Showing 60001 words to 63000 words out of 110071 words

Chapter 21 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

1917

durkusa cikin yanayi mai ban tausayi
"Baba idan akan su Baffa ne tun sati biyu da suka wuce suka so zuwa sai ciwon sugan Inna ya tashi. Zasu zo gidan nan kuyi magana don Allah Baba kayi hakuri ko yaya take zan iya zama da ita"

Mal Fatihu yaji tausayinsa amma yana hango ko anyi auren to da wuya su sami rayuwa irin ta sauran ma'aurata. Idan hakane kuwa bai yiwa Dahiru adalci ba don yasan yau da gobe sai Allah.
[08/01 8:32 pm] Biebie: *GUMIN HALAK...*💰17

*Batul Mamman*💖



BB ne akan ruwan cikin Qareeba ya matse mata hannuwa babu sutura a jikinsa kamar a dakinsa. Da zafin nama Dahiru ya fizgo shi ya kai masa naushi. Qareeba na ganin ya dagata ta mirgina gefe tana wani irin kuka. Minti guda da sun kara basu shigo ba da BB ya kafa mata tarihin fyade itama. Yaci mutumcinta karshe tamkar wani dabba. Kayanta da hannu ya tsarge su bayan ya gama dukanta. Dahiru ko kallonta baiyi ba ya haye kan BB dukansa yake iya karfinsa.

A daidai wannan lokacin babu abinda yake hangowa sai Mawaddansa da ta taba riskar kanta cikin yanayi irin wannan. Hakan ya kara masa kaimi ya jibgi BB iya karfinsa don ko motsin kirki ya gagare shi.

Kukan Qareeba ya dawowa da Dahiru hayyacinsa yaji tana kiran Mummy. Juyawa yayi Dr. Tani tamkar gawa a kwance. Sai da ya karawa BB duka a ciki da kafarsa sannan ya tsallake shi ya koma kanta. Dagata yayi amma duk da haka ya runtse idanunsa daga kallon Qareeba yace

"Zaki iya saukowa?"

"Eh"

"Ki rufe jikinki ki sauko muje asibiti ina jin suma tayi."

Wani zumbulelen hijab na sallar Dr Tani ta zura ta biyo bayanshi tana tafiya da kyar ga jini yana diga a kasa. Ashe glass ne ya soketa daga jug din da ta fada a kai wahala tasa bata sani ba.

Da gudu gudu Dahiru ya fita yana kwalawa maigadi kira. Shima a guje ya taho ganin Dr Tani a kafadar Dahiru yana son bude bayan motarsa ya sakata amma hannunsa sai rawa yake yi.

Maigadi ya bude masa yana tambayar me yake faruwa sai ga Qareeba ta taho fuska ta soma kumbura lebe da hanci duk jini. Gaban motar Dahiru ya bude mata ta zauna sannan ya kalli Maigadin.

"Akwai mutum a dakin Hajiya sannan ka kira maigidan nan..."
Lekawa yayi ta taga yace da Qareeba "zaki iya gane asibitin Hajiya?"

Ta amsa masa yace da maigadin ya fadawa maigidan ya samesu a can sannan ya shiga ya tada mota.

Qareeba sai kuka take yi tana kiran Dr Tani wadda har yanzu bata motsi. Dahiru ko danja baya tsayawa saboda tashin hankali balle da ya ga Qareeba ta rike kirji tana tari jini na fita. Da taimakon Allah ya isa asibitin. Ya fita ya kira wani da ya ga kamar likita ne yace masa Dr Tani da 'yarta ya kawo. Ana jin sunanta mutane suka yo kansa aka dauko su.

Tambayarsa ake me ya faru duk ya gigice tsabar tashin hankali. Yafi so Dr Auwal yazo sai ya fara fada masa. Kusan minti shabiyar yana kai kawo a korido din dakunan da aka shigar dasu kafin wata likita mace ta fito ya tambayeta yaya ake ciki.

"Qareeba taji ciwuka a jikinta amma munyi nasarar cire gilasan da suka farfasa mata jiki. Sai kuma buguwa da su fashewar baki wanda zata sami saukinsu a hankali. Babbar matsalar dai bata wuce cikinta da aka taka...mtsw ko waye wannan dabba ta fishi hankali."

Cike da damuwa yace "yanzu dai zata tashi ko kuwa?"

Kallon ido cikin ido tayi masa "zata tashi amma yanzu haka theatre zamu shiga da ita"

"Ki ka ce kuma da sauki?"

"Akwai internal bleeding a cikinta tana bukatar surgery yanzun nan"

Tafiya tayi ta barshi nan a tsaye cikin rudani. Zai shiga dakin da Qareeban take likitan dake tare da Dr Tani ya fito. Yace ta farfado amma jininta yayi mugun hawa. Suna wurin Dr Auwal da su Najib suka karaso. Dukkansu Dahiru suke kallo suna tambayarsa me ya faru.

Dakin da Dr Tani take ya nuna musu su ka shiga duka. Tashi tayi tana kukan ina Qareeba aka ce ta kwanta aiki za'ayi mata yanzu. Hankalinta ya sake tashi ta fara wani abu kamar mai farfadiya dole nurse tace su fita aka sake taruwa a kanta.

A wajen dakin Dahiru ya sanar dasu abinda ya gani. Dr Auwal yayi baya saura kadan ya fadi yana salati Safwan ya rike shi. Faisal ne yace basu ga ta zama ba ya kira Maigadi akan ya rufe gidan zasu zo da 'yan sanda ya fada masa ai mutumin ya gudu. Yaso tare shi yayi kansa da mota dole ya bashi hanya.

"Zancen da nake maka yallabai ya balle kofar gate din" ya karasa da tambayar ya masu jiki.

Kowa cikin damuwa yake likitoci biyu da nurses suna ta shige da fice a tsakanin dakunan har aka fiddo Qareeba wadda fuskarta ta gama hadewa don kumburi zuwa dakin theatre. Zama suka yi jigum har aka fito da ita bayan awa daya.

Ranar sun ga tashin hankali mara misaltuwa. Dr Tani sai allurar bacci aka yi mata saboda jininta yaki sauka kuma ta sawa kanta damuwa da rashin ganin Qareeba. Awa uku Dahiru yayi a asibitin sai da ya fuskanci kamar komai ya daidaita ya fito da alkawarin zai koma washegari.
*****

Bakin motarsa yaje amma jikinsa sai rawa yake yi da kyar ya shiga ya bar asibitin.

Tuki ya rinka yi sai ganin kansa yayi a layin su Mawadda. Ita kadai yake bukatar gani a lokacin a yadda hoton BB da Qareeba suka zauna a kansa. Tunda yake bai taba ganin masifa irin wannan ba. Karin tausayin Mawadda ne ya mamaye zuciyarsa da babu wanda ya kai mata dauki kamar Qareeba har aka rabata da mutumcinta.


Takwas na dare ta dan gota ya kirata. Tana dauka muryarsa gabadaya ta canja yace "don Allah ki fito ina waje"

Tashi tayi zaune ba shiri saboda yanayin da ta ji muryarsa kuma ya katse kiran. Kwakwalwarta ce ta shiga tunanin ko lafiya ta dai saka hijab ta sanar da Yaya yazo ta fita.

A zatonta yana kofar gidan sai ta hango motarsa a inda yake ajiyewa karkashin wata bishiyar darbejiya a kunne. Tasan ba haka suka saba ba ciki yake shigowa amma dai bari taje ta gani.

Kansa ta gani ya kwantar akan sitiyari saboda ya sauke glass din tayi sallama. Yana dago kai gabanta ya fadi. Tashin hankali da damuwa ne karara a tattare dashi.

Kallonta yayi yace "ki koma ciki dare yayi."

"Bangane in koma ciki ba daga fitowa ta" tace tana kara matsowa jikin motar.

"Tafiya zanyi kinga dare yayi. Dama ganinki kawai nake son yi"

Giya ta ga ya saka zai tafi ta zagaya daya bangaren da sauri tayi sa'a a bude motar take kawai ta shige.

Bata san irin dauriyar da yake yi ba a wannan lokacin. Yadda jikinsa yake babu kwari haka zuciyarsa tayi rauni sosai. A sanyaye yace
"Meye hakan?"

Ta riga ta san akwai matsala har ta soma kwalla tace "kai zan tambaya, ka fada min ko ma mene ne don Allah"

Jikinsa ta kula rawa yake yi ya hade hannuwansa a kokarinsa na boye mata. Tsoro ne kawai ya sake kamata ta soma kuka.

"Yayanmu kana ganin ban cancanci sanin damuwarka bane?"

Ba niyarsa yasata kuka ba. Hasali ma zuwa yayi don a tunaninsa ganinta ne kadai a wannan lokacin zai kwantar masa da hankali. Sai dai abin ba haka yazo ba. Ji yayi ya tsani kansa a baya da ya kasa gama tanadin aurensu har aka tura ta aikatau.

Runtse idanu yayi "ki koma ciki kada wani ya ganki a motar nan Baba bazai ji dadi ba"

"Wallahi bazan fita ba sai ka fada min ko kazo mu shiga ciki" tace tana hade rai.

Ya dago kai ya kalleta ta sake daure fuska.

"Naji fito muje".

Sai da ya fita sannan itama ta fito suka shiga ciki gabanta yana ta faduwa bata san me zai ce mata ba.

Sun zauna akan kujeru suna fuskantar juna duk ta kosa taji me zai ce.

"Ki yi hakuri da rayuwarki ta baya Mawadda, kiyi hakuri da talauci yasaki fita neman halak, kiyi hakuri da yadda talauci yasa aka danne miki hakkinki a kotu. Mawaddatan wa Rahma! Kiyi hakuri ni Dahiru banyi komai domin taimaka miki ba a wancan lokacin. Idan mutumin nan yana da rai ina fata Allah Ya hadani dashi ko sau daya ne...." muryarsa ce ta karye alamun yana boye kuka.

Maganganunsa da yanayinsa suka sake daga mata hankali. Yana magana tana hawaye zuciyarta tana tuna mata da kuncin da take ta kokarin mantawa. A tsorace tace "ka fasa aurena ko?"

Girgiza kai yayi "nan da kwana tara zaki zama mallakina in sha Allahu"

"Ka tayar min da hankali ka fada min abinda yake damunka mana. Me ya kawo wadannan maganganu?"

Da ace an daura aurensa da ita babu abinda zai hana shi rungumeta a wannan lokacin. Abinda yake zuciyarsa ya fada mata "Rarrashi nazo nema a wurinki Mawadda. Naso ace kin zama matata zaki iya rungumeni ki kwantar min da hankali. Ki rikeni kice komai mai wucewa ne. I need you a matsayin mata ba budurwa ba saboda a yau zuciyata ta hadu da mummunan tabo. Sai yau na gama fahimtarki da rayuwar da kika yi kina jinyar jikinki da zuciyarki"

Gabadaya ta tsinke da lamarinsa ya kara dagula mata lissafi. Tashi tayi zata fita yace ina zata je.

"Baba zan kira, na gaji da wannan juya maganar taka ka ki fahimtar dani yadda zan gane." Durkusawa tayi a kasa hawaye wani na bin wani a kumatunta "zan rarrasheka amma sai na san mene ne matsalar"

Bashi da zabi da ya wuce sanar da ita abin da ya sami Qareeba saboda baya so ta koma cikin gida kowa ya gane tayi kuka. Sai dai kafin ya gama labarin Mawadda tayi kuka har ta godewa Allah. Shima dauriya ce da rashin son nuna gazawarsa a gabanta tasa ya rike nasa hawayen.

"Ban taba ganin dabbanci irin wannan ba. Ba kasarmu ba duniya gabadaya tayi sake wurin karuwar fyade yanzu ya wuce kan 'yan mata harda yara kanana. Ke da ki ka taba fuskantar wannan abin zaki fini fahimtar halin da Anti Qareeba take ciki."

Kanta kawai take iya kadawa ta kasa cewa komai.

"Bakincikina ba akanta kawai ya tsaya ba. Ina tausayin duk wata mace babba ko karama, budurwa ko me aure da marasa imani cikinmu suke tozartawa ta hanyar yi musu fyade. Ina takaici idan na tuna ranar da hakan ta sameki karshenta bacci nake yi ko cin abinci. I was not there for you Mawadda ba haka naso ba."

"Ba laifinka bane"

Kallonta yayi fuska ta jike da hawaye "ni da nazo ki rarrasheni shine zaki barni da rarrashinki. Ki tashi ki zauna naji dadi ina da ke da zan fadawa damuwata. Kaina da zuciyata duka suka kulle na kasa tunani dazu"

Sun cigaba da hira akan wannan mummunar ta'asa da ta addabi al'ummar kasarmu. Taji tausayin Qareeba sosai balle da taji itama tasha duka kusan irin nata.

"Uhmm Yayanmu ita yayi mata dinne ko dukan ne kawai?"

"Bani da tabbas sai gobe idan naje zanji. Kinga da an daura aurenmu tare zamu je"

"Yanzu ma zanyi mata addu'ar samun lafiya domin wannan tabon da wuya yake warkewa duka zahiri da badini. Ka ga har yanzu ina da tabon belt a jikina guda daya yaki bacewa" tace a hankali.

Dahiru ya dubeta soyayyarta na kara samun gurbi a zuciyarsa.
"Ki tuna min ranar da aka kawo min ke wannan tabon zan fara nema a jikinki nayi kissing"

Tashi Mawadda tayi cikin matsananciyar kunya ta diririce tana neman hanyar fita tace "na shigesu"

Dahiru shima ya tashi "ba ke kadai ba nima na shiga." Ya fada yana dukan bakinsa harda yi wa bakin fada.

Ya rigata kaiwa bakin kofa "kinga ni nayi nan ki tabbata kin manta wannan maganar kinji ko."

Da hannu biyu kamar tana korarsa ta rinka nuna masa kofa "jeka ni dai sai da safe"

Takalmansa ya zura ya juyo yana mata murmushi "nace ba...."

Shan kunu tayi kada ya kawo wasa sai dai kana ganinta kasan dauriya tayi don ba karamar kunya take ji ba ganinsa ma da take a wurin "kace me?"

"Zan iya kiranki kafin na kwanta?"

"Na yafe Yayanmu don Allah ka tafi"

Gira daya ya daga yana murmushi "kin tabbata?"

"Eh, eh na tabbata"

"Da gaske zaki iya bacci batare da nace miki sai da safe ba Mawadda?"

Tunda suke bata taba jin tana so ya tafi irin na yau ba. Kuma sai wani jan zance yake yana kara sakata jin kunya.

"Wayyo Yayanmu kaje duka na yafe."

Dariya yayi ya tafi ta sauke ajiyar zuciya tana rike kirjinta da yake bugawa da karfi.

Ta taho zata fita kawai ya sake dawowa ciki idanunsa karaf cikin nata tayi kasa da kanta da sauri.

"Kina sona Mawadda?" Ya fada da wata irin murya a tausashe.

"Wai baza ka tafi ba?"

"Sai kin bani amsa ko na dawo ciki mu zauna naga daren da sauransa"

"Ka fa san amsar"

"Ban taba ji kin fada bane shiyasa yanzu naji ina kokonto"

Idanu ta ware tana ganin me zai sa shi wannan tunanin. So take ya tafi kuma saboda har yanzu maganarsa ta dazu tana mata yawo a kanta
"Ina yi"

Sake matsowa yayi ta ja baya "kina me?"

Cije lebe tayi ya lumshe idanunsa. Baya so tana wannan abin a yanzu dai da suke da katanga tsakaninsu.

Sai da taja numfashi sannan tace "Yayanmu Dahiru ina sonka amma don Allah ka tafi kafin nasa maka ihu"

"Nima ina sonki Mawaddatan wa Rahma, sai da safe"

Sake fita yayi tayi murmushi tana juyi "oh Allah Ka bani Yayanmu Dahiru"

Bata san ta ina ya sake bullowa ba sai ganinsa tayi a bakin kofar yace "Amin Ya Rabbi"

Ihu kawai tasa masa kunyar tayi mata yawa "Ahhhhh"

Yana jin haka ya fice da sauri yana dariya. Toshe bakinta tayi tana fatan babu wanda yaji daga ciki.

*****

A can asibiti an yiwa Qareeba aiki lafiya. Dr Tani kam basu da zabin da ya wuce sedating dinta wato aka sata baccin dole saboda suna so lokacin da zata farka ta ga Qareeba ma ta tashi. Me yiwu wa hakan zai taimaka wurin daidaituwar jinin nata.

Daki daya aka ajiye su zuwa wayewar gari. Dr Auwal sai shabiyun dare ya koma gida. Falon da abin ya afku wanda a waya ya sanar da Maigadi a fadawa maiaikinsu kada ta taba komai da sunan gyara yaje hankalinsa ya tashi haka ya hau sama yana ganin jinin 'yarsa a kasa. Daki gabadaya ya hargitse musamman da yake a nan Dahiru ya yiwa BB duka. Kansa yaji ya soma ciwo ya bar wurin.

Su Najib, matansu da Dr Auwal da sassafe suka koma asibitin. Sun sami Dr Tani tana ta bada order ayi kaza a dauko mata kaza tana tsaye akan Qareeba. Likitocin da nurses sai rokonta suke yi akan ta koma nata gadon ta kwanta zasu kula da Qareeba amma ta ki. Sai ma fada da take yiwa kowa.

"In koma in kwanta ku karasa min yarinya?"

Maigidanta da ta gani ne ta sa kuka murya a shake tace "Daddy ka ga Qareeba taki farkawa tun jiya"

Tausayi ta bashi matuka yasan yadda take bala'in son Qareeba duk cikin 'ya'yanta.
"Zo muje wani dakin ki basu wuri su yi aikinsu. Za ta tashi in sha Allah"

Sai da yayi da gaske ta biyo shi zuwa wani dakin sauran suka tsatstsaya a waje suna jiran bayani game da halin da take ciki. An dade ana bincike har ta fara wata irin jijjiga akan gadon. Can dai aka sake yi mata scanning abin mamaki wani dan karamin gilas ne cikin wanda su ka suke ta ya shige jikinta ya taba kodarta daya. Dole sai an sake yi mata wani aikin. Su Safwan da girmansu su ka rinka kuka yayin da wata nurse take musu bayanin hakan yana faruwa sosai. Aji ciwo da glass ko karfe idan ya karye a jiki yawo yake yi. Zai iya bin duk inda yaso idan anyi rashin sa'a ya taba mahimman sassa ya jiwa mutum mugun rauni.

Dr Tani dagewa tayi ita zata yi aikin tana ta kuka kamar ranta zai fita. Wani azababben ciwon kai ne ya bugeta lokaci guda sai jiri ta fadi a kasa. Gado aka mayar da ita mai yin aikin ya tafi da Qareeba yayin da wasu suka tsaya a kanta.

Iyalan gidan Dr Auwal sun ga abin da basu taba gani ba a wannan rana. Anyi aiki lafiya kafin azahar an fito da ita.

Suna tsaye a kanta ta bude idonta mai lafiyar a hankali tare da motsa hannunta da yake cikin na Dr Tani.

Tana hawaye ta sake riketa tace "Qareeba kalle ni nan, kin gane ni? Mummynki ce"

Baki da ido daya sun suntume da kyar ta iya motsa shi tace "Mummy"

Mahaifinta da 'yan uwa ta rinka bi da ido daya bayan daya tana hawaye. Ina suke lokacin da take ta kiransu da neman agaji. Hannu ta daga ta yafito Dr Auwal ya duka daidai bakinta da kyar tace "Babawo"

Idanunsa sunyi ja sosai yace "na sani Qareeban Daddy bazan barshi ba. Warkewarki kawai nake da bukata"

Dr Tani na kuka tace ina wayarta. Maigidanta ya miko mata tace da su Safwan duk su fita zata yi waya. Kallon juna suka shiga yi kafin su bi umarninta.

Suna fita ta kira Haj Mara. Ringing biyu kamar tana jira ta dauka a lokacin kuma babban wan Dr Tani ya shigo dakin bata da damar katse kiran tunda ya shiga kuma a zuciye take.

Haj Mara kusan kwana tayi tana kiranta dama harda Qareeba babu wanda ya dauka.

"Haba Tani, haba don Allah. Kun daga min hankali ina ta nemanki tun jiya inji ina Babawo yake daga cewa...."

Daga murya Dr Tani tayi irin yadda wani bai taba ji ba cike da masifa tace "dakata min Marakisiyya. Babawon banza, ashe dan naki dan akuya ne dabba mara hankali... "

Gabanta ne ya fadi ba dai yaje ya tafka wata ta'asar ba. Sai kuma bacin rai don bazata taba yin shiru ana zagar mata da ba.

"Tani kinsan da wa ki ke magana kuwa?"

Cikin fada tace "Wacece ke banda macuciya azzaluma. Ni zaki ha'inta ki turo min wannan mahaukacin ya auri Qareeba. To ki saurareni na rantse miki sai naga bayanki da na Babawo"

"Wai meye haka? Me yayi miki?"

"Ashe iskancin nasa na karya ne tunda bai dawo gida ya fada miki ba. Muna asibiti daga jiya zuwa yau anyiwa Qareeba surgery har biyu kinji daya. Yayi mata dukan da ko a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login