Showing 102001 words to 105000 words out of 110071 words

Chapter 35 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

1907

tsautsayin nan ya faru basu hadu ba har kuma maganar da ta fitar ta janyo aka hanata fita gabadaya.

Tunda Dahiru ya fadawa Mawadda yadda Ummiyo ta dauketa ta matsu su hadu. Yanzu da ta ga duk ta takura kanta sai ta saki fuska ta matsa ta riko hannunta. A dan firgice ta kalli Mawadda ita kuma tayi mata murmushi tana kallon Inna.

"Inna don Allah waye babba a shekaru ni da Ummiyo?"

Kallonta suka yi duk su biyun ita da Baffa suna dariya. Inna ta amsa mata "kece mana bare kuma yanzu girman naki ya karu"

Mawadda ta sake murmusawa "to sai ki gaisheni tunda kinji da kunnenki nice babba idan ba haka ba kuma duk inda muka hadu har kasa zan durkusa miki"

Ummiyo taja da baya da sauri sai ga hawaye "don Allah rufa min asiri abin sai yayi min yawa"

Hankalin Mawadda ya tashi ita da take kokarin ganin ta daidaita tsakaninsu "menene haka daga wasa"

Gefen mayafinta tasa tana goge hawaye "ki yafe min don Allah"

Dahiru da su Inna duka kallonsu suke yi. Shekara da shekaru Ummiyo tana fama da wannan damuwar saboda ta dorawa kanta laifin komai da ya biyo bayan rayuwar Mawadda. Shiyasa bata iya sakewa kamar da duk surutun ya tafi.

Har zuciya maganar ta daki Mawadda. Ta dade da yafe mata ko ince bata taba daukar abin a rai ba ko don albarkacin Dahiru tun a wancan lokacin. Idanun iyayensu ya sanya mata jin nauyi ta rungume Ummiyo ta barin jikinta "komai ya wuce Ummiyo don Allah kada a sake tada zancen nan."

Sai yanzu Ummiyo ta iya murmushi tun fitowarsu daga gida. Bilya ne ya daukosu a tasha don shi niyarsa yaje da kansa ko Danlami su daukosu sai wayar Baffa ya samu wai sun kusa shigowa gari. Shine yaje ya daukosu ko wanka baiyi ba. Yana kawosu ya koma gida batare da ya shigo ba.

Sai da Dahiru ya kula hankalin iyayen ya koma ga Ummiyo da Mawadda suna ta murmushin wannan shiryawa tasu.

"Wallahi Allah Innarmu ba haka ake yi ba" yace yana kankance ido fuskarsa na nuna alamun fushi yake.

Inna ta ware idanu tana masa kallon tambaya "me aka yi ba daidai ba?"

"Jiyan nan mota ta kwasheni ta wulwulani a sama sannan na fado na hadu da gaban mota da zafin kwalta" yana magana yana kwantatawa da hannu "amma shine kun shigo kawai kun biyewa waddan" ya nuna Mawadda da Ummiyo.

"Yanzu kai kishi kake da matarka da kanwarka? Wannan abin kunya da yawa yake" cewar Baffa.

Inna ta zauna a kusa dashi "da gaskiyarka Dahiru babu wani abin kunya. Ya ya jikin"

Saitin Mawadda ya kalla yana harararta "da sauki"

Baffa yace "abin naka harda jin baki."

"Ba fa kace min ya jikin ba har yanzu"

Duka dariya suka yi sai kuma hira ta barke tsakaninsu su uku a can gefe kuma Ummiyo da Mawadda ke yi tasu tana tambayarta game da 'ya'yanta.

Basu jima ba sai ga Attahir da Nawal da abinci. Rungume juna suka yi da Mawadda tana tambayarta mai jiki bayan ta gaisa da su Inna. Suna haka Marwanu ya iso shima da kayan abinci yace su Baba zasu taho anjima. Inna da Iya sunce sai sun biyosu ga kuma su Bilki duka sun baro gidajensu shine suka yanke shawarar sai kowa ya iso zasu taho tare.

Bai dade ba ya fita saboda dakin ya cika. A bakin kofa ya hadu da Danlami da matarsa suma da kayan abinci. Yana rike da kwandon abincin ita kuma ta goya Humaira. Tuni dakin ya kaure da hayaniya. Baffa ya fita daga waje ya bar Inna da 'ya'yanta.

Wata kumbular mota mai kyau ce tayi parking Qareeba ta fito. Tayi kyau sosai don kuwa taci kwalliya saboda tasan zasu hadu da Bilya. Idan bai zo ba ma jiransa zata yi. Tun asuba taso shiga kitchen Dr Tani ta korata daki wai zumudin yayi yawa. Bacci ya sake dauketa tana farkawa ta fada kitchen ta hada girki mai dadi domin farantawa kanin miji don ta sake samun shiga wurin yayansa. Ba yadda Dr Tani bata yi ba akan ta zauna sai shabiyu ta fito taki amincewa har kuka ta kusa yi.

A cikin kwando mai kyau ta jera komai wanda kwanukan Daddynsu ta debo batare da sanin Dr Tani ba. Har zata wuce ciki daga kasan bishiyar dake gefen inda ta ajiye mota a farfajiyar asibitin ta kula da wani dattijo ya kara karamar rediyo a kunnensa. Jini baya karya kallo daya tayi masa ta san matsayinsa.

Riga da skirt ne a jikinta ta kashe dauri mayafi a kafada. Gyara mayafin tayi ta janyo shi har ka a ranta tana cewa dole ta chanja wannan dabi'ar girma ya kusa hawa kanta.

Baffa bai kula ba hankalinsa yana ga labaran da yake ji sai ganin mace yayi a gabansa ta rufe rabin fuskarta.

"Baba ina wuni? Anzo lafiya? Yaya su Mama? Ya mai jiki kuma?"

Kallonta yayi tana ta jero tambayoyi ya amsa mata ba don ya santa ba "baiwar Allah wurin Dahiru kika zo?"

Murmushi tayi cike da kunya tace eh sannan ta tashi ta tafi. Ladabinta ya burgeshi ya bita da fatan alkhairi.

Daga waje ta fara jiyo surutu kofar a bude take ta kutsa kai da sallama tana mitar sun dami kaninta da surutu baza su barshi ya ji saukin jikinsa ba.

Idonta akan Mawadda tana zuba masa abincin da Nawal ta kawo. Dankali ne aka dafa sannan taka burgeshi ta kada da kwai da nama da kayan kamshi ta soya da kauri sai farfesun kaza.

Hannu ta daga ta dakatar da ita "ga nawa abincin nasan zaiji dadinsa faten tsaki ne harda yakuwa da ugu saboda yaji dadin bakinsa. Kuma kinga basai ya tauna ba"

Sam bata kula da Inna ba tayi zaton su kadai ne a matsayinta na matar Bilya to be ta isa tayi musu gyaran kuskure. Mawadda ta tsaya kallonta ta turo mata kwandon ta karbe plate din da ta gama zuba wancan abincin. Nawal ta hade fuska tsaf rai a bace tana kallon Attahir ya kawo dauki. Tasha wahalar girkin kuma ace bazai ci ba wanda akayi dominsa.

Dahiru da Danlami sai dariya suke yadda Nawal ta hade rai itama Qareeba ta sha kunu tana kallon Mawadda "bazaki zuba bane in zuba da kaina? Bawan Allah bai ci komai ba"

Yau dai ta karewa Anti Qareeba kallo kuma har ranta taji tana sonta. Nawal ta kalla "uhmm kinga Sis in ajiye wannan sai yaci da rana?"

Kusa da Inna Nawal ta koma "Inna don Allah ba nice na fara kawowa ba"

Ita Inna bata san wacece Qareeba ba itama Qareeban lokacin ta kula da ita ta zube a kasa a gabanta cike da kunya. Dakin ya kaure da dariyar yadda tayi harda Nawal mai fushi.

Ta gaisheta a mutumce Inna tana tambayar wace ce ita Dahiru yace Anti Qareeba. Dama Mawadda na gefenta ta kuma janyo hannunta sai da tayi kasa itama a hankali tace mata "kiyi mata bayani sosai"

Bata san Mawaddan ma kunyar Inna take sosai ba ta dago ta kasa cewa komai. Kyakkyawan mintsini ta kaiwa Mawadda a dantsen hannunta taji zafi ta hau susa ta kuma fahimci sakon "Inna idan Allah Ya yarda fa Yayarmu zata zama"

Qareeba ta saki yalwataccen murmushi Inna ta kalleta ta koma kallon yaran nata da alamun tambaya. Danlami yace "Yayanmu Bilya"

Kai wannan abu yayi mata dadi don fuskarta ta nuna sai ta wayance da cewa bari taje su wuce gidansu Mawadda da Baffa dakin ya cika. Attahir ya mikawa Danlami mukullin motarsa "ka kaisu"

Qareeba tace "yanzun nan nasha mai ina da full tank gara ya dauki tawa"

Inna tace sun gode babu damuwa zasu tafi a ta Attahir. Jikinta yayi sanyi ko batayi maraba da ita ba.

"Inna nima 'yarku ce don Allah ku dauki tawa"

Sai da Inna tayi da gaske ta yarda su tafi a ta Attahir ta bi bayan su Mawadda aka raka su har mota.

*****

Sun dawo dakin suna hira Mawadda ta zuba masa faten dakin kuwa sai kamshi don yaji kayan hadi. Da zafi sosai sai ta ajiye akan fridge ta sake dukawa zata dauko kofi Furera ta shigo tana faman yatsina. A wulakance ta yiwa Dahiru ya jiki harda karin cewa ya auri wahala.

"Ace tun kafin a shafa fatiha ka gagara kwanciyar hankali ina dalili. Yanzu har an fara harin rayuwarka"

Mawadda tayi shiru tana jin zafin maganganun da Furera ta cigaba da yi. Dakin duka tsit yayi kowa yasan da wa take dama. Dahiru baya son yi mata rashin kunya a gaban su Attahir da Ummiyo sai yace da Mawadda ta bashi ruwa ya fara sha.

Jiki a sanyaye ta zuba masa ta dago ta kusa buge bowl din faten Ummiyo tayi saurin daukewa tana cewa "hankali dai Yayarmu"

Furera na kyalla ido ta hango mene a cikin bowl din ta mika hannu ta karba babu kunya.

"Faten tsaki kayan marmari bari muji..." ta ciko cokali da naman da aka yanka kananu fal a ciki ta kai baki. Dadi ya ratsata ta lumshe idanu "Allah Ya tsaga rabona da haka zaku barshi ya bushe a zubar. Mara lafiya ko don gaba Mawadda abinci kadan ake zuba musu idan sun bukaci kari a kara daga baya."

Wannan zubar da mutumci nata ya kular dasu amma Qareeba nata ran yafi na kowa baci amma tana mata kallon mara kan gado ta sassauta murya tace "Ahirin wace wannan ne?"

Bai amsa ba Bilya ya shigo. Ba karamin kyau yayi da kayan jikinsa ba kufta da wanda na wani lallausan yadi baki sai hula. Ya tsaya a waje magana dasu Baffa da zasu tafi shiyasa bai shigo da wuri ba.

Furera tana shan faten tana ganinsa tace da Mawadda "shima ki zuba masa yana sonsa sosai. Ni bani da jimirin yi ne kawai"

Kallon kallo ake a dakin yadda ta shigo hannu na dukan cinya take nuna iko akan abinda ba nata ba. Da bacin ranta suka fito da Bilya don tun dare da ya fada mata yayi zaton zata yi girkin zuwa asibitin. Da zasu fito yaga babu komai a hannunta yayi magana tace tasan zaa kai daga gidan Baba Prof da gidan su Mawadda. Rai a bace yace duk fadin Kano shine yafi cancanta da Dahiru yake da hakki akansa tunda shine babba. Duk wanda ya kai kara yayi musu. Sai tayi mirsisi abinta ta shige mota.

Qareeba tunda ta ganshi haukan matar da take tunanin 'yar uwarsu ce kawai ya dena damunta ta sunkuyar da kai bayan kowa ya gaishe shi itama ta gaishe shi.

Yaji dadin ganinta sosai kuma yadda yayi tunanin jin tsoron Furera ta sani sai abin baizo masa a haka ba.

Attahir da gayya yace "Anti Qareeba ki zuba masa mana"

Furera tana ta kalkale bowl din da cokali yana ta fitar da sautin kwal kwal ko a jikinta. Sai shine ma yace a koshe yake. Ai da kunya yazo dubiya dubiyar ma ta kaninsa ga matansu a wurin ya hau cin abinci duk da yadda ransa ya biya don da yunwa ya fito saboda bacin ran baa yiwa 'yan asibiti abinci ba. Hararar Furera yayi jin tace a kara mata "tashi mu tafi yanzun nan akace hayaniya tayi yawa a dakin zasu zo suce kowa ya tafi"

Dahiru ya kalle shi ya kalli Qareeba "Yayanmu baku gaisa da Anti Qareeba ba har zaku tafi."

Daga shi har ita sai murmushi yayin da Furera ta shiga bude kwanuka neman fate. Tashi yayi ya fita ta bi bayanshi tana nunawa Mawadda ta karbe food flask din kada Furera ta cinye.

Attahir ma yace gara su tafi an hana su Dahiru cin abinci. Sallama suka yi musu zasu dawo anjima suka fita ya rage dakin saura Ummiyo, Furera da Mawadda.

Sai da Mawadda ta jira Furera ta dibi mai isarta tace da Dahiru zai ci ya bata fuska. Ko don tabawar da tayi ta bata wurin jage jage saboda keta yace baya so. Na Nawal ta sake zuba masa ta wanko hannu ta dawo ta haye gadon daga gefen kafarsa da take a nade a mike ta takwanshe kafafunta yana jingine da filo a zaune ta soma bashi.

Furera tana kallonsu har ta gama zaman wanda dama da uku ma tayi ba da biyu ba don ta tanka ta samu ta fada mata magana.

"Iskanci da rana tsaka Mawadda meye haka? Mutum yana fama da lalura don bakin naci da jaraba a nan din ma sai..."

"Anti Furera abinci zan bashi ba wani abu zamuyi ba fa"

Ummiyo ta soma dariya gashi dai taji kunyar zaman da suka yi. Bude baki yayi da hannu take bashi idanunsa a kanta suna yiwa juna murmushi.

Furera sai ta kasa hadiyar abinda yake bakinta don takaici. Da yanzu fa Hansa'u ce take kula da Dahiru yake nuna mata soyayya irin haka. Itama shegiyar yarinyar wai ta kalli tsabar idonta tace mata ta hakura da Dahirun. Tsaki ta ja bazata iya kallon wannan rainin wayon na Mawadda ba. Ta kalli Ummiyo.

"Ke! Tashi mu fita wannan abin da suke yi gaba zai kara don idan bakiyi wasa ba cinyarsa zata hau a gabanki"

Mawadda ta rufe ido "kai Antinmu ai ba lafiya gare shi ba yanzu" ta mayar da kallonta gareshi tana wani fari da ido yana biye mata da tambayar ko itama ya bata a baki.

Saura kiris Furera ta fashe ta tashi ta fice Ummiyo ta bi bayanta tana dariya. Haba mata duk basa sonta saboda yadda take wahalar musu da dan uwa.

Can bayan fitar Bilya da Qareeba wurin motarta suka je.

"Bilyamin me yasa baka ci faten ba? Ni nayi da kaina"

Wani benci ne a jikin bango suka zauna da tazara a tsakaninsu kafin ya amsa mata "ashe kin iya girki"

"Kala-kala kuwa"

"To amma kina ganin za'a bawa wannan makaniken mace kamar ki Qareeba ya rinka cin daddadan girkinki?"

"Kana tunanin guje min ne?" Ta fada tana kallon idanunsa. Duk abinta kasa jurewa tayi ta kawar da kanta.

Gyaran murya yayi ya nemi ta saurare shi da kyau "Qareeba ban mallaki komai da zai bani damar aurenki ba. Kinga jiya muka hadu zan so mu bi komai a sannu saboda kada nan gaba abin yazo bai yiwu ba"

Zuciyar Qareeba ta karye. Tasan me yake hange amma tayi rantsuwa idan har ya amince mata to bata miji sai shi.

"In hakura kenan?" Tace idanu na ciccikowa da kwala.

"Zaki iya zama dani da matar nan da ta cinye abincin da kika dafawa Ahirin?" Ya bata amsa da dariya.

Rike baki tayi kafin ta kwashe da dariya.
"Matarka ce don Allah"

Yayi murmushi "uwargidanki ba"

Qareeba abin ya bata mamaki yadda Furera ta shigo ta iya cin abinci bata zo da komai ba harda yiwa mijinta tayi. A take taji ta rainata. Ta rinka dariya yau ta ga wadda ta fita.

Fitowar Furera da Ummiyo ya katse mata hanzari. A fusace ta matso inda suke.

"Ka bani kudin mota na tafi. Wai don rashin mutumci a gabana yarinyar nan Mawadda take bawa Dahiru abinci a baki...a baki fa kamar wani karamin yaro. Shi kuma sai wani lumshe idanu yake kamar wanda ya sha wani abu"

Iska Bilya ya furzar ransa yana kuna ya mike zai bata amsa Qareeba ta riga shi don haushi matar take bata sosai.

"Mawadda da Ahirin ba miji da mata bane"

Ummiyo tace "kuma masoyan asali ba"

Furera ta daure fuska.
"To waye mara mijin?"

Qareeba ta kalli Bilya "Bilyamin...."

Zaro idanu Furera tayi "Bil me kika ce? Kai wai ma wace ce ke ne? Me kuke yi a nan?"

"Wadda tayi faten da kika shanye " Bilya ya ce.

"Anti Qareeba sunanta" Ummiyo ta bata amsa a takaice.

"Auuuu ita ce wadda Dahiru yayi aiki a gidansu ko? Shine kima zo duba shi harda girki? Sannu da kokari. Su Mawadda an manta da asalin miji sai wani fiffika take ita ta auri mai kudi"

Qareeba ta kalli Bilya don ta tattaro bakar magana zata bata amsa amma tana tsoron kada yaji haushi. Sai gashi ya bata mamaki.

"Qareeba ga uwargidana Furera. Furera ga Qareeba amaryarki in sha Allahu"

Su biyun kallonsa suke yi ya dake abinsa yana binsu da ido shima. Qareeba ta tabbatar yau Allah Ya kawo mata nata mijin. Furera sai da ta nutsu maganar ta sauka a kwanyar kanta kawai sai ta tura hannunta a makogaro tana kakarin amai. Kanta suka yi Bilya yana cewa meye haka. Ta dago idanu jazir da bala'i.

"Ni zaku kashe don kana son yin aure? Shine aka barbade faten aka bani nasha. To Allah Ya isana. Kuma kayi auren idan ka isa."

Ummiyo ta matsa gefe "Anti Furera babu wanda yayi kiki tayi kika dauka fa"

"Aikin asirin kenan Ummiyo. Abu a ajiye babu mai ci sai ni ina zuwa naji kamar yana cewa daukeni Furera...daukeni"

Da gaske tana ta kakaro amai abu ya gagara. Bilya ya kira Danlami yace yayi sauri ya dawo da motar idan ya kai matarsa gida shima zai tafi ne.

Ciki suka koma suka barta don ita tace kafin ta fara kishi dole ta fito da faten tsakin nan wanda ya sami wuri a cikinta ko gezau yaki fitowa.
*******

Wayar gaggawa aka yiwa Alh Sule tun dare daga ofishin Hisba sai gashi asubar fari yana idar da sallah ya kamo hanyar Kano hankali a tashe. Da kwatance ya isa ofishin nasu da aka kwatanta masa.

Haj Mara ta fita hayyacinta saboda tsabar tashin hankali. Yana isowa bayan an fito dasu ya daga hannu ya sharara mata mari sai da ta ga wani haske nan ya gilma.

Duk zafin bai dameta ba kamar wata muguwar tsanarta da take gani a idanunsa. Zubewa tayi a kasa jiki na rawa ta rike masa babbar riga.

"Alhaji kada kace kaima ka yarda da zargin da ake yi min."

Zuciyarsa har kuna take "Marakisiyya kin cuceni kuma a yau na kara nadamar aurenki. Sai dai nasan kaddara ce ta rayuwata. Na fada na kuma fada yaron nan kina cutar shi ne amma kin ki ji. Karshe ma kin koya masa tsanata da kin jin maganata a matsayin makiyinsa. Yau gashi dan cikina ake zargi da neman mahaifiyarsa"

BB da jikinsa ya gama tsami ya dago kai da kyar "Alhaji na zata Mawaddata ce fa. Mutanen nan sharri suka kula mana."

Shima Alh Sule ya sani Haj Mara bazata taba yin abinda ake zargi ba. To amma tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa ke duka. Cike ciken takardu yayi tare da 'yan sandan da aka kira suka zo suka daukesu bayan ta aminta da bakinta biyan kudi tayi aka fito mata dashi.

Wunin ranar sur ayi nan office din dasu su gama bayani a koma yi wani wurin dasu.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login