Showing 63001 words to 66000 words out of 153671 words
Chapter 22 - GA IRINTA NAN Hausa Novels By Binta Umar Abbale.txt
magana gabana kuma na cigaba da faduwa
Yace."Ki saurare ni da kyau kiji abinda zan fada miki." Na kalleshi ina goge hawaye ya cigaba da cewa"Tun kafin na aureki jama'a suke kawo min suka akan ki cewa babu abinda kikeyi a gurin aiki sai lalata da maza wannan dalilin yasa na sake gazgata maganar mutane tunda naga zahiri kada ki mayar dani yaro nasan komai kin cuce ni kin yaudare ni ashe kin san baki da kamun kai kika sa na tsaya na 'batawa kaina lokaci gurin auranki."!
Ina wani irin kuka na zube gabansa hannunsa na rike nace."Wallahi Alhaji duk k'arya ce kada ka gazgata maganar mutane akaina sharri sukai min amma ni bana bin maza zan iya rantse maka da al'kur'ani ni ba karuwa bace budurci kuma da kake magana akansa watakila ya fita ne saboda tsayin lokacin dana dauka banyi aure ba bayan haka kuma kaga kullum bana zama ina zurga zurga zuwa gurin aiki hawa babur da Napep hakan zai iya janyowa na rasa budurcina.
Shuru yayi yana kallona da akwai alamun sassauci a tare dashi a sanyaye nace."Dan Allah ka yarda da maganata Alhaji ban yaudare ka ba kada ka amince da maganganun mutane a kaina sharri sukayi min."
Hannu yasa ya d'ago ni na zauna kusa dashi yace."Naji maganarki kuma na gamsu tabbas zaki iya rasa budurcin ki ta wad'annan hanyoyin da kike fad'a sabida haka ki share hawayen ki na amince da maganarki.
Ajiyar zuciya na sauke nace."Nagode sosai mijina ina rokon Allah ya kauda idanun makiya akanmu." ya amsa da ameeen yana kokarin miqewa yace."Ni zan tafi kasuwa saboda kin san bamu jima da shigo da kaya ba bana zama a gida sosai dan haka kina iya zuwa kiyi breakfast d'in ki."
A sanyaye nace"To shikkenan sai ka dawo Allah ya bada sa'a.'' ya amsa da ameeen ya kama hanya ya fice daga dakin.
Ajiyar zuciya na dinga saukewa ina godewa Allah da yasa ya yarda da maganata yanzu dama ashe kallon karuwa mutane keyi min? shin me nakeyi a makaranta da har mutane zasu sanya min ido su dinga zargi na da aikata fasikanci." hawaye na share a fili nace."Ya Allah kabi min hakkina akan dukkanin wanda ya d'ora min kazafi na zina.
Fuskata na wanke na d'an shafa hoda nasa kwalli a idanuwana kana na fita falon......a hakimce akan kujera na sameta tayi ado sosai kamar itace amaryar tafkekiyar wayarta ce a hannunta tana dubawa.
Gani na yasa ta saki fuskarta tana murmushi ta nuna min kusa da ita na zauna a nutse muna gaisawa.
Yaran na tambaya tace."Sun tafi makaranta sai biyar da rabi zasu dawo ai da har sun zauna suna jiran fitowarki sai kuma direbansu yazo daukarsu da kyar na lallabasu suka tafi.
Murmushi nayi nace."Ai idan sun dawo zamu gaisa da kyau." Tana tauna cingum! din bakinta tace." Kwarai hakane.
Falon ya sake daukar shuru na 'yan mintina kafin tayi magana "Sa'ida kije kiyi breakfast mana." Murmushi nayi ba tare da nace komai ba. tace."Dan Allah ki saki jikin ki dani ni bana kishi irin na jahilci kanwata na dauke ki.''
Nace."Nagode kwarai auntyn Murja. " tace."Nima nagode da kika fahimce ni saboda haka sai ki tashi kije ki karya ko." ba tare da nayi mata musu ba na mike a nutse na nufi gurin cin abincin.
A ranar haka muka yini da Aunty Murja muna hira na dinga mamakin saukin halinta kamar bata da damuwa akaina domin daidai da 'kwayar zarrah banga ta nuna wani kishi a kaina ba wannan dalilin yasa na saki jikina da ita sosai muka shiga kicin a tare mukayi aiki tsaf muka kammala komai muna hira cikin fahimtar juna
Koda yaran suka dawo daga makaranta a daki suka sameni ina shiryawa suka gaisheni suna nuna farin cikin su da zuwana cikinsu nima na dinga jansu a jikina ina duba litattafansu na makaranta.
Sai da mukayi sallar isha'i tukkuna suka fita suka barni ni kadai a dakin.....sai kawai na yanke shawarar fita falon. abin mamaki da al'ajabi maigidan na samu zaune a gurin cin abinci iyalin nasa suna zaune ko wanne da kujerarsa suna cin abinci....sosai na shiga mamakin al'amarin yaushe ya shigo gidan babu labari kuma me yasa basu nemi ni gurin cin abincin ba.?
Gwiwa a sanyaye na juya zan koma daki muryar Yusura ta daki kunnena...."Aunty kizo muci abinci." a sanyaye na juyo ina kallonsu naga shi gogan ko kallona ma beyi ba sai abincinsa yake ci itama aunty Murjar haka.... hakan da sukayi sai ya nuna min cewa basa bukatata a gurin.....jiki a mace na bude kofar dakina na shiga na rufe tare da jingina jikina jikin kofar gabana sai wani irin faduwa yake....wace irin rayuwa ce wannan? shin wai me Alhaji Nura yake nufi dani ne? ganin bani da mai bani amsa yasa na sulale nayi zaman durshan a gurin hawayen bakin ciki ya shiga karakaina a fuskata.
Na jima a zaune a bakin kofar dakin ina kuka kafin na bawa kaina hakuri na mike a sanyaye na shiga bandaki na wanke fuskata na fito ina kallon agogo goma har ta gota bai shigo dakin ba ga yunwa na kokarin cinye min 'ya'yan hanji a sanyaye na mike na fita falon sai na gansu a zaune yaran suna kasan kafet suna duba littafansu na makaranta su kuma suna zaune a kan kujera a tare yana nane da jikinta sai soyayya sukeyi. fitowa ta bai hana su abinda sukeyi ba, ta kalle ni na kalleta ina mamakin iya sharrin ta wai ni za tayi wa dariya na tsaya kawai ina kallonta da jin abinda take fad'a...."Sa'ida kina ji Yusura nayi miki maganar abinci kika share ta.''
Kai tsaye nace."Aunt Murja naga kamar bakwa bukatata a gurin ne."
'Yar dariya tayi tana kallonsa tace."Abban Yusura kaji amaryar ka da wata magana ko."?
Murmushi yayi irin na dole yace." Ina jinta ai na fahimci neman fitina take."
Kallon banza na watsa masa a zuciyata nace"Lusari mijin tace kawai."
Daga ita har shi sunga abinda nayi kuma na lura sunyi mamaki. nace."Ai idan an damu da naci abincin kira na Za'ayi ba kawai sai na fito na tarar daku kuna ci ba.''
Fuskarta ce ta sanja da yanayi na 'bacin rai kafin tayi magana ya rigata da fad'in "Ke wace irin banzar magana ce wannan? kina so ki rusa min tsarin gidana ne."? shuru nayi masa ya cigaba da fuffuka yana kumfar baki.
Nace." Dan Allah kayi hakuri naga kamar maganata ta fusata ka kasan ita gaskiya d'aci gareta."
Da sauri tace."Sa'ida kiyi hakuri anyi miki ba daidai ba kai kuma ka daina wannan kumfar bakin haka.'' Kamar anyi ruwa an dauke yayi shuru sai wani muzurai yake.....naja tsaki cikin raina na bar gurun
Gurin cin abincin na zauna na zuba daidai cikina naci na tashi na bar gurin......nesa dasu na tsaya da fad'in "Aunt Murja sai da safe." Fuskarta kamar gonar audiga ta amsa da fad'in "Allah ya tashe mu lafiya.
Dakina na bude na shiga takaici kamar ya kashe ni cikakken mutum a zahiri mai haiba da kamala uwa uba kudi amma saboda lusaranci mace na juya shi a gida wani irin tsanarsa naji a cikin raina.
Wanka nayi na shirya jikina na kwanta kan gado da waya ta a hannuna.......Misscall din Khalid na gani gabana ya fadi da sauri na mike zaune hannuna sai rawa yake.
Wani kiran ne ya sake shigowa, kamar kada na daga sai wata zuciyar tace " ki daga kiji abinda zai ce."
A hankali nayi sallama naji sanyayar muryarsa yana amsa wa. kafin yace."Aunty ya kike ina fatan kin wuni lafiya." ?
Nace."Lafiya khalid fadi abinda yake bakin ka inada uzuri.'' murmushi yayi wanda yasa tsigar jikina tashi. na lumshe idona ina sauraransa.
Yace."Wato aunty Sa'ida idan bani na kira wayarki ba ban isa ki kira ni kiji lafiya ta ba ko."?
Shuru nai masa yace."Yau so nake nayi hira dake inaso na rage feeling's ne auntyna ina nan sha'awar ki duk ta addabe ni kiyi min wani taimako mana." yakarasa maganar a sanyaye.
Wani irin yanayi na shiga na tsantsar tashin hankali da fargaba nace."Khalid yaushe zaka dawo gida." Ajiyar zuciya ya sauke yace."Na fada miki cikin satin nan zan zo kuma da sadaki na domin ba zan koma ba sai an daura mana aure.
Shuru nayi kaina yana wani irin sarawa nace."To kayi kokari ka dawo kaji ko." Yace."Insha Allahu ki bani Gwaggo mu gaisa.'' da sauri nace."Ta riga tayi bacci." yace."Okey da safe zamu gaisa insha Allahu yanzu meye labari auntyna ki fad'a min kinyi kewa ta ko."?
Ina kokarin magana ya shigo dakin, da sauri na datse wayar na ajiyeta, ya karaso kusa dani a daida lokacin da ya 'kara kira, sai kawai na dauki wayar na kashe ta gabadaya na ajiye saman bedside.
Jallabiyar jikinsa ya cire na dauke kaina daga kansa toilet naga ya nufa da gashi sai gajeran wando naja tsaki da fadin"Shashashan namiji kawai.
Minti biyar ya fito daga toilet din ya kashe wutar dakin, kusa dani ya zauna na sunkuyar da kaina ina jin wani irin haushin sa.
Shuru yayi yana tunanin da abinda zai fara "Sa'ida." ya kira sunana kallonsa nayi a kaurare yace."Kada ki sake ganin wani abu a cikin gidan nan ki tanka kome kika gani yana tafiya ne akan tsari mun riga mun tsara gidanmu nida Murja saboda haka abinda kika zo kika tarar dashi zakiyi amfani."
Na dinga kallonsa ina mamakin maganarsa......"Alhaji wannan ai ba tsari bane kwana na daya kacal gidan ka na fahimci abubuwa da yawa a gaskiya dole da kai da matarka ku canja tsari tunda yanzu na shigo gidan kuma a matsayin matar gida nake."
Hannu ya d'aga min da fad'in "Bana bukatar canza wani tsari a gidana wanda yake kai shine daidai saboda haka idan kina bukatar zama tare dani dole kibi abinda nace."
Na dinga kallonsa ina me mamakin al'amarin.... matsowa jikina yayi yasa hannunsa ya janyo ni jikinsa ya matse gam! raina ya 'baci! nayi yunkurin tureshi ya rike ni sosai ya sa min nauyinsa, hakura nayi na kyaleshi ya cigaba da budurunsa yana sambatu sai lugudar breast d'ina yake yana sha kamar zai tsinke nippels d'in, yanayin jikina gabadaya ya sanja zazzafar sha'awa mai zafi ta taso min.
Sakar masa jikin yayi ya dinga sarrafa ni iya son ransa.. Daf da zan samu satisfied ya zare jijiyar daga ramin ya dinga mutsika brest d'ina yana wani irin sambatu kafin naji saukar ruwa mai d'umi a tsakanin cinyoyina duk ya 'bata min jiki da sperm d'in shi, kafin nayi wani motsi naji saukarsa daga gadon, cikin mawuyacin hali na bude idona na bishi da wani irin kallon mamaki a lokacin da yake kokarin shiga toilet.
*SADAUKARWA NE GA IYAYE NA BIYU*
*FATIMA MUSA (MOMMY NIJAR)*
*TARE DA*
*USAINA ABDUL-MALIK ISA (KAITA)*
*(HAJIYA BABBAH)*
*_Ha'kika ina Alfahari daku da irin kaunar da kuke min.🥰🤝🏻💜_*
*43&44*
Wani irin azababben ciwo mara ta take min ta dinga wani irin d'aurewa tana murd'awa . fillo na janyo na matse shi tsam-tsam a kirjina ina cigaba murkususu da birgima a gadon gabad'aya hankali na a tashe yake ina jin wani irin azababben feelings yayin da mara ta ke sake turnukewa da ciwo mai zafi.
Zafafan hawaye ne suka shiga sauka a fuskata na rintse idanuwana ina kiran sunan Allah a fili da zucci motsin sa naji ya fito daga toilet din na bude idona dishi-dishi nake ganinsa sakamakon k'an'kancewar da sukayi,
Ni kaina nasan ina da tsananin bukata shiyasa sam ban fiye kallon india film ba dan wannan rungume rungumen da suke yakan tayar min da hankali na uwa uba kuma a yanzu na kai matakin da dole sai da d'a namiji zanyi rayuwa kamata yayi ace na samu jarumin namiji da zai dauke min dukkanin lalurata ta tsayin shekarun da nayi babu aure kwata-kwata ban tsammaci haka daga gurin Alhaji Nura ba saboda ni inayi masa kallon namiji cikakke wanda zai biya min bukatuna ashe ba haka bane *Kallon kitse na kewa rogo* Alhaji Nura ta ko'ina yana da matsala mai girma.
Zaman sa kusa dani yasa na kalleshi naga yana jan bargo zai kwanta duk ya tuje bedshirt din da ya 'bata yana so ya kwanta kan katifar a haka, raina ne ya 'baci na miqe zaune ina kallonsa.
Ya kalle ni babu wata cikakkiyar kulawa yace."Ko da akwai wata bukatar ne."? Kai tsaye nace."Eh da akwai." yace."Okey bukata mutukar ta kudi ce ki fada kawai."
Jikina yayi sanyi da jin maganarsa nace"Ni bana bukatar kudi Alhaji." kallona yayi yana neman 'karin bayani.
Kunya da tsoro na cire nace "Alhaji ni fa
Bangane abinda kake nufi ba."
Yayi shuru yana kallona na cigaba da cewa" Me yasa kake min haka ne sai ina daf da samun satisfaction sai ka rabu dani jiya haka kayi yau ma haka meye amfanin zubar da sperm din da kake a waje."
Jim yayi kafin yayi gyaran murya da fad'in "Sa'ida bana bukatar haihuwa a yanzu Yusura da Yasir sun ishe mu itama Murja abinda mukeyi kenan ni da ita tuntuni mukayi tsarin mu.
Raina ne ya 'baci nace." To ni me kake nufi dani kenan kana nufin ba zaka haihu dani ba."?
Ba tare da damuwar komai ba yace."Eh haka nake nufi ai na fada miki yara biyu kacal sun isheni rayuwa ga Murja nan munfi shekara bakwai muna haka da ita bata samu ciki ba kuma ba ta ta'ba cewa bata gamsuwa ba sai ke sarkin jaraba ko."
Hawaye suka zubo min nace." Alhaji wannan Wace irin magana ce ni kake kira da jarababbiya.''
Yace."To idan ba ita bace me yasa zaki sani a gaba kina min kuka okey kina so na jigata kaina a kanki ko? na yini a kasuwa ina nema da daddare sai na 'kare a gindin ki ko ? to ni ba haka nake ba idan nayi sau d'aya shikkenan na gamsu matata Murja bata da matsala dani .
Wani irin kallo nake masa ina mamakin maganganunsa wato dai Alhaji Nura yaudarata yayi Ashe bashi da mutunci dama."? Zuciya tace "Aa Sa'ida ke kika cutar da kanki yanzu da Khalid kika aura ai bakin ki alaikum zai cika miki mara ya dauke miki dukkanin bukatunki.
Ajiyar zuciya na sauke na kalleshi ya juya min baya ya rufe jikinsa da bargo babu abinda ya dameshi baccin sa kawai yake.
A tsananin bukace na matsa kusa dashi ina dan shafa jikinsa, ya juyo da saurin gaske ya ture ni da fad'in " Sa'ida bafa ki isa kisa nayi abinda banyi niyya ba ni na gaji ki kyale ni nayi bacci na huta gajiya."
Sakato nayi da baki ina kallonsa yaja tsaki mai karfi ya koma ya kwanta.
Shuru nayi a zaune a gadon ina sa'kawa da kwancewa, nafi karfin rabin a wa a zaune ina tunani shin ya za'ayi na warware wannan gagarimar matsalar da nake fuskanta. Hakuri kawai na bawa kaina na cire abin daga raina na mike da mataccen jiki na shiga bandaki na tsarkake kaina har na fito daga toilet din gabana bai daina tsut-tsut ba babu shakka har yanzu gurin bai daina bukatar a gaji ba.
Ban kwanta kusa dashi ba sai na dauki fillo na ajiye kasan kafet na kwanta na takure jikina cikin hijab ina addua akan Allah yasa bacci ya dauke ni......Cikin ikon Allah kuwa bacci mai nauyin gaske ya dauke ni.
Sai wajejen shida na safe na tashi, lokacin shi tuni ya fice daga dakin na dinga mamakin yanda akayi bai tashe ni nayi sallah ba. a sanyaye na mike na shiga bandaki wanka nayi a gurguje na daura alwala na fito sai da nayi sallah tukkuna na shirya jikina gabad'aya auran Alhaji Nura ya fice min daga raina, gefan gado na zauna na kunna waya ta ina dube dube so nake na kira k'awata Hauwwa na fada mata halin da nake ciki ko da akwai shawarar da zata bani....Ina kokarin kiran wayar ta Khalid ya kira babu kwari na daga wayar gami da sawa kunnena.
"Auntyna kin tashi lafiya." A sanyaye nace."Lafiya Khalid." Yace."Ya na jiki wani iri ko baki da lafiya ne."? 'Kwallah ce take kokarin zubo min na daure nace."Lafiya ta lau." Yace."Okey ki bawa Gwaggo mu gaisa a gurguje zan fita gurin wasa ne." Nace."Khalid Gwaggo tana bacci." Jim yayi kafin yace." Tunda nake banta'ba ganin Gwaggo na bacci da safe ba a daidai wannan lokacin take zaman kad'i tana sauraran redio aunt Sa'ida ko dai da akwai abinda kike 'boye min."?
Nace."Khalid Gwaggo ba ta jin dadi ne shiyasa tana karya kummalo tasha magani ta kwanta bacci ya dauketa." Cikin jimami yace."Allah sarki Gwaggo ki gaishe min da ita idan mun fito daga wasa zan sake kira." Nace."Tom shikkenan." Kokarin kashe wayar nake ya shigo dakin cikin dakakkiyar shaddar galila kamshin turaransa ya game ko'ina har ya karaso inda nake ban dauke idona daga kansa ba cikin zuciyata nace"A zahiri cikakken mutum amma a bad'ini malalaci ne.
Gaishe shi nayi ba tare dana kalleshi ba, ya amsa yana duba agogon hannunsa da fad'in "Dawa kike waya ne."? Gabana ne ya fad'i ! nace" Khalid ne."? Jim! yayi yana kallona da fad'in "Menene zai kira ki da sassafe haka."? Nace." Wai yana so su gaisa da Gwaggo
17, October 2025
Fatima
Wow