.




An yiwa manyan baqi maraba da zuwa,sai parade na musamman ada aka shirya saboda su,sai da aka fara gudanar da parade din sannan zahra tadan dago daga danna wayar da takeyi ta dubi wajen.




Sai abun ya dauki hankalinta fiye da yadda ta zata,don wannan shine karo na farko da aka fara parade a gabanta,a nutse take binsu da ido,yadda suke komai a nutse sannan kuma a tare,duk wanda yake wajen sai abun ya bashi sha'awa ya kuma qawatar dashi,musamman idan shi din ba ahalin abun bane.




Suna kammalawa wadanda zasu karbi qarin girman suka soma shigowa da daya da daya,kusan inda ta zauna din yana kallon inda aka tanadar musu domin zama,sannan kuma daura da wajen qofa ce,hakan ya bata damar ganin duk wanda zai shigo din.




Mutum na shida ne ya shigo
"Oh god dear.....yau ka canza sosai" taji de nasreen na fada cikin wani irin exciting,tadan kalleta kadan sanda take daga yatsunta,saita maida hankalinta ga wanda ke shigowar,ga mamakinta ya hangi matar tasa,shima kuma yatsunsa yake daga mata a fakaice,sai taji ta aika masa da kisses ya kuma dawo mata da amsa sanda yake samun waje yana zama fuskarsa dauke da wani irin murmushi.




Murmushi tayi itama wanda ya tsaya iya cikin zuciyarta,ko ba'a fada mata ba tasan cewa dr nasreen da mijin nata narkakkun masoya ne,idanu kawai sun isa baka amsa,tana shirin dauke idanun nata daga wajen ta hangi shigowarsa,wanda shigowar tasa tayi dai dai da sakin wani take daya dauki hankalin jama'ar dake wajen.




Taso qaryata idanunta da suka nuna mata yadda shigar kakin dake jikinsa ta amsheshi fiye da duk wani wanda yake sanye da kaki dake wajen,hakanan taso qaryata kanta data hangi zallar kwarjini dake kwance saman daurarriyar fuskarsa da ayau tadan sassauta daga yadda aka santa zuwa matakin daurewa na qasa qasa,batasan kaki na yiwa mutum kyau ba sai a lokacin,saidai ta alaqanta hakan da cewa rashin taba ganinsa cikin shigar da bata taba yiba yasa dukka taga hakan,saita janye qwayar idanunta sanda shi kuma nashi idanun ya sauka a kanta ba tare daya shiryama hakan ba,ya lura da dr nasreen daketa aikawa lieutenant jafar kallo wanda a yanzu xai koma matsayin captain,saiya lumshe idanunsa gami da yin bismillah ya zauna a mazauninsa.




Yanayin yadda taron ke gudana kawai ya isa ya sanyawa mutum nutsuwa da sha'awar ganin dukkan abinda ake gudanarwa a wajen,hakan ya sanya ta jefa wayarta a jaka,ta tattara dukka hankalinta a kan abinda ke wakana.




Hakanan lokaci zuwa lokaci idanunta na sauka a kanshi,kusan tunda ta sanshi bata taba ganin fuskarsa a sake haka ba,duk da ba dariya ko murmushi yake ba,tana jin su salma na gulmarsa,itadai batace komai ba,ganin haka hafsat ta tabo ta
"Wai yau bakiga fuskar sojanki ta saki ba?" Harara ta watsa mata tana dauke idanunta,daidai sanda suka hada idanu,saiya dauke kansa gami da sake daure fuskarsa,yadan juya kadan yana yiwa lieutenant jafar magana qasa qasa.




Bayan gama gabatar da komai,abu na kusa da qarshe daya rage shine saka musu igiyoyi da stars daga commanders dinsu,hakan yasa wajen ya sake nutsuwa kowa ya sanya idanu yaga nashi wanda yazo dominsa.




Daki daki aka dinga bi ana saka musu alamun qarin girmansu,cike da ban sha'awa karramawa da kuma girmamawa kan yadda suka sadaukarwa da qasarsu rai da lafiyarsu.




Aliyyu mas'ud dabo shine mutum na biyar bisa layi,general hamza shine zai saka mishi nashi,ya matso kusa da haidar din,saidai tsahonsa bazai iya kaiwa ba ga haidar din ba,cikin barkwanci yayi maganar a nemo masa abunda zai taka wanda hakan ya baiwa mutane dariya,murmusawa aliyyun yayi ya duqa dai dai yadda hannun general zaikai ya saka masan sannan akaci gaba.




Duka sai da aka gama sanya musu da sauran jawabe jawabe,sannan akayi sanarwa ta musamman akwai mutum biyar a cikinsu da za'a karrama da wasu lambobi masu siffar kwabo da za'a rataya musu,saboda sadaukantaka gaskiya riqon amana da kuma qwazon aiki,bayan wajen ya nutsu aka fara kiran sunayensu,mutum na farko ya isa wajen,saiya nema alfarmar iyalinshi ce zata sanya masa,duk da cewa shekarunsa sun kusa arba'in da wani abu hakan ya burge mutane,cikin nutsuwa ta taso ta rataya masa sannan ta tsaya aka musu hoto ta wuce,hakan ya sanya aka maida rataya abun wuyan ga iyalan sauran,marasa matan aure a ciki kuma mahaifi ko mahaifiya,abun saiya dinga bada qawa da burgewa,saboda kowacce mata in a romantic way take sanyawa mijinta,tana jin yusra na cewa
"Gaskiya ne,ban sake yarda soja akwaishi da son matarshi ba sai yau....jiba don Allah abun sha'awa,sun sadaukar da farincikinsu ga qasarsu...ma sha Allah,Allah ya dafawa sojojinmu".




Lieutenant jafar wanda a yanzu ya koma captain jafar aka kira,dr nasreen ta damqi hannun zahra cikin farinciki ba tare dama ta sani ba
"Ma sha Allah my happiness....lallai yau ranarmu ce" ta fada tana duban zahra,itama zahra dubanta tayi,tana mamaki cikin ranta wannan wacce irin soyayya ce?wadda bata boyuwa,saita sakarwa dr nasreen murmushi kawai na qarfafa gwiwa,ta gyada kai
"Thanks" ta cewa zahra tana miqewa a nutse ta sauka daga wajen zuwa inda yake tsaye yana jiranta.




Kafin ta qaraso tuni ya miqa mata hannunshi,tana murmushi itama ta isa ta dora hannunta cikin nashi,kamar sun manta da tarin jama'ar dake wajen,ta amsa abun wuyan,tadan rusuna kana ta miqe ta zira masa fuskokinsu dauke da murmushi ta juya tana maqale a kafadarsa aka musu nasu hoton,tana jin salma na fadin
"Wow....matar nan ta hadu wlh"




Sam zahra bata damu ba bata kuma kawo komai ba,don bata tsammaci zuwan sunan Aliyyu ba,sannan tunda daga mama har abba babba na wajen,sun kuma fita cancanta,saidai me?,cikin sakanni sunan aliyyu dabo ya karade abun maganar,wanda kamar qiftawa da bismillah duk sojan daya kasance junior dinsa dake wajen saida suka miqe,sukayi salute nashi sanda yake takowa zuwa inda kowa yake tsaiwa cikin nuna zallar girmamawa,da alama akwai akwai alaqa mai matuqar kyau a tsakaninsu
"Ma sha Allah" 'yan uwa dake kusa taji suna furtawa,lumshe idanunta tayi tana duban wajen yadda suke tsaye,abun ya qayatar da duk wanda yake wajen
"Get up mrs aliyyu dabo" dr nasreen ta soma fadawa zahra cikin fara'a,yayin da dukka su salma suka waiwayo suka sanya mata ido,kai ta kadawa dr nasreen
"Mama tana nan....haka abba ma"
"Tashi kije inna wuro" ta jiyo muryar mama,wanda sam bata zaci taji ba,saita miqe a hankali tana jin wani nauyi na saukar mata,qafafunta sukayi sanyi kamar ba zata iya tafiya ba,wanda wannan ya qarawa tafiyar tata zama slow,hakan saiya qarawa yanayin takun nata ado,da wani salo na daban mai qayatarwa.




Tunda ta taho ya zuba mata idanu da wani salon kallo,wanda ba lallai kowa ya fahimta ba,saif dake tsaye daga gefansa ya soma masa magana qasa qasa
"Smiling please....,just once" banza yayi dashi,saidai idanunsa yana kanta sanda take ci gaba da takowa,taqi kallon koda saitin inda yake,saidai tana sauraren salma dake bayanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login