Showing 54001 words to 57000 words out of 110071 words

Chapter 19 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

1908

zama tayi kafin ta amsa masa "a'a ni sana'ata gyaran jiki. Idan ka tashi aure ka kawo min matarka nayi alkawarin yi mata kyauta"

Dagowa yayi sosai yace "alkawari fa, Allah Ya kaimu ko wace amaryar kice tun yanzu nasan an 'yanta ni daga kudin gyaran jiki."

Dadi kawai take ji ganinsa da magana dashi a haka. Itama tunanin tasa sauyawar take yi. Ya zama dan gayu sosai banda kamshin turarensa da ya cika falon shigarsa ma kawai ta isa ta sanya mace ta soshi.

Tayi nisa a tunani taji ya kada mata yatsunsa har sun bada sauti tayi saurin dauke kanta daga gareshi.

Shi kuwa yace "irin wannan kallon sai kisa nayi tunanin promotion na samu, har na fara murna."

Kunya taji ta jawo mayafinta ta sake rufe fuska. Shi kuwa sai dariya yace "Allah kuwa haka kawai aje a sa min rai ina dalili. Yanzu dai fara bani labarin da nake kwadayin ji"

Kasa dago kai tayi maganarsa tasa mata jin nauyinsa "labarina kayan kuka ne da bakinciki kawai a ciki"

"Assha Kanwarmu a rinka godewa Allah dubi yadda rayuwa ta koma miki fa. Ni dai ina son ji. Idan anzo wurin kuka muyi tare idan na bakinciki ne mu rarrashi juna. So nake wannan gap din shekaru na tsakaninmu mu cike shi ta hanyar sanar da juna komai. Kada ki manta na roki alfarmar zama dan uwa abokin sirrinki ne"

Ji tayi bazata iya yi masa musu ba ta soma bashi labarin tun daga shigarsu kotu na farko har zuwa yanzu. Tayi kuka sosai kafin ta gama. Dahiru kuma jijiyoyin kansa suka dago saboda bacin rai.

"Kiyi hakuri Mawadda ban so haka ta faru dake bama tare ba" yace murya na rawa saboda yadda yake ji.

Dago kanta tayi wanda ta kifa akan cinyarta ta turo baki "ni ban yarda ba yanzu kace idan abin kuka yazo tare zamuyi"

Yasan wasa take so ta sako domin sassauta musu yanayin da suka shiga sai ya biye mata.
"Kada kiso jin kukana don muryata sai ta cika gidan nan ga rashin dadin sauraro"

"Ni kam tana min dadi" tace ba tare da ta kawo komai a ranta ba. Kallon da yayi mata ne yasa ta rufe baki sai kuma tace saura nashi labarin.

Tun farkon zuwansa Kano ya soma fada mata har yau da yaje gidansu Qareeba.

Sai ga Mawadda tana dariya kamar ba ita ta gama kuka ba.
"Yanzu Yayanmu mace tace tana sonka shine kake ja mata aji. Huhmm gaskiya ka koma kace ka amince kawai don ni tayi min"

Dahiru yasha kunu da gaske baya son zancen Qareeba.
"Ita ce nace miki tana kirana Ahirin ko Dashiru da farkon labarin ko baki gane ba?"

Ta kuma dariya "Ahirin na Qareeba yaushe zamu sha biki?"

Kula yayi zolayarsa kawai take yi shiyasa ya dena biye mata. Sun cigaba da tattauna abubuwa da dama yace "amma likitan da taci amanarku a kotu baku sake binciken dalilinta ba?"

"Barta ta yiwa kanta ne. Kasan ranar Baba ya fadi muka taho asibiti shiyasa komai ya dakata"

Dahiru yace "naji dadi kinyi karatu yanzu Kanwarmu. Kinsan babban abinda ake cutarmu dashi bayan talauci shine rashin ilimi. Akwai abubuwa da dama da yakamata ace an kula dasu wancan lokacin. Kamar sanar da lauyan binciken farko na asibitin Bebeji, kawo wadancan 'yan sandan shaida da sauransu. Duk da haka kada ki damu hakkin da suka dauka bazai barsu ba"

Hawaye ne ya zubo mata tace "Yayanmu bazan taba yafe musu ba. Akwai ranar da abin ya ciyoni fa na kwana dashi a raina kawai sai gani a Kaduna"

Idanu ya zaro "me???"

Da sauri ta shiga girgiza hannunta tana kallon kofa "shhhhh babu wanda ya taba sani"

Yace "to wallahi fada min yadda abin ya faru ko na tona"

Wata harara ta doka masa wadda ta shiga ransa don yadda ta kada idanun ma burgeshi yayi "naji amma wallahi amanatul amana..."

"To ya isa kada ki karasa bazan fada ba bare ta cini." Ya yamutsa fuska "kai Kanwarmu ashe baki girma ba har yanzu wai amanatul amana"

"Rigakafi nake yi don kada ka janyo min duka"

Shekara biyu kenan lokacin tana ganiyar mafarkin BB tun da barayi suka shiga makotansu akace sun kusa yiwa matar gidan fyade. Shikenan abu ya dawo mata sabo tana kwanciya take farkawa a firgice. Ranar da abin ya isheta zuciya ta raya mata wai taje Kaduna ta hadasu da 'yan sanda a koma kotu. Karyar makaranta tayi sai gata a tasha kamar wasa. Taje Kaduna ta fadi sunan unguwar amma ta kasa gane ko ina. Tana cikin yawon tambaya kamar wata mahaukaciya Baba ya kirata yace ta taho masa da maganinsa na hawan jini a lamco pharmacy. Sai lokacin ta dawo hayyacinta a gaggauce ta koma tasha. Ranar sai bayan magariba ta dawo gida ta zuga musu karyar dalilin rashin dawowa da wuri. Babu wanda ya tuhumeta tunda ansan ba yawo take ba.

Dahiru na jin labarin ya sake tausaya mata da sabon kuduri a ransa na tunanin dole ma ya aureta ya nuna mata soyayyar da zata gusar mata da tunanin wannan azzalumin mutumin.
******

BB ne ya fito daga dakin Alh Sule yana ta gunaguni don me zai ce masa sai yayi aski. Kunyar yanayin shigarsa yasa sun kasa tura shi ya gaishe da 'yan uwa ma.

Yana saukowa Yasmin ta fito daga kitchen da food flask ta yiwa yaranta girki. Haj Mara tace masu aikinta bazasu yi girki da ita ba. A nata bangaren hakan yafi mata don yadda ta kula ta sawa yaran nan ido ba abin mamaki bane ta nemi hallaka su. Anyi sa'a damuwarta gabadaya tana ga BB yanzu.

Yasmin ya hango ya taho inda take kusa da dinning table ko kula Haj Mara baiyi ba da take tambayarsa yaya sukayi da Alhaji.

"Matar Alhaji wai yaya kanen nawa suke kiranki ne ba dadi ina cewa matar Alhaji dinnan."

Yasmin tayi murmushi ganin Haj Mara ta bata rai "Mama suke kirana"

"To ai nima kawai sai nabi ayari. Ni dasu ai same to same ne...so ba wani abu kingane ai" yace yana yin gaba.

Ita kuwa kai ta gyada kawai. Bayan ya wuce Haj Mara ta tashi zata bi bayansa taji Yasmin tace "ta inda aka hau ta nan ake sauka"

Dawowa tayi ta tsaya a gabanta "me ki ke nufi"

"Nayi miki magana ne?"

Rai a bace dama neman wurin huce takaici take ta cakumi wuyan Yasmin din.
"Ki bar ganin na kyaleki idan na dawo gareki bazaki ji dadi ba. Kina tunanin kin shigo min gida ne don ki kwace komai nawa?"

Bude baki tayi zata rama taji Alh Sule ya fito sai ta soma kuka tana bawa Haj Mara hakuri. Harda cewa idan saboda zuwansu ne zasu koma Abuja nan ba da dadewa ba.

Alh Sule yana saukowa ya kamata da fada sosai da ja mata kunne babu ruwanta da iyalinsa.

Mamaki ne ya hanata magana kawai ta bi bayan BB tana hawayen zuci.
*****

Kwana biyu da zuwan Dahiru tun ranar Qareeba ta dena walwala a gidan. Dr Tani ta sami maigidanta tace lokaci yayi da zasu nema mata lafiya a ajiye boko a gefe.

"Neman lafiya wane iri?" Yace yana kallonta.

"Daddy na tabbatar Qareeba aljanu gareta irin masu hana auren nan. Idan ba haka ba wane dalili zaisa ta kai har yanzu babu aure babu mijin auren a hannu"

Bayan gajeren nazari ya amince da bukatarta don shima ya gaji da gorin 'yan uwa. Abokansa ma wasu sukan yi masa maganar tun yana bada amsa har yayi shiru.

Maigadinsu suka sanarwa saboda ustazu ne. Washegari sai gashi da malami aka zo aka rinka yi mata karatu harda hayaki. Malamin gudun kada ace baiyi komai ba ya zaro bulala zai fara lafta mata wai aljanun masu taurin kai ne. Tana ganin haka ta tashi a guje ta koma ciki.

Bayan 'yan kwanaki ta sami Dr Tani har daki tace ita dai tana son aure tunda Dahirun bai samu ba su taimaka su sama mata miji.

Ranar hankalin Dr Tani ba karamin tashi yayi ba don da kyar tayi bacci. A ina zata sami mai auren Qareeba? Bata son mijinta yaji wannan maganar sam domin a danginsa zai nema daga nan su sami na gori ace gwanjonta aka yi musu. Mutum daya gareta da ta rike kawa aminiya amma sun kwana biyu ko gaisuwar kirki bata shiga tsakaninsu ba. Duk da haka gani tayi gara ta sake gwada sa'arta a karo na karshe kafin a nemi wata mafitar.

Wayarta ta dauko ta jima tana sake-sake kafin ta danna kira.

Haj Mara tana zaune yau ko wanka ta kasa abin duniya ya isheta ta mika hannu ta dauki wayarta da take ruri. Sunan Dr Tani ta gani to itama damuwa ta isheta ta dauka da sauri ta gyara muryarta tayi sallama.

Dr Tani tana amsawa Haj Mara tayi wata shewa kamar bata san waye ba sai yanzu "Tani kece don Allah? Wayyo aminiyata shiru shiru na rasa nambarki ke kuma kin dena nemana"

Dr Tani taji dadi ashe dai Haj Mara bata ya da ita gabadaya ba rashin number ne amma sai ta dan dake.
"Haba Marakisiyya idan babu waya baki san gidana bane? "

Kamar zata yi kuka tace "na sani amma tun tafiyar Babawo naga kamar kinyi fushi dani. Kuma na fada miki Alhaji ne yace gara ya bar kasar kura ta lafa"

"Har shekara takwas? Ni mu bar wannan zancen dama kira nayi mu gaisa inji lafiyarku" ga dama ta samu na son jin yaya BB amma tana gudun kada ace yayi aure.

Kamar Haj Mara ta sani tace "ina 'yata kuwa Qareeba? Nasan yanzu kila tayi yara biyu ko uku. Ba rabonmu lokacin gashi shi yaki aure har yanzu"

Kankame wayar Dr Tani tayi dadi har kasan zuciyarta
"To ai nima har yau Qareeba dai tana nan in fada miki taki kowa. Nayi fadan nayi nasihar duk a banza. Wai tunda ta rasa BB na farko ta hakura da aure ke kiji"

Wata siririyar dariya Haj Mara tayi. Ta sani sarai Qareeba babu mashinshini ne tunda takan dan bibiyi me Dr Tani din take ciki. To amma dama ce ta karshe ta samu ta yiwa Babawo aure ko ya kintsu kamar kowa.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰15

*Batul Mamman*💖



Tsohon kango ne wanda yaran unguwar da yake ciki ma tsoron yin dare suke a kusa dashi saboda 'yan daban da suka mayar dashi wurin sheke ayarsu. Daidai ballallen gate din BB ne zaune cikin daya daga cikin motocin Alh Sule yana yiwa shugaban 'yan daban bayani.

"An fada min kaima dan Kano ne ina tunanin nemanta bazai yi muku wahala ba"

Garwashi yace "to Yallabai ka bamu hoto da adireshi mana saboda rage wahala ko ya kace."

Sosa yamutsatstsen kansa yayi wanda yaki yarda ya aske har yau yace da yasan address din me zai kawo shi wurinsu ma. Gajeren tsaki yaja sannan yace.

"Sunanta Mawadda kauyensu yana cikin Kabeji a nan Kano"

Me Garwashi zaiyi in ba dariya ba "Kabeji kuma Ranka ya dade kwadon salak zaka yi hala?....hahahahhh zan taho maka da caras da gurji"

A fusace BB ya fito daga motar ya damki wuyansa. Yaran Garwashi suka soma tasowa ganin an kama ubangidansu. Shaka sosai BB yayi masa yana huci "ba wasa bane ya kawoni. Sati daya na baka ka nemo min inda take koda gidan miji ne zan baku 500k."

Jin haka Garwashi ya daga hannu ya dakatar da yaransa. BB ya ture shi har ya kusa fadowa ya dago kai a wahale "zamu duba amma duk da haka ka bamu wata inkiya mana yadda zamu jidadin yi maka aiki na dai fahimta garinsu a Bebeji yake ko"

Sai da ya shiga mota ya zauna sannan yace "anyi mata fyade shekara takwas da suka wuce har kotu an shiga amma basuyi nasara ba"

Zaro idanu Garwashi yayi "wane dan...."
Sai kuma yayi shiru ganin irin kallon da BB yake yi masa kafin ya bada musu kura yaja motar yayi gaba.

Yaransa da suke gefe suka marmatso yana rike da wuya yana jujjuya shi.

Na hannun damansa cikin yaran yace "Baaba ina tunanin shine fa yayi fyaden kaga ai yayi kalar eh yane. Kuma don rainin sense ya shake maka wuya a fadarka don yana takamar tsohonsa yana da maiko"

Cecekuce yaran suka soma suna nuna takaicin hanasu su far wa BB lokacin da ya shake shi.

"Ku barni dashi zamu nemo yarinyar nan duk inda take. Amma kwarankwatsa zamu nuna mata solidarity tunda 'yar uwa ce bakanuwa. Gayis (guys) mu ware gobe akwai trabilin gabanmu."

******

Mawadda na zaune gaban Baba daga gefen tabarma a tsakar gidansu. Yaya da Ade suna dakunansu haka ma Iya da Inna.

Kamar kullum nasiha da yabonta ya soma yi don baya gajiya wurin karfafa mata gwiwa akan hakuri da tawakkali.

"Ina alfahari dake sosai da yadda ki ka karbi kaddara bata sanya kin zama daga cikin mutane masu gazawa imaninsu yayi rauni ba. Ki cigaba da mika lamuranki ga Allah da sannu zakiyi ta girbar alkhairi kinji."

"In sha Allahu Baba"

"Bayan wannan Mawadda ina so kada kiji kunyata ki fada min gaskiya yaya kuka yi da Dahiru?"

Faduwar gaba taji hade da kunya a lokaci guda ta dukar da kanta sannan ta fada masa gaskiya wato maganar aure da Dahiru yayi mata sai dai bata fada masa yadda suka kare da ya zama yayanta kawai ba. Ta dai sanar dashi bata amince ba.

"Baba kada ka damu nima na san ba zanyi aure ba saboda bazan yaudari kaina ba" ta fada cikin dakakkiyar murya tana kokarin boye karayar da zuciyarta take neman yi.

Tausayinta Mal Fatihu yaji sosai "Allah ne Masani ko kina da rabon aure ko babu. Abinda nake so ki kiyaye dai bai wuce kada kisa Dahiru a zuciyarki ba. Kinga yadda abubuwa suka kasance a da bana jin yanzu zata sauya zani. Duk yadda na matsu inga kina dakinki kamar sauran 'yan uwanki bazan taba yarda kije inda ba'a bukatarki ba. Na shaida Dahiru mutum ne managarci amma aure Mawadda ba alaka bace tsakanin mata da miji kawai. Ta hada da iyaye da 'yan uwa makusanta. Duk inda kika samu matsala da daya daga ciki ko iyayen miji ko 'yan uwansa to ina mai tabbatar miki miji ko hadiyarki yake don kyautatawa sai jindadinki ya ragu musamman idan iyayensa ne."

Kasa daurewa tayi hawaye ya soma fita a idanunta "Baba zan kiyaye in Allah Ya yarda" tana kaiwa nan ta tashi ta bar wurin da sauri saboda kukan da ya taso mata. Bandaki ta shige ta rufe kofa ta shiga kuka har tsakar gidan Baba yana jiyo shesshekarta.

Shi kanshi ba don namiji bane babu abinda zai hana shi tayata kukan. Zuciyarsa ce tayi masa nauyi yana kara ganin laifinsa ne na turata aiki tun farko har haka ta faru. Amma zasu cigaba da hakuri har Allah Ya kawo musu mafita.
*****

Washegari tana gama ayyukanta na gida asibiti ta tafi. Da yake da wuri taje bata dade sosai a layi ba.

Dr Imran ya gama jin duk wani bayani nata ya nuna mata file din gabansa.

"Duk wani bayani ko gwaji daga ranar da na fara dubaki har yanzu suna cikin nan. Ina fata kin rike duka bayannan da nayi miki game da ainihin abinda ya sameki har ya janyo miki lalurar?"

"Na gane Doctor. Nagode sosai" tace a hankali tana kokarin boye hawayenta. Tun maganarsu da Baba jiya haka ta tashi sukuku. Ba wai abin mamaki bane kuma itama kafin ya fada ta riga tasan da hakan. Sai dai yanzu tausayin rayuwarta take yi kawai. Bata taba hango rayuwarta zata zama haka ba. Tuni ta gama shiri da tsara rayuwarta da Dahiru a shekarun baya sai gashi Allah Ya zartar da ikonSa ta koma mai gyara amare wadda bata da ranar ganin nata auren.

Dr Imran tashi yayi ya dawo dayar kujerar marasa lafiyan wadda take kallonta ya zauna. Yana ganin yadda ta sake tura tata baya duk da cewa akwai tazara tsakaninsu tun farko. Ya sani irin haka yana daga cikin tsoron da yake bibiyarta har yanzu. A kokarinsa na taimaka mata ta rage ne yasa idan ta shiga office dinsa yake tilasta mata rufe kofa ko bata so don ta gane ba kowane namiji bane macuci. Tun tana zama tayi ta kallon kofa tana hawaye har ya samu ta dena kukan. Yanzu gashi ta yarda dashi zata zauna ba tare da tunanin komai ba.

"Mawadda."

"Na'am Doctor"

"A ka'ida yau ne last day da zan duba ki sai dai idan wata matsalar ta taso wadda bama fata."

Godiya tayi masa amma yadda ya gama karantarta na tsahon lokacin da take zuwa asibitinsu ya san tana da damuwa a ranta.

"Ko soyayyata ce tayi miki mugun kamu kike tunanin daga yau zamu rabu? Banyi niyar barinki ba yau ko kinki ko kinso zan zo gida neman izini wurin Baba"

Kai ta dago da sauri "don Allah kada kazo. Na fada maka bazanyi auren nan ba."

"Saboda wani banzan BB yake ko wa? Ki barshi haka duk inda yake sakayyar Allah zata kama shi" Ya fada ransa yana dan baci.

Kai ta girgiza tana soma kuka "ni dai kawai"

"Ke dai kawai me? Ko dai Dahiru ki ke jira?"

Dr Imran yasan labarin Mawadda domin kuwa bata boye masa komai ba bayan ya hillaceta da dabararsu ta likitoci a kokarin taimakonta. Duk duniya babu wanda take iya fadawa abubuwan da ba kowa ya sani ba bayan iyayenta sai shi.

Yanayin da yaga ta shiga yasa shi gane ko ma meye matsalarta da Dahirun a ciki. Rarrashi da shawara ya soma bata da kanta ta fada masa dawowar Dahiru cikin rayuwarta da kuma kudurinta na kin amince masa.

Dariya yayi ya shiga zolayarta "Akwai matsala kuwa don nima ba hakura zanyi ba. In fact kince na kara zage damtse mai rabo ya dauka. Wato ciwon soyayya zai tashi shine duk naga jikinki a mace yau kamar wata mara lafiya."

Sai da ya gama sawa ta saki ranta sannan yace ta yawaita addu'a da neman zabin Allah.

"Nasan kina son Dahirun nan Mawadda bazanyi muku katsalandan ba har sai naga yadda ta kasance. Ki sani dai ni masoyinki ne mai burin kyautata rayuwarki. Ina fata zumuncinmu ya dore ba wai kawai tsakanin likita da patient ba"

Taji dadin saurin fahimtarsa don bata jin zata juri fama da maza biyu akan abinda duka babu lallai su samu. Sun jima suna hira kafin wata nurse ta shigo tace ya bar mutane suna jira fa.

*****

Hira Dahiru da Attahir suke yi suna tsara bikin Attahir din da yake gabatowa nan da wata uku.

Ango yana ta zumudi suna lissafin nawa za'a ware domin hada lefe da sauran abubuwa.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login