Showing 87001 words to 90000 words out of 110071 words

Chapter 30 - GUMIN HALAK Complete Book by Maman Batul.txt

22 Sep 2025

1913

zai bita shine namiji idan da mai hakura da gadon shine. Irin dogon pillon nan ta ajiye a tsakiyar gadon saboda a gajiye take idonta har ya soma yaji. Ta nuna masa bari daya

"Ka kwanta a can kuma kada ka wuce pillon nan"

"You are the best Yayarmu Mawadda. Sai da safe. Ki kashe fitilar bana son haske"

Kwanciyarsa yayi a barin da ta nuna masa ta lalubi makunnin fitilar ta kashe. Zata rama ne bari dai yaji saukin hannun nasa tace a ranta.

A darare ta kwanta ta takure jikinta ko hijabin bata cire ba sai zanin kawai ta kwance. Yau ita ce kwance gado daya da Dahiru a matsayin mijinta. Godiya ta yiwa Allah da Ya cika mata burin da ta fitar da tsammani daga tabbatuwarsa. Ba jimawa bacci ya fara fizgarta har Dahiru yaji sauyin yanayin saukar numfashinta.

Wani dadi ne ya kama shi ya matso ya dauke pillon ya cilla shi kasa "anyi kanekane tsakanin mata da miji"

A hankali don kada ya tasheta ya matsa kusa da ita ya lullubesu. Rungumota yayi dama baccin nata babu sakin jiki a take ta farka zuciyarta ta tsananta bugu. Yaji ta fara motsi tana neman kwacewa daga rikon da yayi mata.

"Assha don Allah kada ki koreni tsoro nake ji" yace da karamar murya.

"Tsoron me" ta fada itama a hankali.

"Dodo"

"Zan daure"

"Da me?"

"Mu kwanta a haka Yaya da kaninta matsoraci"

Zai sake magana ta dora hannunta akan bakinsa "bacci nake ji ka dena magana"

Murmushi yayi ransa fari kal kamar an zuba madara. Allah Yayi shi Dahiru zai auri Mawadda. A nata bangaren kuwa shiru tayi kawai zuciyarta kamar ta fito amma tana so ta danne don ta faranta masa. Gajiya da rashin baccin da yake kansu yasa basu dade cikin tunanin da suke yi ba bacci ya kwashe su duka.

*****

Bacci dadi sai da hasken rana ya fara shigowa dakin suka tashi. Mawadda ce ta fara farkawa ta gansu sun cure wuri daya ga hijabinta a gefen gadon ko yaushe ta cire bata sani ba. Matsawa tayi daga jikinsa da sauri. Hannun ciwon ta kalla, wannan hannu ya ga ta kansa ko yaushe zai sami sukunin warkewa.

Bandaki ta shige ta dauro alwala ta fito tazo tana dukan gefen gadon. Da kyar ya bude ido yana ganin haske ya ware su sosai ya tashi "Subhanallahi wane irin bacci nayi haka?"

"Na gajiya"

Ya kula tayi alwala yace ta jira shi suyi tare. Bayan sun idar ya duba wayarsa ko Attahir ya kira shi tunda sunyi akan wanda ya fara tashi ya tashi dan uwansa suje masallaci tare. Bai ga missed call ko daya ba yaji dadi ya sami abin tsokanarsa.

Bayan azkar a wurin Mawadda ta sake bingirewa ya saka mata pillow shima ya janyo wani ya kwanta. Bacci suka sha sosai sai shadaya wayarsa ta tashesu. Sunan Baffa ya gani ya gyara murya tare da yin sallama suka gaisa.

"Dahiru kayi hakuri zan fito da kai kana fama da wannan hannun. Ana nemanmu a ofishin 'yan sanda wai mahaifiyar yaron ce tazo"

Zama yayi sosai yana kallon Mawadda ransa ya soma baci. Ya tsani komai da zai sa ya tuna da BB to amma fa dole wannan karon a yiwa tufkar hanci ta yadda za'a kawo karshen abin once and for all.

Da sauri-sauri ya shirya motsinsa ya tashi Mawadda. Kunya taji ace tana bacci har wannan lokacin Dahiru ya tashi yayi wanka.

Hijabinta ta gyarawa zama "Yayanmu ina kwana".

"Lafiya kalau, na tasheki ko?"

"Yakamata na tashi dama, yaya hannun?"

"Da sauki. Kinga koma kiyi kwanciyarki kada ki tashi sai azahar. Baffa ke nemana zamu je police station akan case din BB"

Dukar da kanta tayi jikinta yayi sanyi lakwas da jin sunan mutumin da ya zame mata dodo. Dahiru ya saki fuska yazo gabanta ya tsaya ya dago da kanta da hannunsa. Rufe ido kawai tayi ya ga hawaye yana zuba. Matseta yayi kam a jikinsa ta fashe masa da kuka mai ban tausayi. Kyaleta yayi tayi kukan har don kanta ta dena ta koma ajiyar zuciya.

"Mawadda" ya kira sunanta daga kasan makoshi har taji tsigar jikinta ta tashi.

"Uhmm"

"I love you so much abinda nake so ki sakawa ranki kenan a kodayaushe"

Kankame shi tayi ta cusa kanta cikin kirjinsa. Ita ta sani har abada bata da hanyar sakawa Dahiru. Yayi mata halaccin da addu'a da fatan alkhairi a kullum sune kadai abinda zata iya yi masa.

Dariya yayi yana son hada ido da ita "ko dai yau Mr and Mrs muka tashi ne? Kinga ina dawowa sai na cigaba da nuna miki yadda ake yiwa amarya"

Matsawa tayi da sauri tana murmushi a kunyace ta canja zancen "baka ci komai ba zaka fita"

Ya shafa cikinsa "zaki iya hada min coffee kafin na karasa?"

Ta gyada kai ta fita shi kuma ya kira Attahir yana tambayarsa mukullin motarsa.

"Fita zaka yi ne?"

Nan ya fada masa wayarsa da Baffa. Attahir ya nuna rashin jindadinsa da bai neme shi ba akan su je tare.

" Ba don kai na rabu da kai ba. Idan na yiwa Nawal haka ban kyauta ba. Ka zauna ka kula da ita don Allah."

Attahir yayi dariyar shakiyanci "me kake nufi?"

"Ka fini sani. Zancen gaskiya bai kamata muyi ta shiga hakkinta ba. Idan akwai matsala zan nemeka amma yanzu kayi min wannan alfarmar kayi zamanka"

Attahir ya kalli inda Nawal ke kwance tana bacci fuska a kumbure an sha kuka. Shima yasan idan ya fita bai kyauta ba gaskiya. Mukullin ya je ya ajiye a seat din gaba na motar ya koma wurinta aikin lallashi.

Dahiru ya sha coffee sai bread kadan saboda kiran da Baffa ya sake yi masa. Mawadda ya jaddadawa tayi bacci zai taho musu da cefane saboda babu kayan miya idan zai dawo.

"Nasan zanyi missing dinki so zan kiraki duk rabin awa"

"A wace wayar?" Tayi murmushi.

"Ohhh to sai kin sake hutawa zamu je a sayi sabuwa. Da kanki zaki zaba"

Tana tsaye a bakin kofar ya soma sauka benen ta daga masa hannu. Sai da yaje kofar kasa ya dawo da sauri ya sumbaceta a kumatu ya sake sauka.

*******

"Nace ko nawa kuke so ku fada a fito min da yarona na ganshi" Haj Mara kenan tana ta kumfar baka a cikin police station din.

Wata murdaddiyar police ce ta fito ta daka mata tsawa "kina hauka ne zaki cika mana wuri da ihu kamar kasuwa? Kai Corporal idan ta sake bude baki ku rufe min ita"

Haj Mara shiru tayi sai da matar ta gama magana ta tafi ta sassauta murya "ku taimaka don Allah"

Wani Sergent yaji tausayinta "Hajiya case din fyade da satar mutum ne akansa ba'a bari a gansu sai anje kotu"

Duk ta fita hayyacinta saboda damuwa ta nuna jakarta "kai ni wurin DPO a kashe maganar nan zan biya."

Tsaki yayi ya bar wurin suka kyaleta tana ta babatu. Sai bayan kusan awa guda Dr Auwal, Dr Tani da Alh Sule suka shigo tare.

Ganinsa da tayi da makiyanta ya harzuka ta matuka. Dr Tani ta washe baki kai kace gonar auduga saboda jindadin ganinta a wannan yanayin.

"Haj Mara ashe rai kan ga rai? Kwana biyu. Me kike yi a nan?"

Dr Auwal ya bita da kallo wai don ta dena ta dauke kai kamar bata gani ba ta cigaba da magana.

"Yaron da yaso kassara min 'ya ne aka kamo yaje ya sace amarya ranar da zata tare don karfin hali."

Haj Mara ta cika kamar ta fashe ta kalli Alh Sule shekeke "ka biyosu ne domin a ga yadda za'a hukunta danka ko me?"

"Marakisiyya ki ajiye makaman yakinki mu ceto yaron nan."

"In ceto abuna daga hannun makiya dai. Alhaji kotu fa za'a je da dan cikinka."

Irin alamun kwancewar kai Dr Tani take yi da hannunta tana kallon Haj Mara, wato bata da hankali.

Shigowar Dahiru da Baffa da Baba ya mayar da hankulansu bakin kofa. Duk hassadar mutum dole ya yabi Dahiru saboda ganin farko zaka gane ya wuce raini. Ba wai ta fanin kudi ba don su Haj Mara sun kere shi nesa ba kusa ba. Kwarjini gareshi da cikar zati ga kyau ga kuma iya ado na mazan da suke ji da kansu a wannan zamani.

Da sauri Dr Tani ta matsa kusa dasu "Dahiru dana na kaina ina kwana"

Ya dan dakata ya kalleta ya tabbatar kunnensa ba karya ya jiyo masa ba. Dr Tani ce take gaishe shi yau da kanta.

"Lafiya kalau, yaya mai jiki?" Yace yana karbar hannun da Dr Auwal ya miko masa.

Wani dadi Dr Tani take ji kawai ace tasan Dahiru. Bayan an gama gaisawa ta nunawa Haj Mara shi "ga fa dana Dahiru angon da Babawonki ya sacewa mata. Kin tuna Mawadda Fatihu ai, ita ce amaryar"

Yawu ta hadiya da kyar tana kallonsu. Ta gane Mal Fatihu sai dai sabanin sanin da tayi masa da jikinsa da suturarsa sun nuna duniya bata wulakanta shi ba.

Ofishin DPO aka kira su domin karin bayani.

"Wannan case din babu zancen sulhu domin ita Dr tace sai an bi mata hakkinta. Haka nan iyayen amaryar Mawadda da mijinta sun ce su ma babu maganar sulhu saboda haka mun tattara komai za'a mika kotu"

"Wane irin kotu officer? A kashe maganar nan kowa ya huta" inji Haj Mara tana daga murya.

"Hajiya gaki ga mutanen da aka yiwa laifi"

"A yadda kuka ce ba. In ba tsoro ba ina ita amaryar da aka yi masa sharrin ya sata kamar wata jaka ko allura?"

Cikin fushi Baba yace "sharri fa kika ce? Kin manta ni ne? Kin manta 'yata da danki ya lalatawa rayuwa...."

Dahiru ya kankance ido yana kallonta "Baba ka barni da ita kafi karfin bata amsa. Mawadda da kike nema tana gida bazaki ganta ba sai ranar da za'a fara sharia."

A fusace ta mike tsaye "aikin banza kai, an fada muku zan yarda da wannan kullalliyar ne? Tani kinji dadi ki zuba ruwa a kasa kisha. Kinje kin samo mutane kun biyasu kudi ace shine mijinta saboda kin sha alwashin ganin bayana don yaki auren dolowar 'yarki"

DPO ya soma cewa suyi shiru amma ina kowacce ta kule. Haj Mara ta tafi kowa zakalkalewa har tana cewa

" *wane mahaukacin ne zai auri yarinyar da aka taba yiwa fyade har ya daki kirji ya nuna kansa idan ba biyansa aka yi ba*"

Shiru ofishin yayi sai da ta fadi maganar ta gane abinda tayi sai kawai tasa kuka.

DPO kuwa dama ransa ya baci da hayaniyar da tayi don har ya kira azo a kulle su.

"Wannan abu yayi kyau ga shaidu sun ji da kanki kin amince anyi mata fyade kamar yadda iyayenta suka sanar damu tun farko. A kotu sai kiyiwa alkali bayani sosai."

Kuka ta saka "wannan duk sharrin Tani ne yallabai. Kuyi hakuri a taimaka min in ga dana"

Baffa yace "yaro taimaka ka fito mata dashi ko don a tabbatar dan nata ne ba wani kuka kama ake yi musu sharri ba"

Basu jima ba kuwa sergent ya ingizo keyarsa aka shigo dashi da ankwa a hannu.

"Na bani na lalace BABAWO!"

Kansa tayi a gigice ta rungume shi. Tafiya yake baya iya hade kafafu wuri ya kumbura. Fuskarsa kuwa fitar hakora uku ba wasa ba. Tayi suntum kuma yayi rashin sa'a cell daya aka hadasu da Danmami. Bakincikin an kama shi ya yiwa BB dukan kawo wuka cikin dare saboda ya janyo masa za'a sake kaishi kurkuku. Ya taba zaman wata uku baiji dadi ba ko kadan.

"Wallahi nima sai na shigar da kara. Inji ubanwa yace idan ana tuhumar mutum ayi masa jinajina?"

Babu wanda ya kulata BB da ido daya yake hawaye don dayan ya hade don kumburi shima. So yake ya tambayeta ko an sake shi ne a yau amma babu dama. Ya kalli Alh Sule wanda shima zuciyarsa ta tausaya dan nasa sosai ya kawar da kai.

Alh Sule a raunane yace "Babawo Allah Ya fissheka alkhairi Yasa wannan abu ya zama izna ga 'yan baya."
Muryarsa ta soma rawa ya fice yana jin babu dadi.

Haj Mara tana kallo aka kada keyar gudan jininta tana kuka kamar ranta zai fita shima yana yi. Su Dahiru ko gezau suka fita bayan DPO yace kowa ya nemi lauya za'a sanar dasu lokacin shiga kotu.

******

Baba suka fara ajiyewa sannan ya wuce ya kai Baffa gidan Bilya inda daga nan zasu wuce Tariwa a yau.

"Baffa ko hutawa baku yi ba"

"Wane hutu kuma banda abinka. Gara mu kuma kaima ka samu natsuwa kafin kwanakin da aka ce za'ayi zaman farko su cika. Ga waya nan ku rinka sanar damu yadda abin ya kasance"

Tare suka shiga gidan. Inna ma ta gama shiri ta nunawa Dahiru abinci tace ya dauka Furaira ce ta dafa musu shi da amarya. Zaiyi godiya ya ga uwar hararar da take watsa masa daga ita har kanwarta Hansa'u. Ya tabbatar dole Inna tayi mata ta zuba abincin.

Bata san halinsa bane har take tunanin zaici wannan abincin da aka bawa matarsa ba da zuciya daya ba. Ai kuwa tana ganin Inna ta koma daki dauko jaka taja tsaki.

"Wahalalle tunda ka fara soyayya da yarinyar nan matsalar yau daban ta gobe daban amma ka like kamar wanda aka bawa ruwan asiri."

Amsa ya tattaro zai yaba mata sai ya tuna daraja da kimar Bilya ya fasa "Abincin nan idan na tafi dashi karashenta sai dai a bawa almajiri don tayi girki ma"

Furaira ta sha kunu "ita wa?"

Kai ya sunkuyar wai shi kunya "ita din"

Hansa'u ta rike haba sai kuma ta soma tafa hannuwa "matar taka ce bazaka iya fadan sunanta ba?"

Irin murmushin nan mai ban haushi yayi musu duk su biyun "so kuke Inna taji? Duk abuna da kunya in fadi sunanta a gaban iyaye. Kunsan Babyna nake kiranta"

Babu wadda ta tanka masa suka wuce ciki a fusace. Dariyar Danlami ya ji a bayansa.

"Yayanmu Dahiru ka matsawa matan nan wallahi"

"Baka san takaicin da nake na yadda take yiwa Yayanmu Bilya ba. Shi kuma sai yayi shiru baya iya nuna bacin ransa ma"

"Dama dai yayi aure" Danlami yace yana daukar jakar Innarsu.

Idanun Dahiru ne suka kara girma saboda wata idea da ta fado masa. Shi kadai yake ayyanawa a ransa lokaci yayi da Anti Qareeba zata hadu da Man.

Suna bakin mota da Inna yake tambayarta game da rashin zuwan Ummiyo.

"Kaima kasan dalili dai"

"In sha Allahu har tsakar dakinta zan kai Mawadda komai ya wuce"

******

Sahad ya wuce ya siyo kayan da yake tunanin suna bukata. Sauran ko nan da sati sai ya fita da Mawadda su saya ko tayi masa list. Daga nan ya tsaya ya sayi kayan miya da nama. Dariya abin ya bashi wai cefane.

Mawadda tana zaune a falo tayi kwalliya cikin wani material mai santsi anyi mata gown me siririn hannu. Irin daurin nan na murde jelar dankwali ta gaba a zagaya dashi daga bari daya tayi. Tayi matukar kyau kamar a sace. Gidan kuwa tun daga kofar hawa saman yake zuba kamshi.

Dahiru na tsayuwa da mota ya fita da sauri yana burin saka matarsa a ido. Da sauri ya hau saman yana bude kofa ya ganta tana fitowa daga daki.

Tamkar numfashinsa zai tsaya tsabar kyaun da tayi masa. A tare suka sakarwa juna murmushi ta ware mayafin da ta dauko da niyar idan ya dawo ta yafa saboda haka kawai taji kuma nauyin zama da rigar.

"Kada ki yafa ki bata min kwalliya mana" yace yana ware mata hannuwansa ta taho gare shi.

Dage gira tayi tana dariya "Yanzu a Gwaggo nake sai ka karaso mu gaisa ka sami wuri ka zauna"

Dariya yayi harda hamdala sannan ya nufota gadan-gadan. Bayan kujera ta koma da sauri ya biyota tana gudu tsakanin kujeru.

"Yayanmu ba kyau wayo Gwaggo nace fa"

Yana bayan kujera ita kuma ta zagayo gaban yace "haba Gwaggo don Allah ki tsaya duk na gaji"

"To ita Gwaggo ana rungumeta ne?" Ta turo baki.

"In kinji runguma daya kenan. Tsakaninmu da Gwaggonni rungume-rungume ne. Haka ake yi idan an gansu har kwanciya ake yi a jikinsu"

"To waye ba'a rungumewa?"

Ya dan kalli sama "amare saboda kowa ya sansu da kunya"

"Wayo kake son yi min to ban yarda ba"

Kai ta ga ya dukar "na hakura bari na koma akwai kaya a motar da ban dauko ba"

Da jan kafa ya soma tafiya har ya kusa kofa ta bishi da sauri ta kamo hannunsa. Wani abu suka ji duka su biyun ya juyo yana kallonta.

Daurewa tayi tace "rabin minti a matar Dahiru"

Wani irin kallo yayi mata mai tattare da soyayya da kauna.

"Kin tabbata?"

"Ko in fasa?"

"Maganar farko Sarki yake karba."

Hannun nata da ta rikeshi da shi ya janyo ta fada jikinsa. Wata kyakkyawar runguma yayi mata suna jin bugun zukatan juna.

Muryarta a sanyaye tace "rabin minti ya cika"

"Me ki kace?"

"Ra...."

Hadiye kalmar tayi lokacin da ya hade bakinsa da nata. Sun dauki lokaci a cikin yanayin da su kansu basu san yadda zasu fassara shi ba.

Ya dago kai yana neman idanunta ta rufe su.

"Kunya?"

Ta gyada kai tana kara hannunwanta akan fuskarta.

"Nima haka" yace yana rufe tashi fuskar.

Sosai taji kunyarsa ta juya bayanta ya tsaya yana kallonta daga sama har kasa yana dada godewa Allah da Ya bashi ita.

Sauka yayi ya dauko ledoji biyu da hannu daya. Tana gani tazo ta karba sai ta koma bakin benen idan ya dauko sai ta karba har suka gama hawowa dasu.

Daukar komai tayi tana kaishi inda ya dace shi kuma ya tafi yayi wanka. Yadda take aikin tana tunanin Dahiru haka yake shiryawa yana tunaninta da jin kewarta ta dame shi kamar wadda bata gidan.

Kananun kaya ya saka ya fito bata falo amma ga abinci akan dinning table.

Kitchen ya shiga tana gaban sink tana wanke nama.

"A ina muka sami abinci?"

"Wani yaro ne yace inji Haj Mama"

"Allah Ya saka musu da alkhairi."

"Amin"

Shiru taji na dan lokaci kafin ta juyo taji shi a tsaye a bayanta.

Wani iri taji zata motsa ya sauko da fuskarsa daidai kunnenta yana mata magana kamar mai rada "apron zan saka miki kada ki bata kayanki"

Zura mata yayi ta saman sannan ya janyota jikinsa ya daure mata igiyar a kugunta.

Dena komai tayi saboda yadda take ji a lokacin ya dora kansa a kafadarta tare da zagaye hannuwansa a cikinta "cigaba da aikin Matar Dahiru"

Da kyar tace "uhmmm na koma Yaya"

"Da wuri haka ba notice"

"Eh ni dai na koma" tasan idan suka cigaba da zama a haka da wuya ta iya karasa aikin. Soyayyarsa na ranta da kuma fargabar da take kasan zuciyarta.

"A bani rabin minti please"

Wuyanta taji yana sumbata ko ta ina sannan ya daure ya rabu da ita ba don yaso ba.

"Yaya in

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login