Showing 99001 words to 102000 words out of 153671 words
Chapter 34 - GA IRINTA NAN Hausa Novels By Binta Umar Abbale.txt
bashi auran 'yarmu."
Yace."Nifa ban fahimce ki."? A nutse ta warware masa abinda yake faruwa....Yace."To ai ba laifi bane don anyi daurin aure babu ango a kusa sau tari hakan na faruwa kuma hakan ba yana nufin cewa aure bai d'auru ba aure ya dauru mutukar an d'aura shi akan tsari da shedu da kuma waliyyai sabida haka don Allah ki daina wannan surutan."
Gwaggo shuru tayi tana kallonsa mamaki dan'kare a zuciyarta tace."Khalid kai kake fadar wannan maganar kanka tsaye yaushe Allah yasa maka dangana haka."?
Murmushi yayi yace." Tuntuni Allah yasa min dangana Gwaggo ai na barwa Allah komai na hakura da Aunty Sa'ida tunda ba alkari ce a tare dani ba."
Zaune na mike ina kallonsa sam banji dadin maganarsa ba. kallona yayi na second guda ya dauke kansa agogon hannunsa ya duba da fadin."Ni zan dan fita gurin abokaina." Tace."To shikkenan sai ka dawo." Ba tare da yace komai ba ya bar gurin.
Kaina na sunkuyar kasa ina mamakin sadudar yaron ikon Allah lokaci guda yayi sanyi ya mikawa Allah lamarin duk tsananin kishi irin na Khalid wai shine yake musabaha da wanda zan aura hakika al'amarin ya bani mamaki mutuka.
To kamar yanda ango ya tsara al'amarin hakane ya kasance kwanasa biyu da tafiya kasar india aka daura auran kuma a ranar na tare a dan'kareran gidana dake Unguwar Jambulo gida gari guda komai na more rayuwa akwai a gidan Yaya Aminu jin dadi dai na duniya na sameshi sai dai fatan zaman lafiya Layuza da Karima 'kannansa su aka turo domin su taya ni zama kafin ya dawo naji dadin zuwansu sosai dama mun saba dasu tunda ina ziyaryar gidansu sa'i da lokaci, bamu da fargabar komai gidan tunda akwai matakan tsaro a gidan sosai akwai securities masu dagi da karninuka a Estate d'in.
*72&73*
A ranar da Gwaggo tazo gidan sai da ta kusa bani kunya gabansu Layuza sai wasu irin maganganu takeyi akan gidan da kuma maigidan sai da nayi mata jan ido tukkuna tayi shuru da bakinta tana yin sallar azuhur tace ita tafiya za tayi abubuwan kwad'ayi na had'a mata masu yawa nasa direba ya dauketa ya kaita har gida, Gwaggo koda ta koma gidan kasa shuru tayi da bakinta da Kawu Iro ya shigo ta tare shi da maganar wai anya kuwa A harkar kasuwanci Yaya Aminu ya tsaya baya yakan kai wannan uwar dukiya daka gani bata Allah da Annabi bace." Kawu Iro zaunar da ita yayi ya dinga yi mata nasiha gami da kawo mata misalai Allah yakan arzita bawansa da dukiyar da bai san iya adadinta ba saboda haka ta kwantar da hankalinta duk wani binkice yayi ya kuma tabbatar da cewa mutumin a harkar kasuwanci ya tsaya." Gwaggo dai shuru tayi da bakinta tana jajanta al'amarin.
Gwaggo kullum za tayi girkin ta da nama taci ta koshi ta ajiyewa mutumin nata idan ya dawo tace masa yazo yaci abinci kai tsaye yake ce mata ba zai ci ba ya gwammace yaci garau-garau din da mahaifiyarsa tayi ko kuma yaci aljihunsa.....Gwaggo tayi tai masa naci shi kuwa yace."Ba zai ci ba dole take hakuri ta kira almajirai ta raba musu sadaka.
"Khalid kwata-kwata fa ni ban amince maka da wannan tafiyar ba, kai harkar ball din ma gabadaya bana sonka da ita ka hakura ka zauna a gida ka fara kasuwanci shine yafi alkairi a tattare da kai.
Cikin wani irin yanayi na damuwa yake kallon mahaifin nasa yace." Baba kayi hakuri ka lamunce min tafiyar nan akwai nasara a cikinta.
Kawu Iro yace."Ai dama duk hanyar shaid'anci zaka samu nasara a tare da ita hanyar Allah da Annabi kuwa kun dinga kawo suka a cikinta to ni dai na gama magana mutukar ni na haifeka ban lamunce maka tafiya wata america ba.
Kawu Iro na gama maganarsa ya bar gurin.....Ya jima a tsugune a gurin yana sa'kawa da kwancewa kafin ya mike kai tsaye gurin Gwaggo ya nufa domin kuwa yana ganin itace kadai zata iya tursasa mahaifinsa ya barshi ya tafi inda yake muradi.
Tana zaune da kwanon farfesun kaji a gabanta gefe ga lemo nan irin na kwali farfesun take sha hankali a kwance Gwaggo har wani qiba tayi saboda ka'bakin arzikin da Sa'ida take kawo mata duk bayan kwana uku ko hud'u......Dakin ya shiga ya zauna yana kallonsa....Sai ta tura masa kwanon farfesun da fadin."Gashinan ko kayi sha'awa."
Girgiza kansa yayi yace."Bana bukata." Kwanon farfesun ta janye ta cigaba dasha tana tauna tsokar data dahu luguf.
Yace."Gwaggo Alfarma nake nema a gurun ki." Tace."Ai dama tinda naga ka shigo dakina ka zauna nasan da walakin goro a miya.
Sajensa ya shafa yace."Eh wallahi Gwaggo ke kadai ce zaki umarci Kawu Yayi abinda kike so."
Tace."Eh kwarai kuwa ai mahaifinka yana da biyayya duk abinda nace inaso to shima yana so.
Yace." Yawwa Gwaggo dan Allah kice masa ya barni na koma gurin sana'ata."
Tace."To akan me dama zaice ba zaka koma ba."? Yace."Kin san kwanaki nayi miki magana kancewa zamuje america muyi wasa to tafiyar ce ta taso dan tun satin da ya wuce oganmu yake kiran waya ta na bashi hakuri kancewa insha Allahu ya tsammaci zuwa na a cikin satin nan to kuma yanzu da nake shedawa Kawun maganar yake cewa shi bai amince ba.
Tana sud'e hannunta tace."Khalid wace irin ball ce har sai anje america mai zai hana ka ka cigaba da buga abarka a cikin 'kasar ka nima wallahi sam bana sonka da wannan harkar.
Yace."Gwaggo kada kice haka mana zuwa na america matakin nasara ne domin kuwa zanje mu fafata da manya manyan 'yan ball wanda suka shahara sukayi suna duniya tasan dasu."
Hararasa tayi tace."Kai kuma shahara kake nema da makiya Allah da Annabi kenan."? Girgiza kansa yayi da sauri yace."Aa Gwaggo ai ba kafurai ne kawai ba harda musulmai a ciki kowa yana kokarin ya nuna bajintarsa ne."
Shuru tayi masa ya matsa kusa da ita gami da rike hannunta yana rarrashinta. Tace."Shikkenan ka kwantar da hankalin ka zan sameshi muyi magana Allah ya za'ba maka abinda yafi alkairi."
Cike da farin ciki ya amsa da ameeen Uwargidana." Harararsa tayi tace."Ina uwargidanka amma ka daina cin abincina ko da yake ai nasan uwarka ce take zuga ka." Cikin kulawa ya kalleta da fadin."Gwaggo babu ruwan Ummatu ni ne dai ba zanci wani abu da ya shafi aunty Sa'ida ba kin san haka tsarina yake ba tun yau ba.
Tace."In banda abinka kuma wane kishi za kayi bayan komai ya wuce kake cutar kanka." Yace."Kinga Gwaggo dan Allah a bar maganar duk nau'in abincin da nake so naci ina da kudin siya ba sai kin tursasa ni naci abincin ki ba.
Tace."To ai shikkenan tunda haka ka za'ba, mi'kewa yayi yana kallon agogon hannunsa yace."Ni zan fita gurin abokaina." Tace."To sai ka dawo." Fitowa yayi tare da sa takalmansa ya fita daga gidan.
Kullum ta Allah Yaya Aminu yakan kira waya ta sau biyu ko uku mu jima muna hira dashi al'amarin ya dinga bani mamaki ganin gabadaya baya nuna wani d'oki da zumud'in irin na angwaye idan ya kira waya ta hirar kasuwancinsa kawai yake min babu wata kalma mai dadi irin to so da nuna cewa ina bukatar ki abin ya dinga bani mamaki yana sani a cikin damuwa! a gaskiyar magana lamarin yana min ciwo sabida ni na kasance mace mai son soyayya inaso naga namiji na kula dani da nuna min so......Amma Yaya Aminu sam babu wannan a tare dashi shidai harkokinsa yasa a gaba.
Yau asabar Allah yayi nufin dawowarsa sosai nayi gayu cikin shaddan galila taji uban stone work nayi ado da gold wuya da hannu sai zuba kamshin tururuka nakeyi ni kaina dana tsaya gaban mirror sai da nayi mamakin uban kyawun da nayi......Amma abin mamaki wanda akayi kwalliyar dominsa bai wani kula sosai ba dan bayan na bashi abinci yaci dakinsa ya bude ya shiga ya kwanta, sai nayi tunanin binsa dakin koda na ta'ba kofar sai naji a kulle. jiki a sabule na bar gurin zama nayi kujerar falo abin duniya ya dame ni, ga Layuza da Karima sun tafi sai ya kasance ni kadai a gidan dana gaji da zaman falo mikewa nayi na shige dakina na kwanta kawai sai hawaye suka 'balle min wannan wane irin ango ne mara kula. sosai naci kuka na na koshi bacci ya dauke ni.
Sai daf da la'asar na tashi a gurguje nayi wanka na fito daure da alwala sai dana kimtsa jikina tukkuna na tsaya kan dadduma na tayar da sallah.
Ina sallama ya shigo dakin daga kai nayi ina kallonsa kamshin turaransa duk ya cika dakin a shirye yake da alama futa zaiyi.....zama yayi gefan gado har na shafa addua na juyo muka hada ido dashi, murmushi yayi min da fadin"Amarya." ya'ke kawai nayi naje na zauna kusa dashi tare da gaishe shi, ya amsa cikin kulawa ido ya tsira min kafin yace."Naga idanuwanki sunyi jawur ina fata ba wata matsala bace."
Daurewa nayi nace."Babu komai bacci nayi shiyasa idon ya sanja." Yace."Okey to ya kike ya zaman kadaici." Mirmushi kawai nayi ban tanka masa ba.
Ya kalli agogon hannunsa da fadin."Ni zanje babban gida mu gaisa dasu." Nace."To ka gashe min dasu." Mikewa yayi yana fadin."Insha Allahu zasuji sa'kon ki.
Bayansa nabi da kallo har ya bude dakin ya fita.....Jingina baya na nayi jikin gadon na shiga tunanin rayuwa.
Sai kusan tara da rabi ya shigo gidan, gani na a zaune a falo ya bashi mamaki yace."Baki bacci ba."? A nutse na mike da fadin."Eh na tsaya ka dawo ne." Murmushi yayi na kar'bi wayoyinsa ina masa barka da zuwa.
Amsawa yayi ya rike hannuna muka nufi dakinsa.
Da kaina na hada masa ruwan wanka yana ta sa min albarka na fito masa da jallabiya da gajeran wando na ajiye kusa dani.....Daure da towel ya fito sai yayi saurin dauke kansa a maimakon ni naji kunyar ganinsa a haka sai ya kasance shi yake jin kunyata, dan sai naga kamar a tsarge yake tsayawa yayi bakin kofar toilet din da fadin."Bani kayan nan." Da sauri na mike da kayan a hannuna na kai masa, kawai sai naga ya koma toilet din ya banko kofar. sakato nayi da baki ina mamaki!
Ina nan tsaye ya fito ya wuce ni ba tare da ya tanka ba, a sabule nabi bayansa falon sai na sameshi zaune a kasan kafet yana duba loptop. zama nayi a hankali nace."Ba zaka ci abinci ba."?
Hankalinsa nakan Loptp din yace."Bari na rage aiki tukkun." shuru nai kawai na zuba masa ido ina mamakin al'amarinsa.
Kusan rabin awa yana aiki a loptop din kafin ya rufe a nutse ya kalle ni da fad'in "Tashi muje dainng din ki bani abincin." Mikewa nayi ya biyo bayana.
Tsaf na shirya masa abincin na tura masa gabansa zama nayi ina kallonsa yana cin abincin yana amsa waya
Nace."Yaya Aminu kayi abu d'aya mana ka ajiye wayar kaci abinci sai hakan yafi.''
Ba tare da ya kalle ni ba ya cigaba da wayarsa.....Ji nayi raina ya 'baci sai kawai na miqe na bar masa gurin.
Koda ya kammala cin abincinsa zuwa yayi ya dauki loptop dinsa bece min uffan ba ya bude dakinsa ya shige! ni dai mamaki ne ya kusa kasheni a gurin da kyar na iya kai kaina daki na kwanta.
Haka rayuwar mu ta cigaba da tafiya tsayin wata guda da dawowarsa babu wata mu'amula ta aure data ta'ba shiga tsakanina dashi Kullum a dakinsa yake kwana a garkame! gabadaya ma ya daina yarda na ra'bi inda yake dan duk kokarin da nake masa idan ya dawo daga kasuwa sai ya dakatar dani yace naje na huta shima Allah ya bashi lafiya zai iya had'a ruwan wankansa.
Ganin wulakancin yayi yawa yasa na daina shiga dakinsa sai dai idan ya fito mu gaisa ya kama hanya ya fita.......Gashi kamar mara tunani kullum sai ya tura min kudi accont d'ina al'amarin dai sai kace hauka! kuka naci na koshi na yanke shawarar tun kararsa da magana domin dai ni na gaji ba auran kudi nayi ba halastaccan aure nayi irin wanda Allah yake so......Sai da ya fito falon sannan nima na fito daga dakina na sameshi a zaune yana abinda ya saba lissafi da amsa kiran waya cikin zuciyata nace."Ban ta'ba ganin sahoramin namiji irinka ba. Wayar hannunsa ya kashe ya kalle ni da fadin."Kina da wata bukata ne."? a nutse nace."Eh ina da ita." Ya zuba min ido da fadin."Ina sauraranki." Murya na rawa nace."Yaya Aminu wai me kake nufi ne."? Cikin wani irin kallo yace."Bangane ba."? Na d'aure fuska tamau! nace."Shin dutse ka ajiye a gidan ka kome? ko kana da lalura ne."? Tsira min ido yayi yana kallona na sake cin kunu da fadin."Tsayi wata d'aya da sati biyu nake cikin gidan nan naci na koshi naci nama nasha madara nasha nono na kwanta a Ac me kake tsammanin zai faru." ? Dariya yasa yana kallona, sai kawai hawaye suka 'kwace min. Nace."Wato saboda kai baka da damuwa ka maisheni mahaukaciya kana min dariya ko to wallahi na gaji ni zan samu mahaifiyarka na fad'a mata halin da ake ciki." Da sauran dariyar a fuskarsa yace." Ai ba sabon abu bane a gurinta idan kin fada mata tuna mata kikayi domin tafi kowa sanin matsalata." Hannu nasa na share hawaye da fadin."To me yasa kasan kana da matsala ka amince da aurena."? Jim yayi kafin yace."Kawai bana so na bijirewa umarnin mahaifina ne." Cikin takaici nace."To kawai daga yau ka kira kanka da mace tunda ka fita daga sawun maza wato har wani fad'a kake kana da lalura to zaman me kake a haka da ba zaka nemi magani ba."? Rai a d'an 'bace yace."Ke Sa'ida kada ki fad'a min maganar banza mana." Nace."Ai gaskiya ce." Hannu ya daga min da fad'in "To tunda dai kin damu yau zan jarraba na gani." Naji wani kuttun bakin ciki ya tokare min a ma'koshi nace."Wallahi tallahi kudin ka na banza ne tunda har ka sake ka mayar da kanka haka meye amfanin neman kud'in naka kana fama da lalura irin wannan." Shuru yayi min, na dinga masa surutai ina farfad'ar masa maganar da duk tazo bakina.....A fusace! yace."Ki tashi ki bani guri idan ba haka ba wallahi ranki zai 'baci! Mi'kewa nayi na bar gurin raina a mugun 'bace.!
[3/29, 8:12 AM] +234 706 435 8270: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*74&75*
Koda na koma dakin kasa hakuri nayi raina a bace na dauki wayata number Hauwwa na nema kiranta zanyi na fada mata abinda yake damuna domin hausawa na cewa Abokin kuka shi ake fadawa mutuwa na yarda da Hauwwa mutuniyar kirki ce kuma na tabbatar da cewa ba zata fadawa kowa sirri na ba...... Cikin barkwanci tace."Amarya Amaryar Alhaji Aminu young millionaire ya kike ya amarcin.''?
'Karamin tsaki naja ciki ciki nace."Hauwwa ki daina kira na da amarya domin dai har yanzu ban amsa wannan sunan ba."
Cike da mamaki! tace."Kawata bangane ba.'' Ajiyar zuciya na sauke nace."Hauwwa akwai gagarimar matsala kizo don Allah.
A sanyaye tace."Sa'ida matsala wace iri kuma? mai kika rasa a wannan gidan da har kike kiran matsala.''
Nace."Hauwwa sai dai kinzo sai mu tattauna maganar domin a waya ba zaki gamsu ba.
A sanyaye tace."Tom shikkenan idan na taso zan shigo Allah yasa mu dace." Na amsa da ameeen ya Allah."
Motsin shigowarsa dakin naji sai nayi saurin rufe idona gabadaya bana son kallon fuskarsa dan wani irin mugun haushinsa nake ji.
Zama yayi a kusa dani yana kiran sunana, shuru nayi ban amsa ba.
Yace."Nasan idonki biyu ki tashi inaso nayi magana dake." Sai da na mula tukkuna na tashi ina kauda kaina.
Cikin taushin murya yace."Ki juyo ki kalle ni ki kuma fahimci maganata."
A hankali na juyo muka hada ido sai na hango alamun damuwa a fuskarsa.
"Sa'ida nasan na zalince ki dana amince da auranki bayan nasan bani da wani karfi irin na mazantaka bani da wani kwanjin da zan biya miki bukatarki ta aure saboda wannan dalilin. Sa'ida tunda na taso na girma na kai munzali ban ta'ba jin sha'awar wata 'ya mace ba ban san meye dalili ba mahaifiyata sosai al'amarin ya dameta duk inda taji labarin wani mai magani sai taje ta bada sadaka ta kar'bo min bana mata gardama zan kar'ba nayi amfani dashi amma duk da haka bata sanja zani ba har yanzu jiya i yau bana jin wani sauyi a tare dani kiyi hakuri insha Allahu zan je asibiti domin a duba lafiya.
Nace." Yaya Aminu mai yasa kasan kana da irin wannan matsalar ka kar'bi aurena.''? Girgiza kansa yayi yace."Na fada miki dalili na bana so na bijirewa umarnin mahaifina ne."
Ajiyar zuciya na sauke na koma na kwanta da fadin."Allah ya sawwa'ke maka." Ameeen yace tare da mikewa tsaye hanyar fita ya kama na bishi da kallo ina jin wani katon abu ya tokare min a kirji a gaskiya banga dalilin da zai sanya na cigaba da zama dashi da wannan lalurar ba dole ne na nemawa kaina mafita.
Kimanin minti ashirin da fitarsa ya sake shigowa a shirye da shirin fita ya kalle ni a nutse yace."Ni zan fita." Ba tare dana kalleshi ba nace."To Allah ya bada sa'a." Ya amsa da "ameeen ya Allah."
Ya juya ya fita daga dakin.
Sai yamma Hauwwa tazo
17, October 2025
Fatima
Wow