Showing 6001 words to 9000 words out of 110071 words

Chapter 3 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

176

inda aka ce ta rinka dakatawa saboda ba'a taka kafet indai ba maisharar cikin gidan ba ta durkusa.

"Dama akan maganar da na soma yi miki ce rannan na zuwa gida naga baki ce komai ba"

Tsaki Sakina ta buga ta ajiye remote din hannunta.
"Bala'i! wato na lura Ade ke fa da mayya ce idan kika kama mutum sai buzunsu. Kin tado maganar nan yafi sau biyar saboda bana son ji nake katseki amma kinki hakura. Ku wai baku da aiki sai son zuwa gida? Kwanaki kince kaciya akayiwa autanki na barki kinje har kwana biyu yanzu kuma kina son sake zuwa wani wurin..wane uzurin gareki kuma?"

Duk da ranta ya baci haka ta danne "Yarinyata ce bikinta ya matso watan cika ciki"

"Yarinyarki kuma? Yaranki duka ba maza bane su hudu kuma dai ai suna yawan zuwa gidan nan ganinki tunda suma a cikin Kanon suke"

"Ita babbar a kauyenmu take wurin nata mahaifin"

Sakina ta sake jan tsaki. Wannan abu yana matukar konawa Ade rai don bata son ayi mata tsaki amma ya ta iya.

"Gaskiya bana son yawo Ade idan aikin kika gaji dashi sai na nemi wata"

Hankali a tashe tace "Hajiya me ya kawo neman wata? Wallahi bikin 'yata ne baifi wata biyu ya rage ba. Shine nace bari na sanar dake da wuri don nasan ba kya son titsiye"

Shiru Sakina tayi tana tunanin muddin Ade ta tafi zasu wahala. Ita take wanke wanke da kula da yara. Mai shara namiji ne dama sai mai girki wata bayerabiya duk rashin mutumcinta bata iya yi mata saboda tsoronta ma take ji. Matar bata daukar raini don da iliminta. Ade kuwa marainiyar wayonta ko waya zata kira sai ta bata ta roki ta nemo mata sunan da take son kira.

Da gangan tasha kunu "Ni dai bangane wani watan cika ciki ba. Bayan sallah da kusan sati biyar za'ayi bikin babban dan Alhaji kuma baki da yawa zasu sauka a gidana. Idan kin bincika watan bikin yar taki a na bature sai ki fada min. Satin bikin ki tafi talata ki dawo lahadi. Nasan halin mutanenmu uwar amarya bata wani abin kirki a bikin 'yarta akwai 'yan uwa da abokan arziki."

Ade tayi shiru tana tunani. Wato bikin dan Alhaji shine biki na 'yarta kuma ko oho. Dan kudin da take samu a gidan ba karamin tallafi yake mata ba. Ga yara hudu a gidan mijin data baro ga babbar a kauye tare da nata uban da aurensu ya dade da mutuwa. Bazata so rasa aikin nata ba shiyasa ta amince da sharadin Sakina ba don taso ba.

Murmushi tayi wai Mawaddanta ta isa aure. Da aikin nan ta hada ya kusa dubu dari da zata fito da tilon diyarta wadda kaddara ta rabasu.
*****

Gidan Mal Fatihu kuwa sun tashi da bakinciki da bacin rai. Mawadda a kwance take ba yadda take don jikinta har wata irin kyarma yake. Yau Yaya da kanta tayi mata wanka duk inda ta taba Mawadda sai tayi kara. Sai lokacin ta tabbatar da muguwar barnar da BB yayiwa diyarta. Har wani wari ciwon ya soma fitarwa saboda rashin kula da muninsa. Lokacin zabura Mawadda ta rinka yi tana sambatu sai kayi zaton wata mai haihuwa ce. Kuka sosai suka sha sannan ta fito da ita tana taku da kyar. Kannenta kuwa yadda suka dauka aljanu ne haka iyayen suka barsu.

Abu irin wannan babu mai son duniya ta sani shiyasa suke komai su kadai. Sunyi shirin tafiya asibitin karamar hukumarsu ruwa ya kece babu yadda zasuyi suka koma gida. Sannan ne kuma Yaya ta bawa Baba shawarar kiran Ade a matsayinta na mahaifiyar Mawadda.
[03/12 23:02] Meela Adeel: *FIKRA WRITERS ASSOCIATION*


*GUMIN HALAK...*馃挵1

*Batul Mamman*馃挅

*Bismillahir Rahmanir Rahim*



Karar rufe kofar dakin Hajiya ta jiyo alamun ta gama shiri zata fita. Gabanta ne ya fadi saboda fargabar da ta dirar mata.

"Shikenan na banu na lalace" ta fada a fili cikinta yana wata irin yamutsewa saboda tashin hankali.

Tun shekaranjiya bata da lafiya ga matsanancin ciwon jiki amma ta kasa fadawa kowa. Hawaye ne ya shiga sintiri a kumatunta taji bazata iya karasa wanke tukunyar da ta fara ba ta ajiyeta a sink ta fito falon a gaggauce.

Baki na rawa kamar wani zai rigata tace "Haaaa....Haa..Hajiya...Hajiya yau ma fita zakiyi?"

Wani irin kalo Hajiyan ta bita dashi rai a bace tace
"Lallai Mawadda ni kike tambaya ko fita zanyi? Ni da ke wa yake zaman wani?"

Ko dukanta zata sake yi yau ma bazai hanata magana ba. Durkusawa tayi akan gwiwoyinta ta hada hannuwa tana kuka sosai.

"Don Allah Hajiya a kaini gida bani da lafiya"

Haj Mara ta sami wuri ta zauna tana mata kallon tuhuma.

"Ke! Tashi ki dauko min jakar kayanki maza-maza kafin na kirga uku kin dawo"

Da hanzari Mawadda ta tashi ta dauko jakar Ghana mustgo dinta harda sako hijabi ta fito da 'yar murnarta zata rabu da kaya.

Haj Mara tana zaune tana karkada kafa ta warce jakar ta zazzageta a kasa. Da kafarta wadda take sanye da takalmi ta rinka bankade mata kaya ta tabbatar babu wani abu a ciki da ba na Mawaddan ba sai tsirarun tsofaffin kayanta da ta bata tun farkon zuwanta Kaduna ta fara mata aiki.

Ita dai Mawadda tana daga gefe tana kallon ikon Allah. Kayan sawarta ne kamar kashi a kasa ake takewa da takalmi. Abin bai ma bata mata rai ba tunda a ganinta burinta zai cika-zata bar gidan.

"Tattarasu ki mayar daki"

"Na'am" ta fada cikin zaro idanu.

Tsawa Haj Mara tayi mata wanda yasa ta fara kwasar kayan tana cusawa a jaka.

"Dama nayi zaton sata kika yi min shiyasa kike son tafiya gida na kuma ga ba hakan bane. Makota da kike shiga ne idan na aikeki aka zuga ki ko me?"

"A'a Hajiya bani da lafiya ne"

"Kinibabbabiya sai kiyi ta sunne kai irin na rikakkun munafukai. Wata gulmar ce zaki ce kina son tafiya ko shekara bakiyi ba. Ita mai kawokun duka duka yaushe tazo ta karbi kudin aikinki bakiyi zancen tafiya ba sai yau"

Ita dai bazata iya fadin dalili ba ko don tsira da rayuwarta amma a barta ta tafi kawai.

Ta cigaba da sababi "Dama haka kuke masu aikin nan da shegen kwadayi da rashin godiyar Allah. Sai kuzo da kunyi 'yan watanni an murmure ku fara hangen wani gidan. Ki bace min da gani kafin jikinki ya fada miki. Kuma ki tabbatar kin gama komai kamar yadda na fada miki tun daren jiya kafin na dawo. Banza jaka sai kiyi ta rarraba ido irin na mayu. To kurwata kur idan ma ita ce. Kudi dai ina aikawa iyayenki balle ace kyauta kike min"

Tunda ta fara magana Mawadda ko tari batayi ba sai zubar hawayenta da ya karu. Nadama ce fal a zuciyarta da mamanta ta dage bazatayi aikatau ba irin na sauran 'yan uwanta amma ita da Baban suka kafe wai a haka zata samo kudin da za'ayi mata kayan daki ga nauyin gidansu yayi masa yawa. Tabbas suna fama da talauci kuma gidansu babu maza sai yaran karshe biyu duk kananu bare su taimakawa Baban nasu. Sai gashi wata bakwai da zuwa ta gane tayi kuskure babba ma kuwa. Haj Mara masifaffiya ce ajin karshe ga rashin sanin darajar dan Adam. Duk da shekarunta sha bakwai amma yanayin rayuwa da wahalar kauye sai ka zata bata fi sha hudu ba. Idan tayi laifi duka Hajiyan keyi mata kamar wata kankanuwar yarinya ga zagi da gori har sun dena damunta ma. Duk wannan ba shi bane tashin hankalinta kamar dan Hajiyan da ya dawo daga turai BB wata daya da ya wuce. Dan duniya ne na bugawa a jarida ko irin kyamar nan ma baya mata ganinta 'yar kauye burinsa kawai ya bata mata rayuwa. Har alkawarin kama mata gida yayi da taki yarda shekaranjiya yaso gwada mata karfi suka sha dambe a dakinsa da aka shardanta mata gyarawa da kyar da sudin goshi ta kwaci kanta.

Jiya da Hajiyan ta wuni a gida ko bangaren bai shigo ba amma ta tabbatar tana fita zai dawo. Ta rasa yadda zatayi domin yace idan ta fada sharrin sata zaiyi mata yasa a kulleta a gidan yari. Da yake batayi karatu ba kuma babu wayewa shiyasa ta yarda da maganarsa ta kasa fada kuma tsoronsa yayi mata mugun kamu.

Tana wannan tunanin bata ma san Hajiyan ta fice ba haka ta dauki kayanta ta koma daki jiki a sanyaye.

Bayan ta ajiye ta dawo ta kama kofar falon ta rufe da sakata sannan ta saki dukkan labule tana fatan tsira daga sharrin BB sai ji tayi ana kokarin dagata ta baya. Wani irin razanannen ihu ta saki kafin ya gama fita daga bakinta ya toshe shi da hannu daya ya soma janta zuwa dakinta.

Suna shiga ya rufe kofar sannan ya dauko wata 'yar karamar wuka daga aljihunsa yana dora hannu akan labbansa. Ba shiri ta hadiye ihun da take shirin yi.

"Ka yiwa Allah ka rufa min asiri"

Katifarta ya dare ya kwanta yana mata wani irin kallo.

"Kinga malama ki saki ranki kici arziki. Duk yarinyar da tazo aiki birni dama ai abinda yake kawoku kenan. Kuji dadin zama ku fara neman mijin da zai ajiyeku a nan kada a koma kauye"

Cikin shesshekar kuka tace "ni anyi min baiko watan cika ciki za'ayi bikina"

"Me zakiyi da dan kauye keda kika dana birni? Nasan kina so gulma ce kawai kada nace miki 'yar hannu. Idan kika amince min fa aurenki zansa Hajiya ta nema min"

Jikinta sai tsuma yake tana kalle-kalle ko akwai wata mafitar bayan kofa. Bata manta irin kashedin Babanta kafin ta taho harda ikirarin sai ya yankata idan ta kwaso abin kunya duk don ya tsorata ta da sauya hali.

Shi kuwa BB wukarsa ya rinka karkada mata karshe ya bukaci tazo ta kwanta itama.

Ja da baya tayi dan hakurinsa tuni ya kare ya taso yayo kanta da wukar. Saduda tayi kawai tana kuka tace gara ya kasheta da ta amince ya bata mata rayuwa. Ganin idonta ya kekashe kawai ya jefar da wukar ya fincikota. Mari ya rinka tafka mata ta hagu ta dama ta ma rasa kuncin dafewa sai kukan da take yi kawai. A haka ya kaita kasa ya bita tana ihu tana rokonsa.

"Wayyo Allah, Baba ka taimakeni, Yaya za'a cutar miki da 'ya....."

Ihunta duk ya cika masa kunne ya zare dankwalinta tana shirin tashi ya danne mata ciki da gwiwar kafarsa sannan ya dangwarar mata da kai akan tiles din dakin ta koma bata iya motsi sosai. Bakinta yake kokarin daurewa tana cewa.

"Wuta balbal BB, wuta balbal bazan yafe maka ba ko kabarinka yana ci da wuta. Ko walakiri...."

Tana ji tana gani ya daure bakin ta samu ta sa kafa ta kai masa naushi a ciki har ya fada da baya. Wannan takaicin yasa shi zarar belt ya rinka tafkarta sai da yaji gunjin kukan ma bata iyawa sannan ya wurgata kan katifarta.

********
Haj Mara bata karasa gidan kanwarta da zata je ba duba maigidanta da ba lafiya kawai ta tuna yanayin fuskar Mawadda. Tsaki tayi don kawar da abin amma ya gagara. Kasa karasawa tayi duk da har ta shiga unguwar ta juya motar ta koma gida.

A wajen gate ta sami maigadinsu yana cin gyada. Ganinta da yayi yasa batayi horn ba ya bude mata kofar ta shige.

Iyakar rashin imani BB yayiwa Mawadda don jinta take yi kamar ba a duniya take ba shiyasa ko motsi ta kasa. Kwatanta ciwon da take ji ma bazai yiwu ba. Yana tashi yasa kafa ya haureta

"Banza arziki na binki kina gudu. Kuma wallahi na fada miki wani yaji zancen nan sai na farke miki ciki. Sannan ki fara shiri gida zan kama miki zamu fi sakewa don bana son takura"

Jin kofa da Haj Mara tayi a garkame yasa gabanta ya dan fadi. Sai tayi tunanin zagayawa ta baya ta shiga ta kitchen. Daidai tagar dakin Mawadda taji muryar BB hantar cikinta ta kada tayi saurin komawa ta kara kunne.

"Dalla malama ki tashi ki gyara jikinki kafin Hajiya ta dawo duk da dai nasanta da yin dare a waje idan Alhaji baya nan"

Haj Mara ta dafe kirji a tsorace tayi sa'a tagar ba a rufe take ba tasa hannu ta daga labulen. BB ta hango duke kan Mawadda yana kai mata mari "ke tashi mana ko wani sabon salon...."

"BABAWO!!!" Abinda Haj Mara ta iya fada kenan da karfi kafin ta soma gudu ta shiga gidan. Dakin Mawadda taje ta hau bugu tana cewa su bude. Bashi da zabin da ya wuce budewar saboda da ido kawai Mawadda ke binsa amma taki motsi balle ta tashi yana tsoron ko ta suma ne .

Bangaje shi Hajiya tayi ta shigo kamar zakanya tayi kan Mawadda ko kula da yanayinta batayi ba ta kwada mata mari.

"Karuwan kauye kunfi kowa iskanci. Ku shigo birni ku lalata magidanta da 'ya'yansu"

BB ne ya rike mata hannu zata sake dukanta "Hajiya bata motsi fa. Ba dai kin kashe musu 'ya ba. Ni dai babu ruwana da ranta na barta"

Sai a lokacin ta kula bakin Mawadda a daure yake ta yaye bargon ba shiri ta kawar da kai.
"Auzubillah Babawo ka jawo min masifa. Fyade kayiwa 'yar mutane?"

Mawaddan ya kalla wadda azaba taci karfinta tsoro ya kamashi kada ta mutu.
"To ai kece Hajiya nasan da cewa nayi ina son aurenta bazaki yarda ba"

Tashi tayi tana kuka tayi kansa da duka "fita dan ubanka....na shiga uku na."

Da kyar ta tallafi Mawadda ta dagata zaune ta ma rasa me ya kamata tayi mata kuma. Hannunta da kyar ya iya zaro waya a jakarta ta kira maigidanta Alh Sule Chanji. Yana can Lagos inda harkokin nasa suka fi karfi. Ko da ta fara masa bayani ba karamin tashin hankali ya shiga ba. Fada ya soma yi mata kamar ita tayi sannan yace a kai yarinyar asibiti yana nan tafe ranar laraba.

Haj Mara ta amsa har ta sakawa Mawadda kaya wata zuciyar ta kwabeta akan tonawa kanta da gidanta asiri. Dammara taci da mayafinta dankwali kuwa bata san inda ya fadi ba ta tafi dakinta ta debo ruwan zafi bokiti uku. Ita kadai take ta hawa da sauka bene BB ya fice ma bata san inda yayi ba. Haka ta zage ta soma yi mata wanka sai dai tana soma jin kwari a sanyaye tace zata iya.

Fita Hajiyan tayi tana ta kai kawo a dakin har Mawadda ta fito tana bin bango. Sai a lokacin ta tuna yadda ta rinka rokonta akan zuwa gida. Data sani ta barta da haka bai faru ba.

Ganin Hajiya a dakin yasa ta saki wani irin kuka mai shiga rai. Haj Mara ta riko hannunta zata zaunar da ita akan katifar ta zabura ta fice daga dakin da sauri. Ko zata mutu babu ita ba wannam bakin daki da ya kafa mummunan tarihi a rayuwarta balle kuma katifar.

A korido Hajiya ta ganta ta kama hannunta batare da tayi magana ba ta kaita nata dakin a sama. Daga cikin kayanta ta dauko mata doguwar riga wadda fadin ne kawai yayi mata yawa saboda Haj Mara ba tsayi gareta ba. Bayan nan ta bata shayi da maganin ciwon jiki tasha bisa tursasawa. Sai da ta dan nutsu Haj Mara ta soma magana.

"Mawadda kiyi hakuri akan abinda Babawo yayi miki kuma don Allah ki rufa maganar nan kada kowa yaji "

Batayi mamakin furucin Hajiyar ba saboda ta dade da gane mutane suna da son kai.

"Hajiya ki kaini asibiti don Allah" kuka ne ya taso mata mai karfi.

"Idan muka je asibiti kama Babawo za'ayi a kulle ki taimaka kiyi hakuri zan baki magani" Dole ta lallabata kada ta janyo musu bacin suna.
"nasan aure zakiyi kwanannan shiyasa zan baki kudi sosai saboda hidimar bikin naki. Kina samun sauki ko zuwa jibi ne zan mayar dake gida. Maganar nake so ta mutu kawai. Babawo shi kadai ne dana namiji kuma ya sami aiki a babban kamfani bana son abinda zai shafi mutumcinsa"

Yanzu kam tayi mamaki tunda son kai yasa an nuna mata ita nata mutumcin ba abin dubawa bane. Wani irin kallo tabi Hajiyar dashi musamman da taji tana waya da mijinta tana sanar dashi ai suna asibiti har an basu gado. Ransa duk a bace yace kada ta bari Babawo ya sake fita don har garinsu yarinyar sai sunje ta bishi da to kamar gaske.

Ranar Mawadda a dakin ta kwana da mugun zazzabi da ciwon kai bacci ma kasawa tayi. Ko yaya ta rufe ido Babawo take gani ga ciwo ko tafiya bata iyawa sai ta dafa bango amma anki kaita asibiti.

Da safe data tashi fuskarta duk ta kumbura lebe yayi suntum saboda buguwa ashe ya fashe ta ciki. Hajiya da kanta tayi komai Mawadda tana jinsu da da BB tana masa fadan yana son bata musu suna. Haka ta wuni a daki tana kuka Hajiya na kawo mata abinci da panadol wai maganin rage ciwo ne.

Bayan kwana biyu ana gobe Alhaji zai dawo Hajiya ta shigo gidan da sassafe da kaya niki-niki cikin ghana must go biyu manya tasa Mawadda ta sakko daga sama da mayafinta.

Kayan ta nuna mata wai na yaranta ne mata biyu masu aure da na yaransu gashi nan ta kai gida tsaraba. Sai wata jaka ita kuma sababbin kaya ne atamfofi da shadda harda leshi wai tayi fitar biki. Sai kuma kudi dubu ashirin ta dora mata a hannu.

"Mawadda"

Idonta da baya rabo da hawaye yanzu ta dago tare da amsawa. Kana ganinta kasan a tsorace take gani take kamar BB zai shigo. A yanzu ko cokali ne ya fadi sai ta zabura. Ga tafiyarta gabadaya ta canja saboda ciwon da Hajiya taki kaita asibiti balle asan taimakon da ya kamata ayi mata.

Fuska a hade ta cigada da cewa "Yau zan mayar dake garinku. Wannan duk na baki ne ki kai gida magana kuma ta mutu. Wallahi duk ranar da wani naki yazo min da zancen abinda ya faru tsakaninki da Babawo zan sanar dasu bin maza kike yi shiyasa na gaji na dawo dake. Ke da duka garinku bana jin zaku iya rigima dani don bani da mutumci ke shaida ce. Ki kama bakinki sawunki a likkafa kiyi shiru kawai. Zan iya sawa azo har gida a harbeki da iyayenki kinsan kanina soja ne kin sha ganinsa a gidan nan da bindiga"

Zuciyar Mawadda ta tsinke da lamarin Hajiya sai tsoro da ya shigeta. Ita wa ma zata fadawa balle

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login