Showing 93001 words to 96000 words out of 110071 words
Chapter 32 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt
fa nason iskanci matar Yayana zata zama."
Attahir ya fashe da dariya "solidarity sak dan uwa ai nima yayana ne. Muje mu basu wuri. Amma wallahi kamar tsoronta yake yi. Allah Sarki Yayanmu Bilya"
******
Shiru falon daga Qareeba har Bilya an rasa wanda zai fara magana. Shi bai san ta ina zai fara ba ita kuma nan ta kame ne kada tayi abinda ta saba ake cewa bata da kan gado. Gajiya tayi ta danyi gyaran murya.
"Ehemmmm"
Bilya ya zubo ruwa da sauri ya miko mata "sannu karbi ki sha"
Fari take tana juya idanu kafin ta karba ta dan kurba kadan.
Bilya ya kalli yadda tayi da idanu ya zuba hannuwansa a aljihun riga "me ya sami idanun ko zaki shiga ciki ki wanke?"
Kasa hakuri tayi cikin muryarta ta sangarta tace "wai kai baka taba zuwa wurin mace bane?"
Sai da ya koma ya zauna ya amsa mata "ni da nake da aure da 'ya'ya ma"
"Duk abuna nasan wurina Ahirin ya kawoka ko ba haka ba"
Bilya a ransa yace toohh wannan gaba gadi take sannan ya gyada kai.
"Ina ganin sun fita na gane. Shine kazo babu wani tambayoyi irin wanda ake yiwa mace farkon zuwa kayi shiru abinka."
Murmushi yayi saboda yadda take tuttura baki da gani an saba yi mata yadda take so amma kuma tsoronta yake ji don yadda take magana yasan kila ana jinsu kada azo ace ya yi mata wani abu.
"Yi hakuri gani nayi kamar kinfi karfina shiyasa nayi shiru"
Sunkuyar da kai tayi tana jin kamar kwalla muryarta tana rawa tace "kai dai ka fadi gaskiya ko kaima banyi maka bane? Its ok an saba haka bazan ji haushi ba"
Jikinsa ne yayi mugun sanyi ta bashi tausayi. Mace har mace bai hango wata makusa ba amma Allah bai nufeta da aure ba. Aure babu ruwansa da arziki ko kyau. Idan lokaci yayi ne kawai sai anyi.
"Qareeba ni talaka ne, makanike mai mata da yara kuma dan kauye wanda karatunsa ya tsaya a JSS 3. Ina zan kaiki?"
"Inda ake kai mata"
Hannu biyu tasa ta rufe bakinta bayan maganar ta subutu ta fito ta shige kunnuwansa suka hada ido. Mayafinta da yake a kafada ta dauko ta rufe fuska karo na farko a rayuwarta da taji kunyar wani da namiji.
Wani murmushin ya sake yi "indai zaki iya aurena a haka to wannan talakan yayi alkawarin kaiki inda ake kai matan...dakin aure ne a killace su a basu kulawa"
Tashin hankali mamakin kansa ne ya kama shi. Daga ina yake zaro wadannan zantuka shi kuwa. Qareeba tsabar kunya balle da yace zai aureta ta shiga tattaba wuya ta tabbatar kalau take ba zazzabi bane yasa ta kasa magana.
Yana lura da ita yace "baki da lafiya ne?"
"Ina jin dai ba kalau ba. Kaga na kasa dago kai na kalleka abin mamaki" tace da gaske cikin mamakin.
"Bayan kin gama yi min kirikiri da ido meye baki gama gani ba" ya zolayeta.
Ta sake rufe fuska "ban taba jin haka ba tunda nake akan kowa"
"Me kike ji Qareeba?" Bilya ya sami kansa da tambayarta. Sosai yake jindadin magana da ita.
"Farinciki"
Karamar dariya yayi ta dago da kai "don Allah kada ka samin rai kaima naji shiru. Nasan Ahirin ya fada maka komai a kaina amma wallahi ba'ayi raping dina ba"
Bilya ji yayi ko gobe akace yazo a daura musu aure zai yarda saboda yadda Qareeba ta shiga zuciyarsa musamman saboda tausayi.
"Ki bari nayi zuwa uku sai mu tabbatar da zamu iya zama da juna. Sai dai matsala daya wallahi Dahiru baya son sunan nan Ahirin"
Bude mayafin tayi ta sa dariya "ai wallahi sai dai yayi hakuri sunansa kenan a wurina"
******
Dahiru da Attahir a kafa suka fita tunda ba nisa bane titi kawai zasu tsallaka suyi tafiyar kasa da minti biyar.
Fitowarsu a idon BB da Bobo ya tabbatar Mawadda bata bayansu yace "Bobo dawo nan da sauri"
Chanjin seat suka yi ya tada mota da sauri ya bata wuta. Attahir ya haye dan tudun gefen titi inda zai sada shi da gidansu shi kuma Dahiru yana daga bayansa. Daga kafarsa ke da wuya basu san daga ina ba sai ganinsa suka yi yayi sama saboda wani mugun bugu da BB yayi masa ya dawo ya daki kan bonnet dinta ya fadi kasa ko motsi kwakkwara baya yi.
Attahir mutuwar tsaye yayi har maigadin gidan Dr Auwal da wasu maza suka taho suna kokarin daga Dahiru. Jikinsa gabadaya ji yake kamar an sara masa guduma. Bai tashi gane me yake yi ba sai da suka yi ido da ido da BB Sule Chanji yayin da ya fizgi motar a guje kamar zai tashi sama.
[31/01 9:36 am] Batuul Mamman: *GUMIN HALAK...*💰23
*Batul Mamman*💖
Kwanaki shadaya da auren su Dahiru wanda yayi daidai da kwana goma da tarewar Mawadda. A dan tsukin lokacin nan shakuwa mai karfi ta shiga tsakaninsu. Duk abinda Dahiru zaiyi domin ya cire mata tsoro kuma ta saki jiki dashi yana yi. Shiyasa bata da wata damuwa sai ta kokarin kyautata masa.
Zamansu gwanin sha'awa kana ganinsu kaga masoyan da suka yi nisa cikin soyayyar juna. Tsakaninsu dasu Attahir ma sai son barka. Matan suna matukar kokari su hada kai domin jindadin mazansu. Nawal bata da matsala. Yadda ta rungumi Mawadda babu kyama ko nuna ta fita domin ita a yanzu bautar kasa zata fara sabanin Mawadda da Adult education tayi.
Yau da sassafe matan suka tashi saboda aikin da yake gabansu. Gidan Baba Prof zasu je daga can kuma kowanne zai tafi da matarsa gidan iyayenta. Washegari kuma Dahiru da Mawadda su tafi Tariwa su kwana biyu.
Mawadda ta gama tuwon shinkafa da miyar agushi tun daga falo kamshin miyar sai yasa yawu tsinkewa. A kasa kuma Nawal ta kusa gama suyar samosa da doughnut da zasu hada su kai musu.
Shadaya da rabi ta gama komai harda breakfast ta gyara gida ta koma daki domin tashin Dahiru sannan tayi wanka. Filon da take sawa tsakaninsu dogo shi ta gani a kasa shi kuma yana amsa waya.
Wardrobe ta bude inda ta jera musu kayansu ta tsaya tana karewa kayanta kallo.
Bayan Dahiru ya gama wayar taji yace "Matar Dahiru yau ba gaisuwa?"
"Ina zuwa gaisheka na ga ka jefar min da dan amana a kasa"
Dariya ya soma yi yayi rub da ciki ya rike fuskarsa da hannuwansa.
"Kin jawo masa yau zan jefa shi ta taga ma. Haka kawai kullum yana tsakiyar mata da miji shi ko tsoron daukan alhaki baya yi ma"
Sai da tayi dariya tace "babu wani hakki, tunda hannunka ya warke ko zaka koma kasa? Idan ka sauka da kaina zan jefar da filon"
"Haka ma zaki ce? Kwana kike makale da shi fa ga bawan Allah a gefe" ya nuna kansa yana bata rai.
"Laushi ne dashi baka ji ba kamar auduga"
Dauko shi tayi daga kasan ta mika masa wai ya taba yaji laushin. Yana karba ya cilla shi wurin kofa.
"Indai laushi kike nema to kisha kuruminki na fishi. Yau don Allah in meye gurbinsa kinji"
"Kai bread ne?"
Tana fada ya taso yayi kanta tana dariya zata gudu ya janyota kan gadon ya danneta "nine bread din?"
Dariya take sosai "wasa nake yi Yayanmu"
"Sai fa kin dauki bread dinnan yau" yace yana sakar mata nauyinsa.
Nishi ta soma "wayyo Babana mijin Mawadda zai ballani, tsokanar da kake min zan rama amma na fasa kayi min rai tuba nake"
Kadan ya dagata amma yadda bazata iya tashi ba.
"Waye ni?"
"Mijin Mawadda mana"
"Ba kaninki ba ko yayanki ba?"
Sake sakin nauyinsa yayi tace "inaa da kenan, yanzu ka hada duka harda aboki da miji"
"To me zaki bani?" Ya kuma danneta.
"Me kake so? Wayyo kirjina Yayanmu nauyi gareka fa"
Dagata yayi suka tsaya ya nuna filon "kishiyan can nawa zaki dauke yau daya dai a barni na kwanta kusa da amaryata"
"Washhh, naji kuma dole na amince kafin ka rabani biyu"
Hancinta yaja yana tsokanarta reshe ya juye da mujiya. Tazo tsokanarsa abin ya koma kanta. Fada masa tayi ta gama girki da komai gara suyi wanka kada su Attahir su jirasu.
Wata atampa ta nuna masa a kayanta ya girgiza kai ta cigaba da nunawa yana cewa basuyi ba. Sai da ta nuna wani lace mara nauyi ruwan toka da digon ja yace shi zata saka.
Fita yayi ya bata wuri ta shiga wanka shi kuma ya kira lauyansu suna tattaunawa akan case din. Ya sanar dashi yadda suka yi da su Qareeba ta fada masa duka wani abu da ya bukata. Dr Tani da Maigadinsu zasu bada shaida tare dashi kansa Dahirun.
"Yanzu statement din matarka nake bukata duk da na samu wasu bayanai a police station din"
"Idan babu damuwa sai mu hadu ranar litinin in sha Allahu sai kayi mata tambayoyin. Mungode sosai"
"Aikina ne Dahiru. Allah Ya bamu nasara"
******
Daya saura gidajen biyu sun gama shiri. Dahiru da Attahir suna tsaye jikin motocinsu suna hira da tsokanar juna. Kusan minti biyar babu wanda matarsa ta fito.
"Wato da gaske dai idan za'a fita da mata sai anyi jira" cewar Dahiru
"Ga alama ka gani kamar sun hada baki. Shikenan muma mun girma. Yadda manya suke mitar jiran matansu yau abin yazo kanmu"
Dahiru ya soma dariya "sai yanzu ka girma ashe?"
"Ana shafa Fatiha nace to girma salamu alaikum"
Tafawa suka yi suna yiwa juna shakiyanci aka turo karamar kofar gate din da suke bari a sakaye.
Hayaniyar yara suka fara ji kafin Furere ta sako kafa tana cewa su shigo. Su biyar ne yaran harda ita da Hansa'u mutum bakwai.
Dahiru na ganinta ya hade girar sama da kasa. Dazu da safe lokacin da Mawadda take aiki a kitchen wayarta ce ta tashe shi ta sanar dashi zasu zo yini ita da yara. Tun a lokacin ya fada mata fita zasu yi kuma dama har gidan zasu je domin a basu girmansu na yayyensa. Tana jin haka ta tambayeshi yaushe zasu tafi yace suna yin azahar. Wato shine ta tare shi don kawai ta bata masa rai.
Har suka shigo ya kasa sakin fuska sai da Attahir ya tabo shi "meye haka ne Dahiru?"
Saurin gyara fuskarsa yayi "babu komai zamu dan bata muku lokaci matar Yayanmu Bilya ce"
"Na gane ta"
"Dan bani minti goma su gaisa da Mawadda sai mu tafi"
"Haba Dahiru don Allah kuyi zamanku gobe ko wata ranar sai kuje."
Karasowa suka yi Hansa'u tana tafiya kamar ta karye saboda kwarkwasa.
"Ango kasha kamshi kace gara da muka zo yau din tunda fitar bata yiwu ba"
Attahir ne ya masa kallon yayi shiru ya daure yace tazo su hau saman.
Yana bude kofar Mawadda tana yafa mayafi ta rike kunnuwanta "sorry"
Kallon mutanen da suke shigowa tare dashi tayi ta saki fuska duk da bata sansu ba ta ajiye mayafin a hannun kujera.
"Baki muka yi haka? Sannunku da zuwa"
Wurin kofar taje da fara'arta tana cewa su shigo su zauna.
Hansa'u ta tsura mata idanu kamar ta cinyeta har sai da ta tsargu.
"Ba baki bane. Matar yayansa ce da 'yaranta ni kuma kanwarta ce"
Murmushi Mawadda tayi "Allah Sarki ku zazzauna mana bari na kawo muku lemo yau akwai rana"
Anti Furere ta hakimce akan kujera "Allah Yasa da sanyi dai"
Mawadda bata tanka ba ta wuce kitchen. Hansa'u da Anti Furera suka bita da na mujiya. Riga da zani ne a jikinta na lace da gani yana da tsada. Rigar tayi mata kyau sosai ta fiddo da surarta wadda take tafiya da Dahiru duk sanda ya kalleta. BB kansa wannan jikin ne ya fara kwadaita masa ita. Bata fiye tsayi ba don bata cikin layin dogaye ma amma surar jiki da kyaun fuskarta suna daukar hankalin mutane da dama.
Tana tafiya Dahiru yace "Anti ba na fada miki zamu zo ba?"
"Dahiru korata zakayi daga gidanka? Ikon Allah sai kallo. Yau kayi arziki kayi aure dole ka wulakantani"
Kallo ya bita dashi na takaici bai iya bata amsa ba ga yara a wurin. Mawadda ta fito musu da lemuka masu sanyi da ruwa. Sai cake da snacks din da Nawal ta miko mata. Itama tuwon da tayi haka ta dibar musu ta bata idan sun dawo babu mai yin girki.
Zama tayi ta sake gaishe da Anti Furera ta dauko kofuna zata tsiyaya musu lemon.
"Da kin bari kowa ya dauki roba daya zasu iya shanyewa"
Tayi murmushi "to shikenan"
Hansa'u ta dauki remote ta kunna TV ta shiga canja tashoshi. Rai a bace Dahiru ya tashi ya koma daki. Duk wannan.abin yasan ana yi ne kawai don yayi magana. Rigarsa ya cire yayi jifa da ita daga shi sai dogon wando da singeleti ya kwanta ya soma kiran Mawadda.
Tana zaune a kasan kafet suna ta hayaniya su da yaran babu mai kula ta taji yace "Babyna"
Yadda suka tsura mata ido da mamaki itama shi din ne ya kamata.
Hansa'u jiki yayi mugun sanyi kamar tayi kuka dama tana ganin Mawadda ta raina kwalliyar da tayi.
Anti Furere ta soma fada "wane irin abu ne wannan nazo da yara za'a bata musu tarbiya."
Da sanyin jiki ta tashi ta tafi. A kwance yake ya daga hannu yana mata alamar ta taho ta bata rai "Yayanmu so kake ka bani kunya?"
Sai da ya taso ya rike hannunta ta zauna akan gadon sannan ya kwanta ya dora kansa a cinyarta abin yazo mata wani iri.
Dago kai yayi yana kallon fuskarta "kiyi hakuri to. Anti Fureran ce sai da haka."
"Saboda me?"
"Kiyi dai hakuri nasan zasuyi ya yin abubuwa don kiji haushi. Da biyu ne Hansa'u taso na aura"
Kallon idanunta yayi da suka nuna zallar kishi ya kuwa kankameta sosai ta hanyar zagaye kugunta ya cusa kansa wurin cikinta.
"Kada ki damu ke kadai nake so Mawaddatan wa Rahma. Na fada miki ne don kada ranki ya baci ko me zasu yi"
A hankali tace "to sakeni na koma kafin nayi laifin barinsu su kadai"
"Uhmm uhmm" yace yana kara matseta "ni mu zauna a haka"
"Don Allah"
"Kiss me"
Jikinta taji ya soma rawa tsabar kaduwa da kunya ta shiga ture shi "ba zaki tashi ba fa sai kinyi yadda nake so"
Cije lebenta tayi ya janyo kanta daidai fuskarsa ya shafa leben "wannan abin yana burgeni sosai" ya karashe da kissing dinta.
Kamar daga kofar dakin suka ji ana cewa "Kawu Dahiru Umma tana kiranka"
Firgigit suka tashi daga shi har Mawaddan yace "kin gani ko"
"Ba laifinsu bane kaine ka janyoni"
Doguwar riga yasa suka fita tare.
"Don munzo gidanka shine zaka mana wulakanci Dahiru?"
Mawadda ta nufi dinning table inda ta ajiye abincin da ta shiryawa su Haj Mama bisa umarnin mijinta.
"Yi hakuri Antinmu kirana akayi ta wayarsa ni tawa ta lalace. In kawo muku abincin nan kasa ko na barshi a nan?"
"Sauko dashi muna kallo muna ci"
Haka ta kai musu ta hado da plates suka ci suka sha ba godi bare nagode. Sai ma da suka gama Hansa'u tace wai zuciyarta tana tashi kifin miyar yana neman dawo mata. Mawadda tana yi mata sannu taje ta kawo mata cingam.
Zama tayi cikinsu tana hira da yara tunda su tasu suke daban.
Labulenta Furere ta nuna "laaa Hansa'u kinga irin labulen nan da muka gani a kofar wambai mutumin yace akwai kyau a ido sai rashin kwaliti shiyasa suke arha"
"Aikuwa shine. Tun dazu nake masa kallon sani"
Maganar ta yiwa Mawadda zafi sai share. Sunyi dabdalarsu a gidan har akayi magariba. Bayan ta sake yi musu girki sunci abinci tana wanke-wanke Hansau ta sake cewa tana jin tashin zuciya. Daga kitchen din ta fada mata inda zata duba a falon ta sake daukar cingam.
Anti Furera ta tashi tayi hanyar kitchen din "Ke kuwa da anyi magana sai ki ce aci cingam kamar wata tsohuwar karuwa"
Ko motsi Mawadda ta kasa don bakinciki itama Hansa'un da akayi dominta fuskarta ta sauya alamun rashin jindadi.
Ganin haka nata jikin yayi sanyi ta tura babban danta har dakin su tace ya kira Dahiru yazo ya kaisu gida. Duk da baiji dadin shigar yaron ba don a kalla shekarunsa kusan sha daya amma yaji dadin zasu tafi. Jeans da shirt ya saka ya fito.
Kowa ya mike burin kunya Anti Furera har kitchen ta shiga "amarya mu zamu tafi babu rakiya"
"Hannu zan dauraye gani nan"
Ta rakasu har kofar kasa da irin tarkacen gidan amare kayan zaki da na kwalliya da ta bawa yaran. Ta yiwa Dahiru adawo lafiya ta koma. Tana rufe kofar saman hawayen da ta rike tun da aka jefeta da wannan kalma suka soma zuba ba kakkautawa.
Da jan kafa ta koma ta gyare gidan tsaf tana aiki tana sharar hawaye. A ganinta fyaden da aka taba yi mata shine dalilin da yasa har Anti Furere ta iya danganta ta da wannan kalma.
Idanunta sun kumbura da ta fito daga wanka ko abinci bata iya ci ba ta saka rigar bacci mai kyau tayi kwanciyarta.
Tunanin rayuwa da yadda abubuwa suka kasance mata take yi har dawowar Dahiru.
Rufa tayi har ka don kada ya ga hawayenta sai ya zaci bacci tayi ya shiga wanka. Da ya fito har lokacin bata bude kanta ba ya zauna a gefenta ya dan ja bargon "wannan irin rufa iska na shiga kuwa?"
Rike quilt din tayi yana ja tana ja "dama idonki biyu kina jina?"
Shiru ba amsa ya zagaya bayanta ya bude bargon.
"Ka fita ka shirya" tace tana kara rikewa.
Budeta yayi da karfi "naki." Sai kuma ya bude baki hankalinsa a tashe "...Mawadda me ya sameki? "
"Bacci nake ji sosai kawai"
Ya bata rai "wane irin bacci? Kukan me ki ke yi?"
Gabanta ne ya fadi don kuwa bazata taba fada masa ba. Tun da can surutu ba dabi'arta bane bare yanzu da iyaye suka ja mata kunne akan kai kara musamman ma ta dangin miji.
"Na fada maka bacci ne"
Ya daga murya "Me tayi miki?"
"Wa?"
"Anti Furaira. Dama tun da zasu tafi na kula baki da walwala sai na zaci gajiya ce."
Kwantar da kanta ta sake yi akan filo "nace babu komai ko karya kake so nayi maka?"
"Mawadda ba wasa nake yi ba. Ko ki fada ko na koma gidan na tambayeta da kaina, kinsan kuma zan iya"
Tashi ta ga zaiyi ta riko hannunsa da sauri. Tasan abinda ya sakata kuka zai bata masa rai shiyasa da ya zauna sai ta fada masa abinda suka ce game da labulen falon. Sai da ta gama ya riko fuskarta a cikin tafukan hannunsa.
"Shagwaba ko Matar Dahiru. Da nine ke sai nace na gidanta na fada miki a bakin rimi aka kada masa kararrawa. Amma bari idan munje gidan sai ki rama"
Murmushi tayi ganin sakayawar tayi rana.
"Hankalina ya tashi sosai nayi zaton abin yafi haka. Shima idan munje baki rama ba zan rama miki da kaina"
Kwantar da kanta