Showing 21001 words to 24000 words out of 123594 words

Chapter 8 - ALKIBLA COMPLETE BOOK By Safiyya Abdullahi Huguma .txt

22 Feb 2025

11841

"Har yanzu uwata batason makarantar nan hajja" nannauyar ajiyar zuciya hajja ta saki sannan tace
"Damuwar data shiga na jin cewa Aliyyu ne zai maidata.....yafi damuwar komawarta makarantar yawa.....bansan wanne irin nau'in rashin jituwa bane tsakanin inna wuro da haidar ba" shima ajiyar zuciyar ya saki a boye yadda ba zata jishi ba,sam basu son abinda zai taba ran tsohuwar ko ya bata ranta sam sam,don haka cikin salon son kwantar da hankali yace da ita
"Quruciya ce ke dawainiya da dukkaninsu,wataran zai zama labari" dan qaramin murmushi ta saki tana kada kai
"Haba muhammadu.....idan kace innawuro quruciya ce na yarda shi kuma haidar fa?"
"Sai muyi addu'ar samun jituwa tsakaninsu ai hajja" kai ta gyada
"Hakane....don babu abinda ya gagari addu'a"
"Wannan haka yake" ya fada yana janyo ledar daya bawa xahra ta shigo masa da ita.




Washegari qarfe shida na safe ta gama shirinta gaba daya,saidai tana ta faman kumburi saboda wanda zai kaita,qarfe bakwai tana falon hajja tana karyawa da kayan karin da hajjan ta tashi da wuri ta hada mata don kada ta tafi da yunwa.




Shamsuddeen ne yayi sallama falon hannunsa riqe da maqullin mota
"Baki gama shiryawa bane?" Ya tambaya bayan ya gama gaida hajja
"Kai zaka kaini?" Ta tambayeshi itama
"Eh....ya haidar yace na kaiki" baki ta tabe,ita hakanma yayi mata dadi,don haka ta qarasa abinda bata qarasa din ba cikin hanzari,tayi sallama da duk wanda ya dace sannan suka wuce.




Komawarta makaranta duk data koma da tabon nuraddeen cikin zuciyarta amma hakan bata bari yayi mata tasiri ko ya hanata karatu ba,ta tattara hankalinta kacokam kan karatunta,musamman da suke shirye shiryen fara zana jarabawar qualifying,duk da cewa batason makarantar amma shima bata bari ya hanata karatu ba.




Wata iriyar baiwa da basirar karatu Allah ya bata,tana da qwaqwalwa sosai,wanda hakan yasanya tayi tasiri sosai a zuciyar malamai da kuma daliban makarantar ma gaba daya.




Sannu a hankali lokaci ya dinga juyawa yana tafiya da wani sauri da kuma hanzari,wanda yakan fauci abubuwa masu muhimmanci a rayuwar bayi yayi awon gaba dasu,wasu tare da saninmu wasunsu kuma ba tare da saninmu ba.




'Yan kwanaki ya rage musu su fara zana jarabawar suka samu baquncin sabbin malamai da aka sauyasu da wasu malaman dake koyar dasu wasu darussan,ciki kuwa harda malamin da zai dinga koya musu yaren turanci wato english,saidai su dinma na wucin gadi ne,sunzo ne sakamakon horaswa ta musamman da wadancan malaman suka samu damar zuwa suyi na wasu watanni.




*_ALƘIBLARSU_*






Malam nasir,matashin saurayi,ma'abocin iya ado gayu da kuma jan aji,uwa una qwarewa da gogewa wajen iya yaren turanci,wanda tun farkon zuwansa shine abu na farko daya soma jan hankali dalibai mata da dama dake cikin makarantar a kansa,yadda yake da gwalli ya hade da qwarewarsa wajen iya turanci,sai hakan ya zame masa tamkar ado,yana da jan hankali da kuma daukar hankalin kamar mace,da dama daga cikin 'yammatan makarantar yana burgesu,yayin da shi kuma izzar sa tasa bai duban kowacce mace cikin makarantar,har zuwa ranar da Allah ya qaddara haduwarsa da zahra,shigarsa a jinsu na farko,a lokacin da suka fara extra lesson saboda jarabawar dake gabansu.




A ranar ta tashi da ciwon mara,wanda a baya ita sam bata sanshi ba,bata taba yi bama sai a lokacin,haka ta dinga daurewa saboda nacinta da karatun,da kuma burin samun sakamako mai kyau,duk da cewa hasina tace da ita ta zauna,bata da matsala tunda ita zata je amma ga qiya.




Zuwanta ajin saita kasa hasala komai,hakanan ta kifa kanta saman table din da take kai tana jin yadda mararta ke zugi.




Tana iya jiyo sautin sallamar malamin,tashinsu da gaidashi da sukayi,yadda ajin yayi dif sanda yake zagaya daliban,ya tsaya gefan table dinta yana tambayar wacece wannan?,bata jin zata iya dagowa bare ta amsa mishi,tana jin sanda hasina dake gefanta ke masa bayani
"Allah ya sawwaqe" ya fada yana barin wajen bayan ya basu umarnin zama,sannan ya isa gaban allo ya fara aiwatar da abinda ya tarasu.




Rabi da rabi takejin komai,har zuwa sanda jin da zaman saman teburin ya gagareta,ta fara nishi saboda ciwo,wanda ya fara jan hankalin hasina kafin kuma sauran daliban zuwa malamin su ankara,shi ya bada umarnin hasina da wata hasana jibril su dagata su kaita a bata magani,sai a sannan da suka dagata yaga fuskarta,ya kauda kai bayan sun fice yaci gaba da yiwa sauran daliban karatu.




Kwananta uku kafin ta samu sauqi,ranar da zata koma shiga lesson din,da yammacin ranar suna shirin tafiya,ta fuskanci yadda daliban kowa keta qoqarin hada wani assigment wanda batasan na meye ba,saita dubi hasina dake zaune gefan gadonta riqe da nata assigent din tana sake dubawa
"Wai aikin me aka baku,naga kowa hankalinsa a tashe?" Rufe littafin tayi tana murmushi,ta daga kai ta dubi zahra
"Wallahi malamin nan zahra ya hadu tako ina,mugun kaine dashi,da alama yana ja sosai,ga gayu ga iya koyarwa" baki zahra ta tabe tana saka hijabinta
"Nifa ba wannan na tambayeki ba hasina" murmushi ta sakeyi
"Ko baki tambayeni ba ai dole na gaya miki,aikin daya bamu yace zamu iya cin karo dashi a jarabawarmu,zai gani ya zamuyi dashi idan mukaci karo da tambaya makamanciyarta,shine ya bamu yace mu gwada,bari ki gani" bude mata tambayar tayi tana mata bayani iya yanda ta fahimta tsahon wasu mintuna,murmushi zahra tayi bayan ta gama bayanin,saita koma ta zauna,ta jawo jakar litattafanta ta ciro littafi da biro,dai dai sanda hasina ta miqe
"Mu wuce zahra,naga an fara tafiya"
"Jeki kawai zan taho" ido ta fidda
"Kai...wallahi ya hana,yace kowa ya tabbatar yana rigashi shigowa"
"Kije yanzu zan qaraso"
"Idan ya hanaki shiga ke kika jawa kanki,nidai nayi gaba" ta fada tana qarasawa cikin wadanda basu kai ga tafiya ba suka rankaya suka fice tare.




Da sallama ta shiga ajin wanda ya cika da dalibai,malamin dake gaban dan tebur da kujerar zama ta malamai,saidai shi yana tsaye ne bai zauna ba ya waiwayo yana amsawa,dubanta yake ganin tana qoqarin shigowa,fuskarsa a hade yace
"Dakata....ina zaki?,ban hanaku zuwa a irin wannan lokacin ba?"
"Malam kayi haquri.....saida na tsaya nasha magani ne"
"Baki da lafiya?" Ya tambayeta yana dubanta,kanta a qasa ta gyadashi
"Eh,yau kwana uku ban taba samun lesson dinka ba,sai yau na samu sauqi" a sannan ya gane itace,ya tuna fuskarta,don haka yace
"Allah ya qara afuwa.....wuce"
"Na gode sir" ta fada cikin farinciki sannan ta wuce zuwa mazauninta.




Karatu suka ci gaba dayi,ta bada dukkanin attention dinta ga malamin,shi dinma ya fuskanci hakan,don haka saiya zamana karatun kamar da ita yakeyi,saboda kusan dabi'ar malami ce,bada hankalinsa ga dalibin daya fuskanci yana fahimtarsa yadda ya kamata.




Eh tabbas hasina batayi qarya ba,ya iya karatu ya iya koyarwa kamar yadda tace,hakanan taji dadin karatun na yau sosai,ta kuma qaru sosai.




Sai daya gama ya fara amsar aikin daya basu din,da kansan yake bin teburin kowacce daliba ya amsa littafin,ya tsaya a wajen ya duba sannan yayi mata marking ya wuce na gaba har ya qaraso nata teburin,ganin zai wuceta saboda tsammanin batayi aikin ba yasa tayi saurin miqa masa nata littafin,sai daya kalleta sannan ya amsa littafin,ya dawo da baya zuwa wajen mazauninta ya bude ya fara dubawa.




Lokaci lokaci yana daga kai daga littafin ya dubeta harya gama karantawa,saiya rufe littafin kawai ya riqeshi a hannunsa ya wuce teburi na gaba,hakanan taji babu dadi,ko bata rubuta dai dai bane?,tasan iya bakin qoqari tayi wajen ganin tayi assigment din daidai duk da bata zo ba a sannan,mutum ce ita da bata bari assigment sam ya wuceta,saboda tasan hanya ce ta sake samun wani sabon ilimi ga dalibi,hasina dake gefanta qasa qasa tace
"Hala baki rubuta dai dai bane?" Kafada ta daga cikin damuwa
"Ban sani ba nima,ina jin dai hakane" daga haka suka bar maganar harya gama duba na kowacce daliba ya koma gaban allo ya tsaya.




"Fatima sa'id dabo" ya fada yana karanta sunan daga jikin bangon littafin nata
"Yes sir" ta fada tana miqewa,ya kalleta sosai sannan ya mata umarni ta fito gaban aji.




Littafin ya bata yace ta karanta abinda ta rubuta ta kuma yiwa 'yan aji explanation,cikin sanyi jiki ta karba,tana nauyin kada ace shirme tayi,hakanan ta baiwa kanta qwarin gwiwa ta soma karantawa tanayin bayanin kamar yadda ya umarceta,yayin da shi kuma yaja gefe daya ya tsaya jingine da bango yana qare mata kallo,yanajin tana wani birgeshi haka kawai.




"Sauran qarin bayani ga wanda bai gane ba kuma....saiya tambayi sir" ta gama bayanin nata da fadin haka,kana ta maida idanunta kansa,sai suka hada idanu,janye idanunta tayi sanda yake sakar mata murmushi ya tako a hankali ya soma tafa mata yana fadin
"Very good fatima.....every body clap for her" take ajin ya rude da tafi,saida suka tsagaita sannan yace
"Wannan shine karatunmu nayau gaba daya fatima ta gamashi,assigment dinta koni iya abinda zan rubuta kenan,ta dace da class captain....kuma itace headgirl dinku da zarar kun shiga ss 3" da wannan bayanin nasa aka tashi daga aji ranar.




Tun daga lokacin sai ya zamana ya ganeta sosai fiye da zatonta,yakan kama sunanta sau tari idan suna karatu,hakanan itama takanyi tambaya har kan abinda bashi suke karantawa bama saboda qaruwarta,hakan yasa sabo yadan soma shiga tsakaninsu,hakan yasa ta soma samun abokan adawa daga ajinsu dama ajin sama dasu wato 'yan ss 3,wadanda keda muradin nasir din.




Randa wata mardiyya taso takalarta da fada akan sir nasir din abun mamaki ya bata da dariya,don itadai tasan babu komai tsakaninsu daya wuce alaqar malami da dalibi,saitaqi biye mata,ta dinga dariya kan abinda ta fada din,saidai kafin sukai ga rubuta jarrabawa su tafi gida hutu tuni ya bayyanar mata da soyayyarshi.




Da farko tayi dari dari da abun,saboda wasu dalilai da suka hada da dokar makaranta,tsoron abinda ya faru tsakaninta da nuraddeen da kuma sa'idon dalibai,amma daga baya data zauna tayi nazari,ta fuskanci dukka halaye da dabi'un malam nasir din masu kyau ne,sannan ita kanta bawai bata sonshi ba kamar yadda ba zata ce wai tana sonshi kai tsaye ba,amma a qalla a yanzu suna gab da shiga ss 3,wanda ba zasu wuce wata 9 ba zasuyi candy,kuma kafin suyi candy dinne kowacce wanda zata aura zai gabatar da kanshi da magabantansa asan dashi,suna gama makaranta kuma sai maganar aure,tana ga mafi kyau shine ta bashi dama su fukanci juna,ba lallai abinda ya farun ya kuma maimaita kanshi,da wannan tunanin ta soma dan bashi dama kadan,duk da ta gaya masa abu mafi kyau ya bari suyi hutu ta koma gida tukunna,shima hakan ya masa,saboda haka bai zura jiki da yawa ba,ya bari har zuwa sanda suka gama jarabawar suka koma gida sannan ya fara kafa kanshi a zuciyar zahra din.




Cikin wani lokaci taqaitacce ya samawa kansa wajen zama,saboda mutum ne daya qware wajen iya tsara lafazi da iya jan hankali,uwa uba kuma iya ado,yana da faran faran,sa'annan da kansa ga buqaci ya gaisa da hajja tukunna kafin su abba,ta bashi dama suka gaisa,sai gashi cikin lokaci kadan kamar sun dade da hajjan,saboda ita dinma tana da son jama'a da saurin sabo.




Abinda yasa ta kuma sakewa dashi shine,akwai sanayya tsakaninsa da salim dan abban gwammaja yayan umminta,bai kuma fadi wani aibu ko mummunan hali tattare dashi ba,hakan yasa ta sake jin cewa ta samu abokin rayuwa kamar sauran 'yan uwanta......


_to masu karatu.....ya zata kaya?,muje zuwa,mu hadu gobe da izinin ubangiji_������
10/17/21, 10:25 PM - Jummi Hanya: 09
*OUM DUFAIL!!*
_GIDAN ADO ƘAWA DA KECE RAINI_💄💅�


_OUM DUFAIL ta tanadar muku dukkan nau'in kayayyakin gyaran fata gashi dama jiki gaba daya ZAHIRINKI DA BAÆŠININKI samfurin MAIDA TSOHUWA YARINYA_


*kayayyakinmu sune kamar haka*



FACE AND BODY SCRUB=2500(300ml)
Face and body mango butter=3k (250ml)
Face cream= 1800
Corretor oil/vitamin C oil=2k
Fairness skin lotion= 2500
Hot chocolate skin lotion 2500
Serum (for Nuckles )2k
Nuckles cream (stubborn)3500
Mix fruits Arabian black =soap 1800
Mix fruit glycerine soap =1900
Beetroot=1900
Coconut, milk,egg..face soap=1200
Lavender mix fruit soap =1800
Body wash =1500
cleanser=1600
Hair spray =700
Hair oil =1500
Hair relaxer =700
Hair butter 1700
Shampoo =1500
Breast=oil 2k powder 2k
Strech marks cream= 2k
Beetroot pink lips =700
Baby care soap glycerine=1k
Baby care butter =1500
Shea butter baby soap =700
Tsumin tula =2200
Tsumin zinariya =1200
Sliming tea =1500
Amarya set =25k
Liquid Arabian black soap =1900
Cleansing water =1500




*Ku dubamu a handle namu na Facebook da Instagram*
Ummu Dufail


*ko ta number wayarmu kamar haka*


07067943479


*_muna turawa kowacce jaha dake fadin nigeria da yardar Allah_*


*_INGANCI DA RAHUSA SHINE TAKENMU_*������
_____________________________




*_BAYAN SATI BIYU_*






Karfe goma na safe ta kammala duk wani aiki da xata yiwa hajja,kasancewar idan tana nan ita da baba gaje suke mata duk wani aiki,koda taje da niyyar yiwa umminta wani abu takance ta bari taje ta yiwa hajjan,ita ilham zatayi mata wato qanwarta.




Tana gaban madubi tana shafa ma take tunanin zuwa gidan abban gwammaja wajen hasina,amma kuma daxun sir nasir yace mata zaya zo ganinta,tana mamakin yadda baya gajiya da jinta ko ganinta,har kunya yakan bata wani lokaci,ta samu tattali da kulawa wadda ta dara ta nuraddeen,sai a yanzu take ganin ma nuraddeen kamar shidin ba komai bane bai iya komai ba akan nasir din,ita kadai wani lokaci idan ta tunashi da kulawarsa gareta takan saki murmushi.




Cikin doguwar rigar swiss atampha cotton ta shirya mai yarfin stone a jiki,tana tsaka da fesa turare bayan ta taje gashinta ta daure wanda takeson hasina ta mata kitso taji hajja na qwala mata kira,saita aje turaren ta dauki dankwalinta a hannu ta fito.




Ita da abban tsakiya ne,sai haidar dake kallon labarai a VOA,yadda sojoji suka samu nasara a jahar borno cikin satin kan yaqi da 'yan ta'addan boko haram yana kuma magana da abban tsakiyan.




Da sauri ta ware dankwalinta ta daura tana qarasawa inda suke,Allah yasa bai ganta ba,shida abban ta gaida sannan ta maida hankalinta ga hajja dake mata bayanin
"Hadowa Aliyyu abincin kari maza da sauri....." Daga haka ta waiwaya tana mita
"Ku hakannan kuke bakuson cin abinci musamman da safe,koda yaushe sai an tilasta muku kuke ganewa....tafiya daga nan har dawakin kudu amma ciki babu komai,haka zaka tuqa iyayen naka kaje ka kasa qarasa tuqin saboda yunwa......tsabar zumudin zakayi sabon aure?" Kansa ya shafa yana cewa
"Kamar ba namiji ba?,karki.manta soja nake hajja.....nakan iya kwana uku banci ba wani lokacin sama da haka ma idan wani aikin ya taso mana".




Baki zahran ta tabe tana shigewa kitchen,cikin ranta tana fadin
"Ni ki qyaleshi kawai hajja ya tafin haka....yanzu da wahala yaci abincin nan baice wani abu ba akai sarkin qaqale" haka nan ta hada musu abincin daidai yadda zai ishesu shida abban tsakiya,ta isa falon ta dire musu tayi komawarta daki.




Bata sake fitowa ba sai da taji alamun fitarsu sannan ta fito riqe da mayafinta,sai data shiga kitchen ta hada kayan nata karin sannan ta dawo falon ta zauna kusa da hajja,tana tsaka da cin abincin hajjan tace
"Ina tunanin kafin ku koma makaranta fa iyayenku zasu nemi ganawa da magabatan samarinku,saboda yayanku ya tada maganar aurensa,yanzu haka can suka nufa garinsu yarinyar" duban hajjan tayi tana cin abincinta
"Shi zai kaisu da kanshi kenan?"
"Eh" ta bata amsa tana dauko remote don ta canza tasha,saita tabe baki
"Ey...da yake shi idanunsa da kwalli ai ba laifi bane,inda kaine da ka shiga uku" duka hajjan ta kai mata ta kuma sameta,ta gantsare tana cewa
"Wayyo Allah na.....hajja saikin karyani tukunna?"
"Eh gwara ai na karya ki din....tunda ke baki gajiya da dan banzan qorafi,zancan da ake miki daban wanda kike daban"
"Shikenan tunda haka kika ce,kullum nice me laifi" daga haka ta miqe da farantin a hannunta ta wuce kitchen tana zumbura baki,ta ajjiye sannan ta fito ta yafa mayafinta
"Zan wuce hajja" tayi maganar da alamun jin haushi har yanzu akan fuskarta,kudi hajjan ta miqa mata tana gaya mata kada tayi dare.




Kamar yadda hajjan tace kuwa a ranar akaje dawakin tofa dangin mahaifiyar Aliyyu haidar ko ince zaki aka tambaya masa aurenta hannun iyayenta da suke kawunnai a wajensa,mahaifinta qanine ga mahaifiyarsa,ba tare da wani bata lokaci ba aka basu auren,tunda shima kamar d'a ne a wajensu,suka dawo cike da farinciki da murnar yadda akayi komai cikin girma da karamci.




Washegari abba babba ya bada sanarwar kowacce cikinsu ta yiwa maneminta magana,indai da gaske yake yazo ya gabatar da kanshi tare da magabatansa,don suna so nan da shekara daya su hada su duka a aurar,mata biyar namiji daya.




Ba bata lokaci ta shaidawa sir nasir,wanda ya bayyana murnarsa sosai fiye da zatonta,don har mamaki ta dinga yi yadda yaketa farinciki,kusan ma kamar ya fita so da daukin abun,ya kuma tabbatar mata idan basu zama na farko ko na biyu a zuwa ba.....to ba zasu zama na uku ba.




Saurayin salma shi ya fara zuwa rana daya dana yusra,bayan kwana biyu saurayin yasira da magabatansu sukazo,washegari na hafsat ya bayyana shima,a ranar ne zahra ta karbo wayarta daga gyara,wadda ta matsu qwarai ta gyara din,don tafi kyautata zaton rashin wayar ne ya hana zuwan sir nasir kamar yadda yayi alqawari,tana jonawa a chargy ta lalubo number dinsa ta kira.




Bugu daya ya dauka,sai daya saki ajiyar zuciya sannan yace
"Kin wahalar dani fa"
"Me

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login