Showing 15001 words to 18000 words out of 110071 words

Chapter 6 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

183

suka fara fita waje kowacce tana son kaiwa makusanciyarta labari.

Cikin abin da bai wuce awa biyu ba maganar nan tayi yawo fiye da zato. Mata da maza manya da yara da dama sun sani tunda safiya ce. Kusan ko ina zancen ake ta yi gashi a kowacce gaba labarin ya sami karin gishiri ya tashi daga fyade wasu sun kara da ciki wasu ma sun ce haihuwa tayi. Akwai wadanda suka dora da cewa dama tun tana garin ai kallonta kawai suke yi ana cewa tana da nutsuwa su kuwa sun san tana yawace-yawacenta ne kawai. Lokacin da Dahiru ya dawo ana ta binsa da kallo da yake bai kawo za'aji zancen ba ko kadan bai kula ba.

******

Ya fito da shirin tafiya gona saboda rashin samun lokaci tun ranar da Mawadda ta dawo gari bai gama cire kubewar da ya shuka ba wanda kusan duka gonar sun gama yado mai kyau. Idan ya cire Yayansa Bilya ne yake diba akwai masu kayan miya da suke karba a Kano. Sauran kuma Inna da Ummiyo suyi aikin busarwa da dakawa akai a sayar.

Sallama suka jiyo daga waje Inna ta amsa tace ana zuwa. Ummiyo ta shiga wanka bayan ta dawo ta sha fadan Inna. Danlami dama shi ba'a saka shi a lissafi dama.

Da fatanyarsa a kafada Dahiru ya fita. Sakin fuska yayi ganin wani abokinsa Ali.

Hankali a tashe Ali yace "Dahiru ashe kuma abin da ya faru kenan. Ina shirin fita wata makociyarmu ta shigo take sanar da Fiddausi saboda ta san kawaye ne da Mawadda. Yanzu haka na fito na barta tana ta kuka."

Gaban Dahiru ya fadi da kyar ya iya cewa "me aka ce ya same ta?"

Sai kuma jikin Ali yayi sanyi a tunaninsa Dahiru bai sani ba
"To ina jin dai a gida basu sanar da kai ba saboda ansan za ka shiga damuwa. Mu bar zancen nan bari na wuce"

Tunani Dahiru ya soma na inda maganar ta fito kuma mutane nawa ne suka ji.

"Ali dakata mana ba ka fada min me kaji ba"

A dan tsorace Ali yace "ba a ji mutuwar sarki a bakina ba. Nasan su Baffa zasu sanar da kai. Sauri nake Dahiru sai mun hadu"

Bai jira cewarsa ba ya bar kofar gidan a gaggauce. Shi kuwa Dahiru sosai hankalinsa ya tashi. Balle da ya hango kanwar Inna wadda suke kira Yakumbo tana nufo gidan da sauri ita da babban danta Liti.

Tare suka shiga gidan bayan ya gaisheta tana binsa da kallon tausayawa. Sun gaisa da Inna ta dan bata rai.

"Yanzu saboda Allah magana irin wannan sai dai naji a waje? Ba don Liti ya fita siyo siga ba wani yayi masa jaje shikenan..."

Inna ta dakatar da ita itama nata gaban na faduwa "wace maganar?"

Yakumbo ta sake kallon Dahiru "zancen Mawadda mana ance anyi mata fyade wai harda ciki suna asibiti an zubar ne ko zata haihu ni ban ma gama gane zancen ba na fito"

Tafa hannuwa Inna ta soma tana sallallami "wane munafukin ne ya fito da maganar nan harda karya? Nasan dai su Haule bazasu dauki wuka su dabawa cikinsu ba. Sa'ade kuwa har dakina ta biyoni jiya tana rokon rufin asiri"

Yakumbo ta gyara zamanta "kice maganar dai gaskiya ne. Mu dai mun shiga uku duka-duka yaushe aka yiwa 'yar gidan Audu maikifi gashi zaman garin nan yazo ya gagaresu."

Inna dai har zufa ta soma yi saboda tashin hankali. Dahiru ya sami jikin bango ya jingina ransa na tafarfasa. Ummiyo tana fitowa da bokitin wanka a hannu taji Liti yana karin bayani.

"Wanda ya fada min yace wai a bakin kanwar Dahiru aka ji maganar shine duka kusan kowa a shiyarsu yaji. Ina jin haka nace to ko Ummiyo ce, ba tana kawance da yarinyar nan Rahane ba"

Da sauri Ummiyo ta lallaba ta koma bandakin tsoro ya cika ta. Amma Rahane ta cuceta yau ina zata saka kanta.

Hannu Inna ta dora a ka tana kiran ta shiga uku. Dahiru yayi fam yana cewa ina take. Suna wannan halin Inna tana yiwa Yakumbo bayanin ainihin me ya faru sai ga Baffa da Danlami.

Tun daga waje yake fada abin da ba halinsa ba yana kiran Inna. Ganin Yakumbo a gidan ya kara tabbatar masa da abin da yaji.

"Me yasa ku mata baku da hankali, babu rufin asiri sannan ba kwa tunani sam. Saboda Allah abu ya faru jiya amma har ya baza garin nan lokaci guda."

Hakuri Inna ta soma bashi yace tayi shiru kafin rai ya kara baci
"Ko inda zani ban karasa ba Danlami ya riskeni yana tambayata gaskiyar zancen da abokansa suke yi kan yarinyar Mal Fatihu. Ban gama al'ajabi ba Bilya da yake nesa ma ya kira yana tambayata. Wai kanwar matarsa ce ta kira 'yar uwar ta sanar da ita. Me yasa zaki yi min haka do Allah?" Ya kare fadan yana kallon Inna.

Duk jikinta yayi sanyi hakan ya kara konawa Dahiru rai. Wato Ummiyo ce jiya yaji motsinta shine kuma tana ji ana yiwa mahaifiyarsu fada tayi shiru.

Hanyar bandakin ya kalla sai ya ga sawu da danshi. Ta fito kenan ya fada a ransa. Baiyi wata wata ba ya fada bandakin Inna tana ya dakata sai gashi ya fito da Ummiyo da daurin zani har kirji da kuma wani da tayi lullubi dashi.

A gaban iyayen nasu ya soma sauke fushinsa a kanta inda ya fara dukanta kamar wanda aka aiko.

Baffa rabuwa yayi dasu zuciyarsa na kuna. Allah Ya sani baiyi niyyar cigaba da shirin auren Dahiru da Mawadda ba. Amma wannan rashin hankalin na Ummiyo ya janyo dole sai ya sake tunani.

Yakumbo da Inna suna ta fada amma Dahiru bai bar dukan Ummiyo ba. Da kyar Liti da Danlami suka kwaceta bayan ya tumurmusata a kasa. Tashi tayi da kyar tana kuka Baffa ya hauta da fada. Abu ya tarar mata ta rasa yadda zatayi sai hakuri take bayarwa.

Tsabar bacin rai yasa Dahiru ficewa daga gidan ya barsu da tunanin mafita don barna dai an riga anyi.

Sai can yamma ya dawo yana zuwa ya hau wanki. Kayansa masu dan dama-dama ya wanke Inna jiki duk a sabule saboda fushin Baffa tace ina zai je yake ta wanki da shiri.

"Kano zan tafi gobe wurin Yayanmu Bilya."

"Me zaka je yi Dahiru" Baffa ya tambaya.

"Kwanaki yace na sami gurbin karatu a BUK wanda ya nema min nace bana so noma zanyi. To gashi bukatarsa ta taso zan bincika idan har yanzu ban makara ba ina son inje."

"Ai gara kayi karatun kafin nan an kashe wannan gobarar ma" in ji Inna.

Girgiza kai Dahiru yayi "Inna ba zama zanje yi ba don ina dawowa idan ta fito daga asibiti nake so a daura auren sai na tafi da ita. Zan nemi aiki ko na karfi ne inayi saboda ciyar da ita da kuma karatun nawa"

Magana zata sake yi Baffa yace ya wuce abinsa Allah Ya kaimu goben.

A fusace ta juyo "Baffa yaya haka?"

"To gaya min yadda kike so ayi. Kina kallo na kasa fita saboda fargabar haduwata da Mal Fatihu saboda aika-aikar da 'yarki tayi. Kina jin ina da bakin fada masa an fasa auren yaran nan? Salon dan sauran mutumcin nawa ya karasa zubewa ko me"

Tashi tayi ta shige ciki rai a dagule. Ganin Ummiyo tayi rakube da kwaba ta mangareta kafin ta wuce "shegen surutun tsiya gashi nan zaki jawo mana jangwam haka kawai"
*****

Sai wajen taran dare Mal Fatihu suka dawo da Yaya don tun la'asar su Innarsa suka dawo. An baro Ade da Iya a asibitin.

Yau ma sauran yaransu suna gidan kakaninsu.

Bilki, Hasiya, Nana da Jamila sune manyan 'ya'yan Yaya da ke dakunan mazajensu. Ga mamakin iyayen suna shiga gida suka samesu duka su hudun. Jamila ita ce sakuwar Mawadda kuma babbar aminiyarta don ba karamar shakuwa bace tsakaninsu. Sirrin da basa iya fadawa kowa a waje suna yi da juna. Da kuka ta tari Yaya tace tun la'asar suka zo dukkansu labari ya riskesu gashi sun je gidan Malam wato kakansu babu kowa. Kannensu kuma suna makaranta lokacin shiyasa basu san a wane asibitin aka kwantar da Mawadda ba.

Daga Yaya har Baba hankalinsu ba karamin tashi yayi ba. A ina suka ji har suka taho duka su hudun. Biyu ne ma a Tariwa wato Bilki da Jamila. Hasiya da Nana kauyukan da suke aure suna makotaka da Tariwan ne.

Zama suka yi Yaya ta basu labarin komai. Sunyi kuka kamar me suna takaicin dare yayi da a lokacin zasu tafi asibitin.

Kafin Baba ya tambayi inda suka ji wannan labari sai yaji sallama. Shi yanzu gabansa har faduwa yake yi idan yaji ana sallama dashi.

Haka nan ya tashi ya fita. Makocinsa ne da suka hada katanga. Musabaha suka fara yi sannan yace "Mal Fatihu haka ake zaman tare kuma abu irin wannan ya faru ba don gidan Mal Isiyaku ba ashe da bazan sani ba."

Wani irin sanyi ne ya soma ratsa Baba na tsananin shiga damuwa. Suna can asibiti ashe kowa ya gama sanin me suke boyewa. Kuma a rasa daga ina magana zata fito sai daga bangaren wanda yake tunanin ko yaya zasu rufa musu asiri. Shikenan tasu ta same su a garin nan. Basu da sauran mutumci kuma sai yadda hali ya yiwu.

A hankali ya iya cewa "kayi hakuri hankali na ne ba a kwance ba domin dawowata kenan ma gidan"

"Eh ai na kula shiyasa nayi saurin kiran sauran abokan arziki don duka fa mun damu. Wunin yau sur maza da mata zuwa muke ta yi gidan nan babu kowa."

"Mungode bari na shiga ciki kaina ke ciwo sosai" bai jira amsarsa ba ya koma ciki.

A nan ya sami Yaya tana kuka tana sanar dashi basu da sauran sirri an gama tozarta su a garin nan.

Da wannan damuwar gidan Baffa da na Baba suka kwana kowa da abin da ya dame shi.

Da safe da wuri suka shirya da su Bilki , masu goyo suka kintsa yaransu suka fita. Baba yaso ganawa da Baffa amma a yadda ransa ya baci yasan za'ayi batacciya ne kawai.

Fitar su Baba ke da wuya Baffa ya karaso gidan. Da ga waje wasu mutum biyu suka sanar dashi yanzu suka tafi bakin titi da iyalinsa zasu tafi asibiti. Abin duniya ya ishi Baffa ya juya gida jiki a sanyaye.

Nanatawa yake a ransa Ummiyo bata kyauta masa ba. Babu abin da ya kai kima da mutumci a wurin babba gashi ta zubar masa da nasa da kaikayin baki.

Bayan ya koma ba dadewa Dahiru ya shiga rumfarsa yi musu sallama shi da Inna. Idan ya sami yadda yake so baya sa ran wuce sati daya. Sun bi shi da addua da fatan alkhairi ya sabi jakarsa ta viva yayi waje.

*****
Su Baba sun isa asibiti suka samu 'yan sandan nan sun dawo kamar yadda suka yi alkawari. Mawadda na kuka Iya ta tursasata akan ta bude ciwukan jikinta kamar yadda mai hoton ya bukata domin a dauki shaida. Wannan wane irin tozarci ne BB ya janyo mata. Likitan da ya duba ta shine ya fadi wuraren da ya ga ciwo kamar shatin belt a bayanta, cinya da kuma fuskarta da bata gama daidaituwa ba. Da suka fita haka 'yan uwanta suka zagayeta suna ta koke-koke. A wannan halin Iya ta fice sadaf-sadaf ba tare da sun kula ba ta bi bayan Likitan.

Ko zama baiyi ba ta shigo tare da rufe kofa. A hankali cikin sigar rada ta soma magana tana kuma yi masa alama da kada ya daga murya shima.

"Dan nan ka fada min gaskiya ka tabbatar Mawadda ba wai haihuwa ce tayi ba fyade ne kawai"

"Me zai sa kiyi tunanin haihuwa tayi? Jikarki budurwa ce da tsautsayi ya afka mata"

Sake rage murya Iya tayi sannan ta fiddo zanin Mawadda da ta dauka da sunan za ta wanke "Likita ka taimaka ka duba min ita sosai. Tun jiya na kula idan ta jima a zaune ta tashi wurin sai yayi lema. Yau dai na dauki zanin sansana ka ji.."

Saurin kawar da kansa yayi ganin da gaske Iya tura masa zata yi a gaban fuskarsa.

Ko a jikinta yadda yayi ta sake juya zanin "nayi zaton haihuwa kadai ke kawo yoyon fitsari"

Ba arziki Likita ya tashi "yoyo kuma? Kai muje dai na sake dubawa"

Tare suka fita Iya tana biye dashi har dakin. Nos ya kira ya bukaci kowa ya fita da ga shi sai Mawadda da Nos din ya kalleta cike da tausayawa. Yarinya karama tana ta fuskantar matsaloli da kuruciya.

"Malama Mawadda dubaki zan sake yi"

Kukan nata ma ya kafe sai zafin zuciya. Tunda tazo ake bankada mata jiki ko ta ina. Wannan kadai ya isheta bakinciki. Ba musu ta kwanta inda yana daga gefe ya umarci Nos din da ta duba masa ita ko akwai danshi a tare da ita.

Gabanta ne ya fadi jin furucinsa. Tabbas kwana biyu bayan faruwar al'amarin nan gareta ta tsinci kanta da digar fitsari wanda bata iya rike shi idan yaso fita. Ko kwakkwaran motsi tayi sai taji alamunsa batare da kuma tana cikin matsuwar fitsarin ba. Tayi iya kokarinta wurin ganin tana rike shi kamar da amma abin yaci tura. Gashi bata sanar da kowa ba ta yaya aka gane?

Dubawar farko Nos din ta tabbatar masa da abin da suka zo nema. Hakan yayi matukar daure masa kai yayi 'yan rubuce-rubuce bayan Mawadda ta amsa tambayoyin da ya yi mata sannan ya fita.

Kusan awa uku a tsakani ya turo aka kira masa Baba. A lokacin dama suna sanar da su Iya maganar da ta bullo a gida kusan kowa ya san sirrin da suke boyewa a dalilin fitar maganar daga gidan Mal.Iskiyaku. Suna kuka suna bawa juna hakuri ya fita ya barsu.

Kasan babbar rigarsa yasa ya goge hawayen da yake barazanar zubo masa sannan ya shiga karamin ofishin likitan.

Waya ya ajiye ya dubi Baba cikin damuwa
"Baban Mawadda kayi hakuri da abin da zan fada maka"

Cikin Baba ya nemi kullewa a firgice. Me kuma ya faru yanzu.

"Ina jinka Likita"

"Bayan dan bincike da nayi da kuma amsoshin da Mawadda ta bani ina zargin ta kamu da lalurar rashin rike fitsari saboda raunin da jijiyoyinta suka samu har karfinsu ya ragu"

"Nufinka dai yoyon fitsari ta kamu dashi?"

"Eh... to! Ba na ce ba saboda abu ne da sai anyi dogon bincike da gwaje-gwaje. A takaice dai Baba yarinyar nan sai kun sauya mata asibiti. Ku kaita cikin Kano asibitin Malam Aminu Kano ko kuma asibitin Murtala. Mu nan bamu da kayan aiki sosai kuma rashin bata kulawa da wuri kan iya haifar mata da babbar matsala a gaba"

"To nagode" Baba ya iya cewa ya mike jiri na dibarsa. Banda fyade da ciwukan da aka ji mata saboda duka harda yoyon fitsari kuma. Ina zai saka kansa? Ina yake da kudin kaita asibiti a Kano?

Da wannan tunanin ya koma wurin iyalinsa. Bilki ce take tilastawa Mawadda cin abinci Iya tana basu labarin yadda suka yi akan kunu jiya da Dahiru.

" Idan taki ci ku aika a kirawo shi ku ga cin abinci da neman kari"

Dariya sauran sukayi ita kuwa sai murmushin kunya. Da Baba ya shigo kiran Yaya, Ade da kuma Iya yayi waje domin sanar dasu sakon likita.

Yaya da Ade suka soma salati Ade tana matsalar kwalla. Iya bata yi mamaki ba domin tayi zargin haka tun da ta kula da danshin take bari a wuri idan ta tashi.

"Ku koma ciki ba kuka zaku yi ba Allah zai kawo mana mafita" Baba yace yana juya musu baya saboda yadda zuciyarsa take neman gaza daukar wannan bakon lamari.

"A'a Fatihu gara mu san me muke ciki tun wuri tunda Likitan ma haka ya bada shawara. Ke Ade ina so ki saurareni da kyau. Gidan da kike aiki zaki samu ki koma ko gobe ne ki sanar da matar matsalar da ake ciki ko zasu ranta miki kudin ko da ba kyauta ba."

Tana maganar Ade ta soma girgiza kai "gaskiya bazani ba Iya"

Duka Iya ta kai mata a kafada "ji min sakarci fa. Kina so kice min kinfi karfin rokon taimako ne ko me? Indai baka dashi to ka yarda baka dashi din ka nema a wurin wanda ya fika. Kice rance ba kyauta ai dai bashi hanji ne a cikin kowa"

Hayaniyar yaran nasu ce ta fara yawa daga dakin Yaya sai ta fake da zata tsawatar musu ta basu wuri. Batah jiran karin bayani tasan suna bukatar kebewa don a shawarta yadda za'ayi.

Bayan ta shige Iya ta murmusa tana binta da kallo "Wallahi Fatihu matarka ba dai sanin ya kamata ba."

Yau wace rana Iya ta yabi Yaya.

Shiru yayi bai ce komai ba sai tunani da yake yi ta ina zai sami kudi shi ba wata kadara ba balle ya sayar.

Iya ta sami wuri akan wani benci ta zauna tana kallonsu duk hankalinsu a tashe.

"Duk wani so da zamu nunawa 'ya'ya fa ya bi bayan jajircewa wurin nema musu lafiya. Kyautatawar da muka yi muku da kuruciya ita take janyo jin kai tsakanin mu daku idan mun girma. Yanzu meye naki na cewa bazaki je ki ranci kudi a wurin matar da kike yiwa aiki ba? Mutum me da har yana da wani sauran jiji da kai ne idan bashi da kudin kulawa da dansa? Kwantar da kai ake yi gaban masu kudi idan kina son jindadin zama dasu"

Cikin kuka Ade ta labarta musu yadda suka rabu da Sakina. Hatta Baba ransa ya baci balle Iya. Sun jajantawa juna yadda masu kudi basu dauki hakkin talaka a bakin komai ba.

Rai a bace Iya tace "ko da nace ki kwantar da kai ba cewa nayi ki wulakanta kanki ba kina jina. Kwantar da kai daban, shi iyaka ki sawa ranki mutum ya fiki arziki babu ke babu girman kai a neman halak. Amma ban yarda kowa cikinku ya wulakanta kansa akan kudi ba. Kada kuje ana cin zarafinku kuna hadiyewa don wani abu da za'a baku mai karewa a duniya. Duk zafin talauci wuyarta ka mutu kana mumini magana ta kare. Hakkinki kuma ki bar musu muna nan dake ko ba a gaban idonki ba sai tayi nadamar abin da tayi miki" Iyan kanta tana magana kuka na menan cin karfinta. Sai dai dattijuwa ce mai matukatar dauriya kuma a matsayinta na uwa garesu bata so ta karyar musu da zuciya.

Baba ta cewa ya koma gida akwai tumakinta uku da awaki biyar ya kama duka ya kai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login