Showing 105001 words to 108000 words out of 110071 words
Chapter 36 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt
Sai da aka gama komai aka kwashesu sai police station. Wannan karon harda Bobo anyi nasarar kamawa inda suka tarar da kofur Pascal a cell din shima yaci uban duka. Haj Mara kuma tana bangaren mata.
Sai da komai ya kammala da yamma aka kira Dahiru aka sanar dashi an kama su BB kuma an matso da shigarsu kotu nan da sati daya. Godiya yayi musu yace Allah Ya nuna mana lokacin.
******
Kwanan Dahiru uku aka sallame shi. A cikin kwanakin nan ya san shi cikakken dan gata ne don sosai Mawadda take bashi duk wata kulawar da ta dace. Shagwabarsa yake mata son rai tana biye masa.
Qareeba kullum sai taje asibitin inda ita da Bilya suka sake shakuwa kowa ya san da soyayyarsu mai ban mamaki.
Son juna suke yi da gaske ba wai don Dahiru yayi masa tayinta ba itama ba don ta dade da rashin aure ba. Cikin dan kankanin lokaci Bilya ya gama fahimtar wacece Qareeba. Mutane sun santa da dolanci da shagwaba ne kawai. Shi kuwa a yanzu ya santa a matsayin mutum wadda bata boye boye. Abinda tasan gaskiya ne to ko a gaban waye bata shakkar yinsa. Haka zalika shagwabar da dolancin shi burge shi suke yi sosai. A tata fahimtar kuma ta gane Bilya irin mutanen nan ne masu sadaukar da farincikinsu domin kyautatawa wasu. Yana da matukar kirki da saukin kai. Sai kuma to her advantage ta gane baya jindadin rayuwar aurensa. Bai fada ba amma a shekarunta da iya abinda ta gani game da Furera ta san cewa Bilya aure dai yana dashi amma soyayya irin ta ma'aurata ku nesanta da juna kuna begen juna bai sansu ba. Hirar soyayyar ma bai iyawa sosai sai kawai tayi amfani da wannan damar take nuna masa kulawa irin wadda bai saba gani ba. Hakan yasa nan da nan ta shige zuciyarsa. Balle yadda take yiwa 'yan uwansa.
Daren ranar da za'a sallami Dahiru ta kira Bilya. Yana zaune ya saka abinci a gabansa sai juyawa yake ya kasa kai ko loma daya saboda masifar Furera. Abincin ma Hansa'u ce tayi don ta dena girki babban dansa ya kawo masa.
"Ka dai ji kunya Yasin. Ka rasa wadda zaka nema sai matar da kaninka da kuka fito ciki daya ya gama wankewa rigar mama."
Bai iya fada ba wannan sai Dahiru. Shiyasa yaki kulata. Amma furucinta na karshe ya kona masa rai "idan dai ya taba wankewa to lallai Dahiru ya cika yaron kirki mai girmama na gaba. Tun a lokacin ashe yaji a jikinsa matar yayansa zata zama shiyasa yake wanke komai nata"
"Rigar mama fa nace ko baka ji da kyau bane"
A hankali saboda baya son daga murya yaransu suji yace "naji mana. Idan ta zo sai ni kuma na cigaba da wanke mata tunda 'yar hutu ce bata saba ba"
Haushi ya kamata saboda so take suyi fada kuma yaki biye mata. Sai ta chanja taku "wa ya sani ma ko sai da suka gama watsewarsu aka yi maka tayin kwantai"
Hannu ya daga zai mareta sai ya kasa. Yadda taga idanunsa sunyi ja ba karamin tsoro ya bata ba. Amma ganin ya sauke hannun ta shiga tafi harda guda.
"Ahayyeeee nanaye...wato saboda zaka yi aure kake shirin dukana. Ga fili ga maidoki wallahi ka tabani ka tabo masifa ka tabo bala'i. " ta nuna shi da yatsa tana cigaba da cewa "banda kai ma dai lusari ne mara zuciya me zai kaika yin auren jari auren kwadayi"
Bata gama rufe baki ba ya falla mata marin da yake ta kokarin danne fushinsa kada yayi.
"Furera bana son zama cikin mazan da suke tauye iyalansu don suna neman aure amma ki sani idan ki ka kaini bango ranki ne kadai zai baci. Qareeba zata shigo gidan nan ba da dadewa ba in sha Allahu. Bazan ce ki kwantar da hankali ku zauna lafiya ba. Idan tazo ki cigaba da nuna mata haukanki itama zata nuna miki nata. Kuma ina mai tabbatar miki ke karamar alhaki ce a wurin Qareebata"
"Qareebarka? To ni kuma ta waye?" Tace a fusace.
"Ohooo"
Fita yayi abinsa bayan yasha turare yayi kyau sai gidan Dr Tani. Yau Dr Auwal ne ya bukaci ganinsa inda ya tabbatar masa ya bashi ita bayan yayi masa 'yan tambayoyi.
Gida yace zai bashi kyauta inda zai sakata yace ayi hakuri zai kama haya kafin ya gama ginin da yake yi a Zawaciki. Bai nemi Qareeba don ta zama jarinsa ba. Ya tabbatar samunsa na yanzu da yardar Allah zai ishe shi ya rike mata biyu.
Wani sabon girma da kima ya kara a idon su Dr Tani suka ce idan an gama da case din BB ya turo domin basa son a dauki lokaci mai tsaho.
Bayan sun shiga ciki ta fito da murnarta.
"Bilyana Mummy ta fada min an baka ni"
"Shiru ya kamata kiyi ni zan fada miki da kaina"
Bakinta ta rufe tana dariya. Can kuma tace "gaskiya ka bani wuya sosai"
"Da nayi me?"
Da muryar shagwabarta tace "Tun yaushe ka sanni ashe kaine mijin amma sai yanzu ka fito"
Dariya ta bashi "ko in koma ne?"
"Wasa nake yi don Allah"
Kayan abinci ta jere masa kamar tasan da yunwa yazo. Yana ci tana masa hira mai cike da ban dariya.
******
Washegari karfe bakwai a gida ta yiwa Mawadda. Ta gyara gidanta da ya soma hada kura saboda shigowar sanyi ko ina sai kamshi. Lafiyayyen girki tayi sannan ta shiga bandaki ta soma gyara da turara jiki tamkar amarya.
Shiryawa tayi cikin kananun kaya bisa shawarar Nawal. Wando ne mai laushi a hannu amma a ido kamar jeans blue ya kama jikinta. Rigarta fara mai dogon hannu da duwatsu a tsakiya itama ta kama ta. Kunyar kayan taji don bata taba shiga irin wannan ba sai yau. Navy blue din mayafi siriri ta samu tayi yafa a kanta da yasha gyara.
Tana gaban mudubi wurin biyu da rabi taji shigowar mota ta hau murmushi ita kadai. Dama duka kayan kwanan nasu ta taho dasu tun safe abin sallah guda daya ta bar masa da zata taho. Bakin kofa tazo ta tsaya amma bata bude ba tana jiyo takunsa har ya iso suna magana da Attahir yana kara yi masa godiya. Kofar taji ya kama tayi saurin bude masa haka kawai gabanta yake bugawa kamar ta dade bata ganshi ba. Ga kunyar kayan jikinta.
Labule ta daga masa tana tsaye daga gefe ya kura mata ido kamar yau ya fara ganinta. Idanunsa na kanta har ya isa kan kujera ya zauna ya ajiye sandunansa a gefe.
"Taho taho kada ki sani suman zaune" yace yana miko mata hannu.
A kunyace ta karasa kusa dashi ta zauna ya janyota barin jikinsa ya rungume. Yana ji ta saka hannuwanta ta zagaye shi itama tana kara makalewa jikinsa.
Shakar kamshinta yake mai ratsa zuciyarsa "I miss you Matar Dahiru"
"Awa ta nawa da baroka a asibiti?"
"Kenan bakiyi kewata ba ko"
"Maida wukar Mijin Mawadda"
Ya dago habarta "to kinyi?"
"Fiye da zatonka" tayi masa murmushi.
Tashi yayi ya sakala hannu a kafadarta ta kaishi daki. Duk wani motsinta akan idonsa yana binta da kallo. Jikinta kadai ya isa ya ruda mutum.
"Zaki yi min wankan"
"Nifa bana son shagwaba ka warke. Tun ciwon na sabo banyi maka ba sai yau saboda rigima"
Langabe kansa yayi "ni ko?"
"Rigimarka tayi yawa Yayanmu. A asibiti...."
"Can ma don kada kisa a kama mu ne na hakura"
Ita kam gaskiya tana jin kunyar wannan abu amma ya ta iya. Sai wani nanikarta yake ya kwanta akan cinyarta yana mita.
"Kwalliyata zata baci kafin ka gama gani" tace a sanyaye saboda rashin mafita.
"Zanyi miki kuka irin wanda sai Attahir ya hawo a guje"
Tashi tayi ba shiri ta hada masa ruwan sannan tazo ta ja hannunsa tana kumburi don ba haka taso ba. Wani fitinannen murmushin ya rinka yi mata tana shiga ya tura kofar da hannu. Da kayan jikinsu ya sakar musu shawa a ka suka jike. Kamar ta saka masa kuka
"Yayanmu!"
Zagayeta yayi da hannu yana dora kansa a kafadarta "kinga tsoron zamewa nake shiyasa na rikeki. Ai banyi laifi ba ko"
"Baka yi ba" tace don ta riga ta sallama tasan bata da wata mafita kuma. Da kanta ta matsa jikinsa tana hade bakinsu.
********
Kotu ta cika makil duk yawan fankoki zafi ake yi saboda jama'a. Dangin Mawadda, na Dahiru, Baba Prof, Dr Tani da kuma uwar gayya Haj Mara su ne daga gaba gaba.
Alkalin wannan karon mace ce wadda tayi fice a cikin Nigeria saboda rashin ramgwamenta akan duk wata shari'a da ta shafi fyade. Justice Raliya Habu kenan matar da kudi ko son zuciya har yanzu bai sa an taba kamata da laifin tauyewa wani hakki ba sai dai idan lauyoyin ne suka gaza. Gilashinta ta turi kan hanci ta bukaci lauyoyi su gabatar da kawunansu.
"Sunana Barrister Jibril Jibril nine lauyan masu kara"
"Barrister Wisdom Odili lauyan wadanda ake kara"
Justice Raliya ta basu damar fara gabatar da hujjoji da shaidu. Wannan karon shari'ar bata yi kama da zata bada wahala ba saboda yawan shaidu da suke a hannu. An shigo da BB ya rame ya kwanjale babu kyaun gani. Haj Mara tamkar wadda cutar tsotsewar jini ta kamata duk shekarunta sun fito karara babu kyaun gani.
Bisa aiki na kwarewa da JJ ya nuna yayi nasarar nemo likitan da ya duba Mawadda a asibitin Bebeji. Haka nan kuma ya samo Inspector Nalado wanda suka samo hotunan raunukanta tun na farko.
Dr Tani tazo ta fadi duk abinda tayi a wancan zaman shekarun baya sannan Qareeba da Dahiru suka bada shaida akan abinda ya sameta itama.
Zugar su Garwashi kaf sun nuna solidarity domin kuwa sun bada tasu shaidar har zuwa yadda suka taimaka aka gano Mawadda bayan sun saceta.
Barrister Wisdom dena yi musu tambayoyi yayi saboda babu amfanin yin hakan. Haka aka gabatar da Bobo shima ya tabbatar da kade Dahiru da suka yi wanda yazo da sanduna.
Jama'a cikin kotun sunyi tir da halin akuyanci irin na BB da uwarsa mai taya bera bari. Alkalin ta dage shari'ar zuwa kwana shida ranar da zasu dawo a yanke hukunci.
******
Yau kotun har tafi zaman farko cika saboda 'yan jarida har daga gwamnatin tarayya. Case ne babba da yake ciwa mutane tuwo a kwarya.
Bayan gama sauraron bayanai Justice Raliya Habu ta soma magana kamar haka.
"Duba da hujjoji da shaidun da lauyoyi suka gabatar wannan kotu mai alfarma ta yanke hukunci kamar haka."
Shiru kotun tayi baka jin ko da tari an baza kunnuwa.
"Kotu ta karbe lasisin aikin Dr Tani daga yau bazata sake aiki a matsayin likita a kasar nan ba saboda tayi amfani da damarta wurin bada shaidar karya da cutar da mai gaskiya."
Dr Tani sunkuyar da kanta tayi dama ta dade da zaton hakan.
"Hussaini Joji wanda aka fi sani da Bobo kotu ta yanke masa hukuncim shekara biyu saboda taimakawa wurin sace matar aure, fitar da mai laifi daga hannun yan sanda da kuma bada gudunmawa ta yunkurin kisa"
Gigicewa Bobo yayi don bai taba shiga hannun hukuma ba duk tsiyarsa.
"Haj Marakisiyya kotu ta ci ki tarar naira miliyan biyu da zaki bawa Mawadda Fatihu saboda danne mata hakki, bacin suna da taimakawa wurin cutar da ita. Har ila yau zakiyi zaman gidan yari na wata shida saboda fitar da mai laifi daga hannun hukuma"
Kukan ma tuni ta dena saboda dacin zuciya da bacin rai. Ta rasa komai ta rasa kowa saboda Babawo.
"Babawo Sule Chanji. Duba da irin laifukanka wannan kotu ta yanke maka daurin shekara ashirin da biyar tare da horo mai tsanani"
Murna da farinciki a wurin su Mawadda baa cewa komai. Dahiru ji yayi kamar ya taso yaje ya rungumeta don kukan farinciki take yi.
Garwashi da yaransa Alkali tayi musu gargadi akan daba ta kuma basu shawarar su nemi sana'ar da zata rikesu bata fatan sake ganinsu a kotunta indai ba alkhairi bane ya kawosu.
BB yana ta hargagin sai ya kashe Dahiru ya auri Mawadda aka fitar dashi sannan aka sallami kotun bayan Alkali ta tashi.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰27
*Batul Mamman*💖
Daga kotun gidan Mal Fatihu suka wuce gabadayansu. Dr Tani kafin su tafi da nata iyalin ta rike hannun Mawadda ta sake rokonta gafara. Babu bata lokaci tace ta yafe.
Garwashi yazo tare da yaransa. Loba boy dai yaji dadi an kulle Danmani shima ya sami rabon wata shida. Dahiru da Attahir suka jasu gefe suka basu sati daya kowa yayi shawarar me zaiyi amma kafin nan duk su koma gaban iyayensu su nemi gafararsu. Da farinciki suka tafi bayan Mawadda da kowa ya sake yi musu godiya.
Suna isa gidan abincin sadaka da aka dafa tun safe aka shigar fitarwa lodi lodi ana kaiwa asibitoci domin godiya ga Allah. Gidan ya cika da hayaniya tamkar ana biki. Dahiru ya turawa Mawadda text don yaji shiru ko nemansa bata yi.
_(yau fa akwai celebration kiyi ki gama mu tafi da wuri)_
Murmushi tayi Nawal ta zungureta.
"Ade na kallonki dai hajiyar soyayya"
Tana dagowa suka hada ido da Ade kuwa ta rufe ido tana dariya. Sai dare suka bar gidan bayan doguwar nasiha daga Baba da kuma karin godiya ga Dahiru.
A wannan rana da hankulansu suke a kwance Dahiru da Mawadda sunyi kwanan farinciki da dimbin soyayya. Basa ji basa ganin kowa sai junansu.
Bayan kwana biyu suka wuce Tariwa harda su Baba gabadaya. Gabanta har faduwa ya rinka yi akan hanya saboda yadda take ji. Yara da manya tun a hanya suka yiwa motocin dafifi aka rakasu har kofar gidan Maigari dattijon arziki irin albarka.
Shima fitowa yayi yana zaune jamaa sun zagaye shi ta kowane bangare yayi musu nasiha da jankunne akan rayuwa. Mawadda da take sanye da kaya na alfarma kana ganinta kasan ta wuce sa'a ya nuna musu tare da tunatar dasu babban abinda ya kamata a hadu a yiwa mutane irinta wato tsayawa juna da kuma tausasawa.
Ita da su Yaya sun sha kuka mata suka yi ta rumgumarsu ana murna. Satinsu guda a garin suna zaga 'yan uwa sannan suka koma gida.
*****
Sati uku kenan da gama shari'arsu BB aka kira Dahiru da Mawadda kotu domin karbar kudin tarar da aka yankewa Haj Mara.
Alh Sule suka gani ya bada cheque na miliyan biyar. Dahiru ya duba da kyau yace ba haka Alkali tace ba.
Nannauyan numfashi Alh Sule ya saukar "na sani kuma kudin da na kara ba fansar mutumcin Mawadda bane da dana ya tozarta. Na bata ne domin tun shekarun baya naso haduwa da ita Allah bai nufa ba. Allah Ya gani ban goyi bayan abinda akayi miki ba amma bansan inda zan same ki ba. Wannan kudin duka harda na Marakisiyya ne. Shine abu na karshe da zan iya yi mata don nasan ko wuka zaa saka mata yanzu bata da inda zata fitar da wannan kudin. Idan da hali ko don rage nauyi da hakki kuji tausayina don Allah ku yafewa Babawo. Nasan zaku ce wannan tsoho da son kai yake. Sai dai kaddara idan ta hadu da son zuciya rayuwar mutum sai ta lalace. Babawo bashi da sauran gata sai yafiyarku a gareshi"
Fuskar kamala da dattako ta Alh Sule Chanji ita ta sanya Dahiru ya dubi Mawadda.
"Idan har na isa...."
"Ka isa Yayanmu" ta katse shi "Na yafe masa Alhaji"
Bata kara cewa komai ba bayan wannan ta fita daga wurin ta nufi motarsu. Dahiru ne ya karasa komai yazo ya sameta jingine da motar tana tunani. A gefenta ya tsaya.
"Kinsan me na tuna?"
Ta juyo ta kalle shi "me?"
"Ranar da na fara sake ganinki. Wallahi da kika fito ba karamar dauriya da jarumta nayi wurin kin fitowa na rungumeki ba. You looked so sweet lokacin"
"Yanzu fa?" Ta tsare shi da ido.
"Mawadda ce Dahiru, Dahiru kuma Mawadda..."
Kallon fuskarsa tayi suka hada ido a hankali tace "I love you"
Bude mata kofa yayi ta zauna ya rufe sannan ya zagaya ya zauna shima. Hannunta ya kamo ya sarke yatsunsu yana kallon yadda nata suka yi kyau sun sha jan lalle.
"Ina rokon Allah Ya kara min sonki da kaunarki kuma Ya bani ikon kulawa dake har karshen rayuwarmu."
Kwalla ce ta cika mata ido yana gani hawayen ya soma diga duk ya rude.
"Na bata miki rai ne?"
Ta girgiza kai da sauri sannan ta kwantar da kanta a jikin kujera soyayyar Dahiru tana sake cika mata zuciya. Har tunani take yi me zata yi domin faranta zuciyarsa. Kallonsa tayi idanunta kamar tana shirin bacci.
"Ka kaini gida kada nayi abin kunya a gefen titi"
Jin haka ya ware idanunsa a kanta "abin kunya kuma?"
A kagauce ta kalle shi "mu tafi mana da gaske nake"
Tayar da motar yayi suna tafiya yana kallonta yana tsoron me zata yi. Suna zuwa gida ta fice ta barshi a tsaye da rikon baki.
Da saurinsa ya bita suka ci karo a bakin kofa ta cire mayafi da dankwali ga wani zanin a hannunta.
"Ina zuwa?"
Haki take yi saboda gudun da tayi na hawa saman ta durkusa a gabansa ta juya baya.
"Hau"
"Ina?"
"Goyaka zanyi Mijin Mawadda na kaika daki sai nayi abinda ba na kunya ba yanzu tunda mun dawo gida"
Sai da ya gama dariya ya ga ta sha kunu ita da gaske take.
"A wannan dan bayan? Na kagu dai naga abin kunyar nima na koya" ya dora hannunsa a tsakiya.
Murya na rawa tace "Na rasa me zanyi maka a duniya kasan cewa nagode da duka abubuwan da kake yi min."
Tayar da ita yayi ta soma kuka ya rungumeta.
"Abu daya zaki yi min"
Ta dago kai da sauri "me kake so?"
"Mu zamewa juna komai na rayuwa. Abokai, 'yan uwa, masoya da duk wani abu da kika san yana kara shakuwa. Banyi miki komai don kice kin gode ba. Allah ne Ya saka ki a nan" ya dora hannunta a saitin zuciyarsa.
Ga ido fal hawaye ta soma murmushi kuma kunyarsa tana saukar mata. Matseta yayi a jikinsa ya soma shagwabar da ta riga ta sallama masa "zaki goyani din muje ki nuna min abin da kika ce?"
Ta zille "a wane bayan?"
"Irin yadda muka yi a asibiti zaki yi min kinji Mawadda mana"
"Ya na iya tunda ka iya dadin baki"
Dakin suka shige suna yiwa juna dariya yana cewa sai tayi abinda ta fada tana cewa ta fasa.
*******
Abu kamar wasa bikin Qareeba da Bilya saura sati biyu. Dama wata uku aka saka gashi lokaci ya gabato. Dr Tani da mijinta harma da 'yan uwan Qareeba maza kowa ya nuna bajinta ajin farko. Sun kashe kudi sosai wurin kawata gidan da Bilya ya kama mata babu nisa da su Dahiru.
Bisa shawarar Nawal da amincewar