Showing 93001 words to 96000 words out of 153671 words
Chapter 32 - GA IRINTA NAN Hausa Novels By Binta Umar Abbale.txt
kuma akwai wani babban company da suka bude a chana suke sarrafa audiga ai bai fiye zama a gari ba.
Tace."Koda naji duba kaga irin uban lefen don Allah mutane sai gulma suke shigowa mu ba kudi muke so ba albarkar aure muke bukata.
Murmushi yayi yace."Gwaggo kenan ai mutane dama ba zaki rabasu da wannan gulmace gulmacen ba to duk dai wanda ya shigo da sunan ganin kayan lefe sai ku nuna masa shine abinda ya dace."
Tace."To Allah ya kyauta dai ya rufa asiri." ya amsa da ameeen ya rabbi tace."Yanzu sati nawa suka d'iba domin daurin aure."? Yace." Kwana bakwai ne rana ita yau kenan." Tace."To Allah ya nuna mana. " ya amsa da ameeen yana kokarin barin gurin tace." D'azu da safe kuwa Khalid yace yana kan hanya zaizo gobe ko jibi wai zasu tafi america suyi wasa."
Yace."Gwaggo Nifa bana son yaron nan da wannan harkar kafurci ne tsagwaronsa." Tace."Ibrahim nima bana so to ya zamuyi idan ya kasance anan abincinsa yake.
Yace."Dole idan yazo na zauna dashi domin bana tsammanin zan barshi ya koma Lego's din nan bare ya tafi wata uwa duniya america Buga ball da turawa ya haramta." Tace."Ai ko bada da turawa ba ma buga ball a ko'ina ne bai halasta ba kamar an tozarta ahalin gidan Annabi ne." Yace."Gwaggo ai ba kama bane Gaskiya ne duk wanda ya buga ball kamar yana buga kawunan Shirafa'u Jikokin Annabi Muhammad (SAW) wannan dalilin yasa idan ya dawo zan zauna dashi akan al'amarin.
Tace."To shikkenan Allah Ubangiji Ya za'ba abinda yafi alkairi." Ya amsa da ameeen tare da barin gurin
To koda Hauwwa tazo ganin kayan lefen itama sai da tayi mamaki mussaman data ga set din gold har biyu da 'kirar saudi dana dubai ta dinga mamakin al'amarin tana girgiza kanta ta kalleni da fadin."Ke dai Sa'ida 'kashin ki na manyan mutane ne duba dan Allah lefe sai kace na 'yar gatan budurwa."
Murmushi nayi kawai nace."Hauwwa kenan Ni wallahi yanzu duk ba wannan ne a gabana ba burina kawai naga na zauna kalau a dakin aurena dan bana so da kuruciya ta kawai a dinga lissafin min aure ina addua akan Allah yasa anyi kenan.
Tace."Ki daina wani wasiwasi da zancan zucci insha Allahu baki da matsala da Aminu tinda yana sonki zai kula dake kamar yanda kike bukata." Wannan kalaman nata suka sanya ni naji sanyi a cikin zuciyata sai kawai muka shiga tattauna yanda al'amuran biki zai kasance.
Ya kama saura kwana uku daurin aure Khalid ya dira a garin ni lokacin ma bana gidan ina gidan Hauwwa tare da masu gyaran jiki.
Kawai naji kira ya shigo waya ta dana duba sai naga number Gwaggo ce amma kuma ina daga wayar naji muryar Ummatu tana fad'in "Sa'ida sai ki zuba ruwa a kasa kisha ga Khalid a kwance yana aman jini.
Gabana ya dinga buguwa nace."Ummatu ban gane maganarki ba. Tana kuka tace."Ai dama ba zaki gane ba tunda bukatar ki ta biya ni dai idan ki kayi sanadiyar mutuwar yaro na Allah ya isa." Kafin nace wani abu ta kashe wayar.
Jiki a mace na kalli Hauwwa dake kallona nace."Wai Khalid ne ya dawo yake aman jini." da sauri tace."Aman jini kuma."? Murya na rawa nace."Eh." Tace."Sa'ida me ya janyo masa to."? cike da mamaki nake kallonta Nace."Haba Hauwwa ya kike tambayata kamar baki san komai ba."?
Tace."Ashe dai har yau be hakura ba."? nace"Gashinan kuwa mybe daya samu labarin daurin aurena al'amarin ya afku.''
Tace."Kai gaskiya wannan yaron yana nacin sonki haba ai ya dace ace ya hakura kuma tinda dai yanzu kinyi masa nisa gabad'aya ma ke jininki bana 'kananun yara bane sai ya hakura kawai."
A sanyaye nace." Zai hakura ai yaron mugun naci ne dashi bayan abinda yake bukata ya samu a gurina to menene na kulafuci." Kallona tayi tana neman 'karin baya ni a maganata, na share maganar ina kokarin mikewa tsaye.....Yarinyar dake sa min salatif a kafata tace." Aunty ya zaki tashi kuma ki zauna a cigaba da saka salatif din kada yasha iska."
Ina kokarin sa hijabi na nace."Mansura bana tsammanin zan zauna zaman 'kunshi a yanzu zanje na duba halin da d'an uwana yake ciki."
A sanyaye tace."To aunty Allah ya bashi lafiya."Hauwwa ta kalleni da fad'in." Amma zaki dawo ko."? Nace."Watakila zan dawo idan hali yayi." Tace."To shikkenan Allah ya sauwake."
Babu cikakkiyar nutsuwa a tare dani na amsa da ameeen nagode jakata na dauka da sauri na kama hanyar fita.
Yanda naga sun masa rumfa yasa gabana ya tsananta faduwa murya na rawa na kira sunansa yana kwance a kan katifa idonsa a rintse.......Jin muryar ta yasa da sauri ya bude idonsa, saurin sunkuyar da kaina nayi haka kawai naji ina jin nauyi da kunyarsa.... motsa bakinsa yake yana so yayi magana sai ya fasa ya mayar da idonsa ya rufe kawai sai ganin hawaye mukayi yana sauka a kuncinsa...
zuciyata ta karya ina rawar Murya na kalli Gwaggo da tayi firgai-furgai hawaye duk ya bushe a fuskarta nace."Gwaggo mu tafi asibiti dashi a duba shi sosai ina aman jinin da yayi."? ina maganar ina bin tsakar gidan da kallo.
Tace."Sai kawai mu zauna zaman jiran ki ai tuntuni mukaje asibiti suka duba shi suka kuma bashi magani aman jini kuma an wanke domun ke baki isa ayi miki 'karya ba.
Nace."Gwaggo me ya kawo wannan maganar ai nima ba 'karyatawa nayi ba." Dauke kanta tayi ta cigaba dayi masa firfita da maficin hannunta, tsakin Ummatu naji akaina kafin na juyo ta bar gurin tana surutai.
Girgiza kaina nayi nasa hannu na goge hawayen da suka zubo min.....Tace."Sa'ida ai kuka yanzu kika fara tunda baki da tausayi sai Allah ya sakawa wanda kika zalinta.
Shuru nai mata na mayar da hankalina kansa har yanzu idonsa a rufe yake murya na rawa na kira sunansa.
Shuru yayi bai amsa min ba, na sake kiran sunansa tare da kama hannunsa......da mugun sauri ya fizge hannunsa ya bude idonsa yana kallona cikin Sha'kakkiyar murya yace."Bana bukatar ganin ki Aunty Sa'ida I hit you i hit it !! na tsane ki! bana sonki! sai kinga sakamakon abinda kikayi min kije ki auri duk wanda zaki aura ni kuma zan mutu da sonki a cikin raina." Yana maganar yana tari da riqe kirji! Gwaggo duk ta gigice tana rirrikeshi cikin dauriya na hau katifar sosai ina kokarin rikeshi kamar walkiya ya juyo a zafafe ya hankad'e ni na fad'i a kasan gurin! da hannu yake nuna ni yana so yayi magana amma kuttun bakin ciki ya hanashi kawai sai jini muka gani ya ambulo daga bakinsa.
Ihu! na kurma! a kid'eme na sake hawa katifar na kamo shi gefan hijabi na nasa ina goge masa ina kuka wurjajan na kalleshi da fadin."Khalid ashe da gaske ne? me yayi zafi Khalid kada ka kashe kanka don Allah kayi ta wakkali ka cigaba da neman za'bin Allah.''
Zafafan hawaye ne suke sauka a kumatunsa hannu na na rawa na dinga goge masa ina kuka da fadin."Kayi hakuri dan Allah ka barwa Allah lamarin nan Khalid ka daina aman jini kada kasa mu cikin masifa.
Gwaggo da tausayin su ya isheta sai ta mike jiki a sa'bule ta shiga dakinta tana share hawaye da adduar d'auki daga Allah.
Rarrashin sa na cigaba dayi ina shafa kanshi da bayansa gabad'aya ya lafke a jikina sai ajiyar zuciya yake saukewa nauyin sa be dame ni ba ni dai buri na yayi min magana yaja bakinsa yayi shuru idonsa a rufe sai sake sakin jikinsa yake a jikina.
A hankali na kira sunansa. Ya bude idon yana kallona nace."Kayi hakuri ko."? tsira min rikitattun idanun nasa yayi nayi tsai ina karanta abinda yake cikinsu.......Babu wata alama data nuna ya dauki nasiha ta.....Hannuna na turmutsa cikin tarin suman kanshi a sanyaye nace."Khalid komai na rayuwa yana tafiya ne da ikon Allah duk yanda mutum yake son abu idan Allah baya sonsa da abun dole ya hakura shiyasa kaji ina cewa kayi hakuri ka nemi za'bin Allah Ni bana 'kin ka Khalid idan Allah ya kaddara aurena dakai duk rashin sona dole na hakura don Allah ka kwantar da hankalinka.
'Kuguna ya zagaye da hannuwansa, kallonsa nayi gabana na faduwa.........."Zaki auri wani ya 'karasa kwashe min Ni'ima ko."? yafada cikin sar'kewar murya. gabana na wani irin bugawa nake kallonsa....lumshe idonsa yayi ya sake yin release a jikina.......Bana bukatar wani banza ya ra'bi jikin ki aunty Sa'ida ke kuma gashi kina ta basu goyon baya akan hakan yanzu me kika hango a tare da wannan mutumin da zaki aura ko kudinsa kike so."?
Ajiyar zuciya na sauke ina kokarin cire shi daga jikina nace."Khalid me yasa kullum kai baka daukar nasiha ka daina barin shed'an yana tasiri a tare da kai aure nufin Allah ne.
Kansa ya d'ago yana kallona na kauda kaina da sauri! hannu yasa ya juyo da fuskata yana kallona yace."Idan na tafi amarica na tafi kenan ba zan dawo ba tunda kince na fita daga rayuwarki na fita har abadah zan barki kiyi zaman aure.
Hawaye suka kwace min nace."Kada ka yanke wannan hukuncin Khalid America ba gurin zama bane kada ka biyewa sharrin zuciya ka jefe mu a cikin masifa."
Murmushi mai ciwo yayi yace."Zama na a Najeria babban Jidali ne bana tsammanin zan iya barin ki ki zauna kalau a gidan auranki idan nayi nesa sai kinfi samun kwanciyar hankali." Sosai nake hawaye ina girgiza masa kai.....Hannu yasa yana goge min hawayen muka kurawa juna ido.....Haka kawai nake jin mugun tausayinsa na ratsa ni Khalid yana masifar sona babu shakka da maganar aurena da Aminu ba tayi nisa ba zan iya hakura na aureshi ko ya samu nutsuwa sai dai kash lokaci kadan ne ya rage a daura min aure bana tsammanin zan iya watsa mijin mahaifiyata 'kasa a ido.............."Salamu alaikum." Sallamar da muka ji itace ta sanya muka dawo nutsuwar mu. Baito ce da Jamila suka shigo gidan Baito sakin baki tayi tana kallon mu tare da tallafe ha'ba, ita kuwa Jamila ido jawur ta wuce gurin Ummatu fuuuuuuu! kamar tashin Iska.
_Nagode kwarai da adduarku masoya ciwon kai da sauqi sai dai dole ku cigaba dayi min uziri har zuwa lokacin da zan warware ina fata da yardar Allah na gama muku littafin nan kafin azimi a yanzu dai ina shan magani wannan pege din ma dauriya ce ganin kun damu da yawa yasa nayi typing din Ina rokon Ubangiji Allah ya 'kare mu da lafiya wannan zafin da muka shiga Allah kasa mu wuce lafiya NAGODE da Alfarma👏🏻_
[3/25, 9:47 PM] +234 906 667 3667: *SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*68&69*
'Kokarin cire kansa nake daga kan kirjina yana sake lafewa a cikin jikina har da sa hannu da zagaye 'kuguna. Baito ta shiga tafa hannuwa tana fad'in ''Iko sai Allah Khalid wane irin iskanci ne wannan ashe dama rashin lafiyar naka na karya ne akaje har gida aka d'aga mana hankali."?
Ina kokarin magana Gwaggo ta fito daga dakinta ganin Baito a tsaye a kanmu tana surutai yasa tace."Aa Baito kada daga shigowarki kiyi wa yara kazafi shin me kika shigo kika tarar sunayi da har kike farfad'ar maganar da bata dace ba." Kallonta tayi cikin kumfar baki tace."Na shigo na tarar dasu rungume da juna kice kada nayi musu kazafi ki duba fa ki gani har yanzu yana kwance a cinyarta shin me hakan yake nufi.''?
Gwaggo ta juyo tana kallon gurin da muke....babu kuzari a tare dani na dauke kansa daga cinyata na mike na shiga daki raina a masifar bace da abinda Baito tazo tana yi.
Gwaggo tace."Saboda kawai tana rarrashinsa a matsayinsa na d'an uwanta sai ki fassara al'amarin da wata manufa Baito kada kice zaki watsa min zuria domin ni kaf ahali na babu mai mugun hali."
Baito na kokarin magana ya daga mata hannu a kasalance yace."Baito dan Allah a bar wannan maganar ta isa haka babu wani mugun abu da mukeyi da Auntyna kada kiyi mana mummunan fassara."
'Kwafa tayi da fadin."Ai shikkenan Khalid tunda ka mayar dani shashasha naga abu da idona amma ka 'karyata ni." Shuru yayi mata ransa duk a dagule ya tsani rashin fahimta irin na kakar tasa. Baito kofar Ummatu ta nufa tana surutai Gwaggo taja tsaki da fadin"Duk wani sharrinku sai dai ya koma kanku." Baito tana ji bata tanka mata ba saboda ta riga tasan duk masifarta Gwaggo ta dame ta ta shanye.
Kallonsa tayi da fadin."Khalid ya jikin naka."? Kansa na kallon kasan katifa yace."Da sauki Gwaggo wanka nake so nayi ko naji dadin jikina."
Tace."To bari na d'ora maka ruwan zafi kayi wankan sai kasha magani ko."? Yace."To shikkenan Gwaggo nagode." Da sauri ta nufi kicin domin ta hura wuta.
Gefan gadon Gwaggo na zauna kawai na tsirawa guri guda ido gabadaya na rikice na rasa wane irin tunani zanyi hakikanin gaskiya lamarin Khalid yayi masifar tsaya min a raina kuma banta'ba tsammanin cewa son da yake min yayi girman haka a cikin zuciyarsa ba aman jini gaskiya na tsorota sosai cikin zuciyata naji ina tausaya masa domin Allah ya jarrabeshi da son abu gashi kuma ga dukkan alamu ba alkairi ne a tare dashi ba da zaiyi hakuri yayi tawakkali ya mayar da al'amuransa gurin Allah sai yayi masa kyakykyawan tukwici amma gabadaya ya kasa hakuri da kaddara gashi yana nema ya janyowa kansa mummunan ciwo.
Hawaye na goge ina girgiza kaina lokaci ya kure maganar aurena da Yaya Aminu tayi nisa saura kankanin lokaci babu yanda za'ayi nazo da wata magana dole mu hakura mu barwa Allah ikonsa amma dole a cikin 'yan kwanakin da suka rage min na saki jikina da yaron na rarrashe shi ya kwantar da hankalinsa ina ganin idan nayi masa hakan zai dan samu sassauci.
"Kinga Jamila ki daina kuka da damuwa na fada miki mutukar ni na haifi Khalid to ba zai auri wannan tsohuwar guzumar ba duk wani abu da sukeyi daurin gindi suka samu a gurin waccar tsohuwar kuma na lokaci kad'an ne tunda ai saura kwana uku a daura mata aure kinga kuwa Khalid ko yaki ko ya so dole ya hakura da ita.
Jamila ta share hawayen fuskata murya na Rawa tace." Allah Ummatu ba kiji yanda zuciyata take zafi ba na rasa abinda yake min dadi Yaya Khalid duk kuruciyarsa da wayewarsa ya rasa wacce zai mak'alewa sai sauran maza A makaranta fa kullum cikin bin ofis din malamai take suna aikata masha'a." Baito tayi karaf tace."Eh ai gashinan shima tana lalata shi yaro bashi da lafiya ta rungumeshi a kirjinta nayi magana kakar tasu ta daure musu gindi sabida rashin mutunci to wallahi Rabi tun wuri ki tashi tsaye akan d'anki dan mutukar kika zauna kina zuba ido akan duk abinda yake faruwa to zaki d'ora hannu aka sabida tsabar bakin cikin da takaici."
Ummatu tace."Baito kiyi shuru kawai da bakin ki ai da Khalid din da ita mai daure masa gindi duk zanyi maganinsu akwai lokacin da zai zo na nuna mata cewa ni nake da hakki akan d'ana sabida nice uwarsa ni na haifeshi nayi wahala dashi babu wacce ta isa tayi min iko akan ikona wallahi akan hakan sai dai duk abinda zai faru ya faru." Baito tace."Kamata yayi ma ki cigaba da neman taimako gurin malamai dan dole sai ana sa miki hannu a cikin Al'amuranki idan kina so kiga daidai." Ummatu ta shiga bin dakinta da kallo tana neman abunda zata d'aga ta siyar......."Baito yawon malam sai kana da kudi kina dai kallo yanzu bani da katifa a dandayar kasa nake kwanciya sai dai idan samiru na zan siyar."
Baito tace."To meye a ciki don kin siyar da Katifa da Samiru ai dama kafin bukata ta biya dole sai ansha wuya sabida haka wannan karon kawai idan munje gidan malam zamu sa ayi musu farraqu ma'ana a rabashi da kakar tasa haihatahaihatan!." Jamila tace."Eh Baito abinda zakuyi kenan sannan don Allah nima idan kunje kusa malam yasa masa soyayyata a cikin zuciyarsa.
Baito tace."Kada ki damu Jamila zan nema miki taimako kuma ki kwantar da hankalinki Khalid kamar ya aure ki ya gama."
Jamila mirmushin jin dadi tayi da fadin."Nagode sosai Baito.......Motsin shigowar Gwaggo gurin yasa sukayi shuru da bakinsu Gwaggo tace."Rabi kina ina ne? ki bude min dakin Khalid zan daukar masa kayan sawa yayi wanka." Ummatu da sauri ta fito daga dakin tana fadin."Gwaggo shi ba zai shigo yasa kayan da kansa ba sai kinzo kin daukar masa ni bani da mukkulin dakinsa.
Gwaggo tace." To da yaya aka samu ma yayi wankan kin san jikinsa babu kwari shiyasa na karbi mukkulin dakin nasa gashi a hannuna kizo ki bude min dakin.
Ummutu ba don ranta yaso ba ta kar'bi Mukkulin ta bude mata dakin, a maimakon tayi tafiyarta sai taja tunga ta tsaya tana kallon Gwaggo na bude wardrobe d'in kayansa tana fad'in 'Yar karamar riga yace a dauko masa kin san garin akwai zafi."
Ummatu shuru tayi sai hararar ta take, Gwaggo ta dauko masa shirt da 3qutar tana fadin."Naga yafi amfani da irin wannan a lokacin zafi." Nan ma Ummatu uffan ba tace ba.
Gwaggo ta bita da kallo tana nazarinta lokaci guda ta fusata tace." Rabi da kika ja tunga kika tsaya kina kallona ko gadi na kike yi dan kada nayi masa sata."
Ummatu da sauri tace."Aa Gwaggo ni ba haka nake nufi ba.
Gwaggo tace."Haka ne mana Rabi menene
17, October 2025
Fatima
Wow