Showing 54001 words to 57000 words out of 153671 words
Chapter 19 - GA IRINTA NAN Hausa Novels By Binta Umar Abbale.txt
insha Allahu gobe zan shigo da wuri muyi sallama."
Nace."To shikkenan sai kazo din a gaishe min da yarana." ya amsa da fadin"Zasuji da kyau insha Allah." sallama mukayi da juna na kashe wayar na koma cikin gidan.
Cikin nutsuwa na nemi guri na zauna ina kallonsu duk sun shiga yanayi na damuwa nace."Gwaggo ku kwantar da hankalin ku Allah ya kawo mana mafita domin kuwa yanzu muka gama waya da Alhaji Nuran yake sheda min cewa tafiya ta taso masa zuwa chana sabida haka za'a daga daurin aure sai bayan ya dawo wata uku zaiyi a can ko hud'u insha Allahu yace cikin satin da ya dawo sai a daura auran.
Gwaggo tace."Kai alhamdulilahi amma naji dadin wannan magana wallahi dama bayan fitar ki muna ta tararrabin yanda za'ayi a tunkareshi da maganar sai gashi cikin sauki Allah ya kawo mana mafita."
Kawu yace."amma kuma kamata yayi yazo ya same ni mu tattauna maganar a tsakaninmu.
Nace."Eh hakan yace insha Allahu gobe zai zo kuyi maganar." Gwaggo tace."To kaga shikkenan sai ka jira zuwansa kada ka fita kuma kuyi sa'bani."
Yace."Insha Allahu zan zauna nayi jiran zuwan nasa. Mi'kewa yayi da fad'in zai fita ya sha iska a waje." Gwaggo tace."Haba ai zafin ya isa muma yau kwanciyar tsakar gida zamuyi ai." Kawu yana kokarin saka takalmansa yace."Hakan yayi gwaggo ke Sa'ida sai ki fito ki dan gyara muku inda zaku kwanta din." Nace."To shikkenan." mikewa nayi na fito tsakar gidan domin na gyara mana inda zamu kwanta.
To kamar yanda dai Alhaji Nura yayi alias a run zuwa gurin Kawu su tattauna maganar haka din ne ya kasance domin Kawu a daran ranar ya kira wayar Alhaji Shamsu mijin mahaifiyata ya sheda masa dukkanin abinda yake da akwai Alhaji Shamsu yace babu damuwa insha Allahu zai fito da wuri ayi zaman dashi.
Sun tattauna abinda ya dace a tsakaninsu tinda dukkaninsu ba yara bane sun san harkokin kasuwanci mussaman Alhaji Shamsu shi ya 'kara karfafawa Alhaji Nura gwiwa akan tafiyar tasa amma kuma sai yace mai zai hana kawai a daura auran idan yaso in ya dawo sai ayi maganar tarewa.
Lokacin da yayi wannan maganar Kawu Iro hankalinsa ne ya tashi yayi shuru yana sauraran yaji amsar da zai bashi Alhaji Nuran yace yafi so ayi komai a lokacin da yake nan." Alhaji Shamsun yace to shikkenan babu damuwa Allah yasa hakan shi yafi alkairi."
Dukkaninsu suka amsa da ameen ya Allah ." suka rabu cikin mutumci da girmama junansu.
****
*Bayan sati biyu*
Khalid da Salmanu mota suka bi da kayansu da kuma guzirin su domin zuwa Lego's dan su nemi aikin yi su kuma cigaba da gudanar da harkokinsu na buga kwallo a cewarsu duk inda ta fad'i sha ne, Salmanu lafiya lau suka rabu da mahaifiyarsa da da sauran 'yan uwansa shi kuwa Khalid babu sa albarka uwa da uba ya d'auki irin wannan tafiya aikuwa cikin dare suna tsakiyar titi motarsu na sharara gudu *da'u fataken dare!* ('Yan fashi) suka tare musu mota yana ganin haka yayi saurin bude wayarsa ya cire sim card dinsa yasa a bakinsa ya danne a kasan harshen sa......'Yan fashin suka dinga sakin harbi! ta ko'ina suka sanya dik wa'inda suke motar mata da maza suka fito suka kwanta a tsakiyar titi duk motar da ta karaso gurin sai sun tsayar da ita sun fito da mutanan ciki.....Daya bayan d'aya suka dinga binsu suna kar'be musu wayoyinsu wa'inda sukayi gardama a cikinsu suyi musu dukan mutuwa ganin haka yasa mutane suka tsorata domin tsira da ransu da lafiyarsu suka dinga mika musu wayoyinsu da jakkunan kayansu da guzurinsu.
Sai da suka kwace musu komai suka loda cikin motocinsu sannan suka dawo gurin da suke kwance suna haskasu.........Babban cikinsu ya tsuguna kusa da wata mata ta rungume d'anta sai kuka take ta hada uban gumi jikinta sai karkawa yake.
Fuskarta ya haska sosai yake 'karewa jikinta kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin akwai mamora a jikinta yasa ya kira daya daga cikin 'yan uwansa ya nuna masa ita da fad'in "Zamuje da ita mu biya bukatarmu."
Matar ta fashe da kuka tana waiwayen bayanta mijinta take nema can ta hangoshi ya rarrafo gurin cikin fitar hayyaci yace."Oga dan Allah kada kuyi mata wani mummunan abu ni ne mijinta tunda dai kun samu abunda kuke bukata shikkenan."
Wani wawan mari ya kwad'a masa a take hancinsa ya fashe da Jini yasa kan bindigar dake hannunsa ya dinga dukan kansa da mugun karfi har sai da yaga galabaitar dashi tukkuna ya kyaleshi ya fad'i a gurin jina jina dashi! matarsa da 'yarsa sai kuka suke a kansa.........Fizgo hannunta yayi ya hau janta a k'asa ta dinga ihu tana fad'in "Ku taimaka min kada ku bari ayi zina dani." 'Kwakkwaran motsi babu wanda yayi a gurin mijin nata ya rarrafa ya mike domin ceton matarsa dan fashin ya kai masa wawan duka ya fadi a gurin a sume.
Khalid yayi shahada ya mike da saurin gaske yace."Kai bawan Allah kaji tsoron Allah kuji tsoron ranar had'uwa dashi shin wai baka san matar aure ce ba kada kuyi zina da ita da nauyin aure a kanta Allah ba zai barku ba.
A sukwane! sukayo kansa dukkaninsu! Salmanu ya shiga tsananin tashin hankali ya dinga jan hannun Khalid din wai ya tsuguna ya basu hakuri Khalid ko gezau beyi ba yana tsaye suka karaso gurin babban cikinsu ya daga hannunsa zai kwada masa mari Khalid da sauri ya rike hannun.......Cike da mamaki jama'ar gurin suke kallonsa. Kafin kiftawar ido yaji saukar wani mugun duka a tsakiyar kansa...ihu! ya kurma yayin da lokaci guda yaji wani dummmm! a kunnesa tangad'i ya farayi Salmanu ya mike a zabure! yayi nufin rikeshi Danfashin da yake bayansa ya bangajeshi ya fad'i! 'katon dutsen dake hannunsa ya sake bugawa Khalid a kansa a take ya fad'i a gurin ya suma gefen kansa ya fashe sai zubar da jini yake........Fitilolinsu suka kashe gurin yayi duhu! dumd'um! suka ja matar nan tana kurma ihu! suka sanyata a motarsu suka tafi da ita.....
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*35&36*
Cikin tsananin tashin hankali Salmanu ya nufi inda Khalid ke kwance ya tarairayoshi jikinsa yana kiran sunansa, Jama'ar dake gurin suka rufo kansu gurin ya hargitse da kace nace kowa yana fadar albarkacin bakinsa akan abinda ya faru Salmanu shi dai babban damuwarsa abokinsa ya farfado! direban motar ne ya karaso gurin hannunsa rike da jarkar ruwa ya bude da saurin gaske ya shiga tuttulawa khalid ruwan a jikinsa, yana gamawa dashi da sauri ya karasa inda mijin matar nan yake a kwance shima ya daga jakar ruwan ya kwara masa a jikinsa cikin ikon Allah gabad'ayansu suka farfad'o cikin jigata Khalid ya dinga kiran sunan Allah yana jin yanda kansa ke wani irin sarawa! hannu yasa saman goshinsa ya shafo jini Salmanu yace."Sannu Khalid ai ka auna arziki." kallonsa kawai yayi ya juya yana kallon jama'a dake gurin suna surutai da hayaniyar kowa sai gyara jakar kayansa yake Yace."Salmanu ina matar nan take bana so su cutar da ita."
Salmanu yace ."Sai dai hakuri ai sun tafi da ita."
Kansa ya dafe yana kiran sunan Allah! Ihu! mai karfi sukaji da sauri ya dago kansa mijin matar nan ne yake kurma ihu mutane na rirrikeshi wai sai ya tafi neman matarsa jamaa sun hana shi ga 'yarsa sai sandara ihu take itama.
Khalid cikin karfin hali ya mike Salmanu yace."Ina zakaje Khalid kai ma fa kana bukatar taimako.
Yace."Salmanu mutumin can ya bani tausayi zanje na rarrashe ne."
Kafin Salmanun yayi magana ya bar gurin Salmanu yabi bayansa zuwa inda mutumin ke zaune jamaa sun kewaye shi suna bashi hakuri.
Khalid ya dafa kafad'arsa ya dinga rarrashin sa kancewa yayi hakuri ya barwa Allah insha Allahu Allah ba zai basu nasara akan matarsa ba.....Yana kuka yace."Matata ciki ne da ita d'an wata uku gashi bata da cikakkiyar lafiya mahaifiyarta na Lego's ta matsa min da cewa tana so taje ta gaisheta hakika dana san wannan tsautsayin zamu hadu dashi to da ban amince da tafiyar nan ba.
Khalid yace."Kayi hakuri abokina dukkanin abinda kaga ya faru da kai da matarka rubutacce:ne daga Allah kayi mata addua kawai akan Allah ya ku'btar da ita.
Kansa ya sunkuyar kasa hawaye masu zafin gaske suna zubo masa hakika yana son matarsa so mai tsanani yana jin tsoron 'yan fashin nan su haike mata su kasheta da wahala.
A firgice ta tashi zaune tana rarraba idanuwanta a dakin kafin ta fara lalube kan shimfid'arta salati takeyi a zuciyarta tana kiran sunan Allah.
Fitilar ta ta kunna dakin yayi haske jiki a sanyaye ta mike ta dauki buta ta fita bandaki ta shiga ta kama ruwa ta fito garin yayi tsit Allah yana saukar da ikonsa.
Alwala ta d'aura ta shiga dakin ta gyara dadduma ta tayar da sallah.
Nafila tayi raka'a biyu tayi sallama sai ta daga hannunta sama hawaye ya 'kwace mata tana kuka take fad'in "Ya Ubangiji Allah ka karkato da hankalin yaron nan gida Allah ka yafe masa kada ka d'ora masa mummunar kaddara Allah Khalidu mai laifi ne a gurinka Allah ka sassauta masa Allah kada ka jarrabe mu da abinda ba zamu iya ba." Kuka ne yaci k'arfinta hannuwanta a sama ta kasa saukewa.
A tsorace na mike zaune ina kallonta gabana na faduwa nace"Gwaggo lafiya meye kike kuka me ya faru."?
Adduar ta shafa a fuskarta murya a dushe tace."Sa'ida dan Allah da Annabi ki yafe wa Khalid abinda yayi miki kaddara ce ki yafewa dan uwanki ko ya samu sassauci.
A sanyaye nace."Gwaggo me ya faru dashi.?
Tana rawar murya tace."Mummunan mafarki nayi dashi Sa'ida amma kafin na farka daga baccin na manta ni dai nasan na ganshi cikin mawuyacin hali jina jina da jini.
Gabana ya fad'i! nace."Gwaggo mafarki ba gaskiya bane ki daina gazgazata shi." Girgiza kanta tayi tace."Sa'ida ni bazan kira kaina waliyyiya ba ba kuma zan kira kaina 'yar baiwa ba amma Allah yakan nuna min abu a mafarkina mai dadi ko mara dadi kuma mafarkin yakan zama gaskiya ko mutuwa za'ayi Allah yakan nuna min a mafarkina shiyasa hankalina ya tashi da yin wannan mummunan mafarkin.
Shuru nayi har yanzu kuma ban daina jin faduwar gaba. ta cigaba da cewa "Dan Allah kice kin yafe masa ko ya samu sassauci." A sanyaye nace"Gwaggo tuntuni na yafe masa ki kwantar da hankalin ki."
Tace."To nagode sosai Allah yayi miki albarka na amsa da ameeen ya rabbi.
Kasa komawa bacci mukayi har asubah tayi mukayi sallah muna idarwa tace lallai wai sai na kira mata shi a waya, to nima nawa 'bangaran jikina yayi sanyi da al'amarin ban yi mata musu ba na kunna wayata na fara laluben number sa.
Na kira sau kusan biyar bata shiga, nace"Gwaggo kin dai ji da kunnanki wayar taki shiga ko."
A sanyaye tace."Watak'ila sun kashe shi." naji gabana ya yanke ya fad'i!
Kallonta nayi hawaye na kwarara a fuskarta tace."Sa'ida na d'an tuno mafarkin ganin sa nayi wasu mutane masu baka'ken kaya sun zagaye shi da bundigogi a hannunsu suna ta dukansa."
Nace"Gwaggo ki samu nutsuwa dan Allah in sha Allahu Khalid na raye cikin koshin lafiya."
"Kayya! Sa'ida bana tsammanin yaron nan nada rai.'' nace" Bari gari ya waye sai a sake kiran wayar tashi."
Tace."to shikkenan." tagumi! ta zabga har yanzu hawaye take cikin zuciyata nace ko wane irin so da kauna take masa.....Nace"Gwaggo yau ba zaki kunna redio ba."?
Kanta ta girgiza min na dauki redion na kunna mata na ajiye mata kusa da ita.
Dauka tayi tana kokarin kashewa tace."Sa'ida rabu dani nayi salati a zuciyata yau bana sha'awar jin redio nafi bukatar na samu nutsuwar zuciya nayi wa yaron nan addua.
Nace"Hakane Allah ya kare shi." ta amsa da ameeen ya rabbi.'' Mikewa nayi na fita tsakar gida domin d'ora ruwan wanka, sai naji motsin fitowarta na jiyo ina kallonta naga tana sa takalmanta da kudi a hannunta.
Nace"Ina kuma zakije da sassafe haka'' Tace."Zanje gidan Marka mai waina na siya domin nayi wa almajirai sadaka."
Shuru nai ina kallonta har ta fita daga gidan na girgiza kaina tare da cigaba da abinda nake.
Har nayi wanka na fito nasa kaya na Gwaggo bata dawo gidan ba, na zauna cikin damuwa na dauki mai ina shafawa a jikina Kawu Iro ya daga labulan dakin, da sauri na gaisheshi ya amsa cikin kulawa yana fad'in "Gwaggo tana bandaki ne."?
Nace." Aa ta d'an jima da fita wai taje gidan Marka siyo wainar gero."
Yana kokarin magana ta shigo gidan. Kawu Iro Kallo guda yayi wa mahaifiyar tasa jikinsa ya mutu ganin yanda ta zabge idunuwanta sunyi fululu.
Yace."Gwaggo lafiya me yake faruwa."? Hawaye suka 'kwace mata tace."Ibrahim babu lafiya domin kuwa Jiya a zaune na kwana tunda nayi mummunan mafarki da yaron nan Khalid na kasa rintsawa.
Yace."Gwaggo dan Allah ki cire damuwar Khalid daga cikin ranki kada ki janyo wa kanki ciwo mai tsanani.
Tace."Ibrahim idan kaga na cire Khalid a raina to mutuwa nayi amma ba zan ta'ba daina damuwa dashi ba.''
Tana gama maganarta ta wuce gurin Ummatu.
Ummatu na tsaka da dama kunu ta ganta ta shigo kicin din, gabanta ya fadi! tunda suke a gidan sai ta irga iya adadin shigowarta gurinta bai fi uku ko hudu ba Allah dai yasa ba wata masifar bace.
"Gwaggo ina kwana."? tafada babu cikakkiyar sakewa.
Gwaggo cikin kulawa ta amsa da fadin" Rabi gurin ki nazo.'' Ummatu ta saki ludayin da take dama kunu dashi tana kallonta .
Gwaggo ta 'kas'kantar da kanta da fad'in "Dan Allah Rabi'atu ki gafarci yaron nan kiyi hakuri ki masa addua Akan Allah ya sassauta masa domin jiya ni nasan mummunan halin dana ganshi a mafarkina.
Ummatu jikinta yayi sanyi tace." Gwaggo dama ai ni ban 'kullaci Khalid ba tunda dama ban yarda da zargin da kuke masa ba.
Tace."To hakane to amma dan Allah ki dage dayi masa addua saboda bakin uwa albarka gare shi ki daina zuwa kina asarar kudin ki a banza addua zaki masa da kyakykyawan fata."
Ummatu tace."To shikkenan Gwaggo insha Allahu zan cigaba dayi masa addua.
Tace."Bari na tsaya na tafi da kunun tunda naga kin gama damawa." Ummatu tace."Aa Gwaggo kije kawai zan kawo muku." Gwaggo 'kin tafiya tayi har sai da Ummatu ta zuba musu kunun a jug ta zuba musu awara mai yawa a silba Gwaggo ta dinga shi mata albarka kamar basu ta'ba samun sa'bani da juna ba Ummatu ta dinga mamakin al'amarin domin tunda suke da Gwaggon bata ta'ba kwantar mata da kai irin yau ba gashi har da ya sanya mata albarka gaskiya dole al'amarin ya bata mamaki.
'Dakin ta shigo ta same ni na gama shiryawa tace."Sa'ida ga kunu nan da zafin sa ki zauna kisha kafin ki tafi.''
Da mamaki! a tare dani nake kallonta kafin nace."Yau da kanki kika kar'bo kunun."? Tace."Eh gani nayi ta gama damawa shiyasa na tsaya na tawo dashi.
Shuru nayi na samu cup na tsiyayi kad'an a warar ma uku na dauka na zauna ina kur'ba, tace"Ki sake kiran wayar tasa mana.
Ba tare dana ce komai ba na dauki wayar na shiga duba number tashi....Kamar dazu wayar ta katse ta'ki shiga.
Nace."Gwaggo sai dai kiyi hakuri fa domin wayar nan ta'ki shiga.kallona take nace." Dan Allah ki daina wannan kukan Gwaggo mutuwa dai ake Jin tsoro idan Kwanan sa ne ya 'kare Allah ya jikansa.
Tace."Sa'ida amma baki da tausayi da imani yanzu sai kiso Khalid ya mutu a wani guri ai idan ma lokacinsa ne yazo nafi bukatar ya mutu a gabana hankali na sai yafi kwanciya idan naga gawarsa.
Nace."Yanzu ma idan mutuwar yayi kina zaune labari zai same ki kuma za'a kawo miki gawar sa har gida.
Ta dinga kuka tana watsa min harara, dariya na kunshe a gurguje na gama abinda nake nayi mata sallama uffan ba tace min ba har na fita daga gidan.
Sai da gari ya waye tukkuna suka samu damar komawa cikin motar kowa ya zauna a gurin zamansa jikinsu duk yayi sanyi da irin 'barnar da 'yan fashi sukayi musu Khalid baiji takaici sosai ba saboda yasan ya tsira da sim card dinsa da 'yan tufafinsa amma duk guzurin kudin da Sukayi shi da Salmanu 'Yan fashin nan sun hargitsa musu kaya sun kwashe a yanzu ko sun sauka a garin na legos sai Sunyi fafutuka tukkuna.
Motar tayi shuru kowa na sake-sake a cikin ransa yayin da direben ke ta sharara guda akan kwalta, tun kafin su karasa inda matar take kwance a gefen titi Mijin nata yake ihu! da fadin"Innalillahi wa'ina ilaihi raji'un gatacan a kwance sun kasheta.''
Direban suna karasawa inda take ya fara kokarin parking ko kafin ya 'karasa mutumin ya fit ya fito a take ya gangara k'asan wani rami mai Mugun zurfi! gaske.
Hankalin su Khalid ya tashi mutuka hakika tunda yake bai ta'ba ganin masifa da tashin hankali irin na yau ba wannan mugun ramin da mutumin ya fad'a ciki ai sai dai wani kuma, wasu suka nufi inda matar take kwance wasu kuma Sukayi dafifi! a bakin ramin da mutumin ke ciki sai salati suke suna tunanin ita ina zasu taimakeshi.
Khalid yayi masifar tsorata da ganin matar da babu rai a tare da ita har ta fara kumbura ga jini duk ya bushe a jikinta kud'aje da 'kwarika sai bin jikinta sukeyi.......Yarinyar ta na gani uwarta sai ta tsandara ihu!! ta shiga tsakanin mutanan tana
17, October 2025
Fatima
Wow