Showing 39001 words to 42000 words out of 58385 words
Chapter 14 - BA JININA BACE Book Complete by Hassana Abdul'aziz Yakasai .txt
sani sarai takura ta yayi gashi ita kuma babu hak'uri shi yasa.
Bata san tasowar saba sai tsintar sa tayi agabanta ya dafa kafad'anta "babyna me kike sone kika ja kika tsaya anan ki shigo mana?"
Kallo ta bisa dashi mai kama da harara kafin tace "ni ba babyn ka bace, Baffa ke kiranka yace tunda ya shigo baiji motsin ka ba lafiya kuwa?"
"Inafa lafiya an shake min wuya da mugun k'arfi na kasa koda hadiyar yawu" binshi tayi da kallo mai kama da na tausayi dan sam bata gane me yake nufi ba tace "kasha magani me yake damun ka bross?
"Ke ce, ya bata amsa cikin bazata kece damuwa ta, kece tunani na, kece jina, gani na, walwala na, kuma jin dad'i na, Maryam kece komai na" yafad'a cikin muryan daya mugun karyewa ta daga kai tana kallonsa duk yayi wani iri ga damuwa nan kwance acikin idanunshi
" Kazo muje"
"Kije zanzo yanzu"
"Ni dai Baffa yace k'afa na k'afar ka"
"To jira nayi wanka"
Daga haka bai k'ara cewa komai ba ya haye saman sa da gudu.
Cikin 20 mints ya sauka sanye cikin blue jeans da riga ruwan toka kayan sun mugun amsar sa kunsan farin mutum kuma mai kyau duk shigan da yay amsar sa yake.
Tana can yawon kalle kallen ta a falon taji ya rik'o hannunta binshi tai da kallo yadda yayi mata kyau ga wani fitinannen k'amshi dayake yi ma mugun dad'i, har sukaje bakin falon babu wanda yace da d'an uwansa komai sai itace ma da suka zo bakin falon ta warce hannunta daga cikin nasa ta wuce ciki abinta murmushi ya d'an saki kafin ya rufa mata baya
Duk su Baffa suka bisu da kallo yayin da zuciyar haj. Sailuba kamar zaiyi bindiga tsabar fitina da tsanar ganin Maryam daya Kuma mamaye ta Baffa yace "maman malam daga aike kuma sai najiki shiru?"
Rasa me zata cewa Baffa tayi sai ta d'ago ta dubeshi shima ita yake kallo, kafin ta lalubo abin fad'a yay saurin cewa "sanda taje ina wanka"
"To ku gama cin abincin akwai maganar da zamuyi daku duka"
"Nima Baffa akwai abinda nake son fad'a maka tun kafin kaje wajen Inna kuma naso binka sai bansan katafi ba"
Dafa kanta yay yace kar ki damu wannan zuwan ma sai da Inna tai fad'a sosai na rashin ganinki, laifin mamanki ne da tafiya ya tashi sai ta kawo uzurin da dole ake fasa tafiyan dake shiyasa Nassar kawai Inna tafi sani.
Yay maganar yana kallon haj. Sailuba da tayi wani kicin kicin da rai zuciyar ta nayi mata mugun sak'a.
Shima daga haka ya wuce falonsa Ammey ta tashi ta rufa masa baya dake yau ita ce da girki.
Suna barin wajen ta juyo da niyyar zuba abincin dan har ta k'agu taji neman da Baffa yake mata sai karaf idanun ta suka sauka cikin nasa ya wani yi tagumi ya kafe ta da ido, a ranta tace gaskiya wannan mutumin da bansan shi ba babu abinda da zai hana nace maye ne yadda yake da jarababbe kallon nan.
Azahiri Kuma abincin da zata ci ta d'iba a flat ta mik'e zata bar masa wajen, gane hakan da yayi ne yasa yayi saurin dafe hannunta yana binta da wani marai raitaccen kallo "dan Allah kar ki tafi ki barni"
Ya fad'a kamar zai mata kuka, binshi tayi da kallon mamaki, yayin da shi kuma ya k'ara wani marai raice mata sai ta samu kanta da kasa yi masa musu ta koma ta zauna, shima tsulum ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita "lafiya?"
Tace dashi tana kallon yadda yake wani faman shafa cikin sa d'an marairaice mata yayi yace"yunwa nakeji nima"
Abincin da ta zuba zata ci ta tura masa ta d'auki wani flat d'in yay saurin dafe hannunta yana girgiza mata kai ta d'an kafe shi da ido dan neman k'arin bayani "ki bani mana" ya fad'a yana kallonta ta d'an had'e rai shi kuma ya kafa mata naci sai da ta bashi haka kuma shima yabata suka ci suka k'oshi.
Da alama nacin MD ma kawai zai sa yasamu yadda yake so lol🤣🤣🤣🤣🤣
Maman Islam ce
بسم الله الرØÙ…Ù† الر ØÙŠÙ…
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 32
Tana fitowa daga d'akin daidai shigowar haj. Sailuba, idanunta k'yar abakin k'ofar Ammey dan sam bata son had'uwa da kowa wannan shine sa ar aikin ta na yau tana ganin Maryam da bata kula daga inda ta fito ba ranta yai masifar b'aci babu makawa wannan la'a nanniyar yarinyar ta b'ata mata shiri.
Tsawa ta buga mata tace "ke dan ubanki daga ina kike bana hanaki mu a'mala da wadannan matsiyatan ba?"
Da kallon mamaki Maryam ta bi mama wadda tun kafin ta kai karshen maganar ta ta gano kuskurenta tayi saurin fuskewa dan kar ta gano ta, amma duk da haka sai da Maryam ta hango tsantsar tashin hankali atareda maman tata.
"Lafiyan ki kalau mama?"
Kallonta mama ta d'an yi cikin alamun rashin gaskiya kafin ta wuce b'angaren ta cikin tsantsar tashin hankali.
Tana shiga bata bi ta maganar sallar magriba da ake ta kwad'awa a masallaci ba ta zari waya jikinta har rawa yake ta dannawa haj. Zakiyya wacce ita shigarta nata gidan kenan kira da mugun mamaki ta d'aga kiran tana cewa.
" Ya akayine k'awata ko zama banyi ba sai ga kiranki?"
" Na mutu zakiyya, shikenan kuma nawa ya K'are na shiga uku zakiyya da wannan la'ananniyar yarinyar na fara karo wacce boka yace har gwanda naga kowa dana fara ganinta?"
Ta fad'a cikin rushewa da wani fitinannen kuka cikin tashin hankali.
Ita kanta wani irin fad'uwar gaba ne ya rufeto mata agigice tace
"Ke kuwa Sailuba wanne gangancinne yasa kika bari kuka had'u?"
"Cikin kuka tace wallahi nima bansan zamu had'u da itaba kawai ina shigowa mukayi kicib'us"
"Allah yasa bakice zakiyi mata fad'a ba dan gudun kar kija mana matsalar kuma"
"Nayi, sai dai kafin na dire na gano kuskurena nayi saurin fuskewa"
Nan dai suka fara tsara yadda zasu sabunta shirin su tunda wannan ya ruguje.
Ganin yadda maman ta d'aga hankalinta har tayi hanyar d'akin sai kuma ta fasa aranta tace ai kina da kud'i zaki sha kan matsalar, ta juya ta shige d'akin ta batare da wani damuwa ba ta shiga wanka a gurguje tayi wanka ta fito ta kabbara salla bayan ta idar ta d'an yi kwalliya sama sama ta fice, duk suna wajen cin abinci kamshinta ne ya sanar dasu zuwanta, duk suka bita da kallo babu MD awajen duk sai taji babu dad'i dan tun d'azu take ta faman juya labarin da Ammey ta bata nasa tana da tausayi duk da kasancewar ba wai yasha wani wuya na azo agani ba amma rashin mahaifiya ba d'an k'aramin gib'i bane ga rayuwar yaro.
Tana shirin zama Baffa ya dakatar da ita yace taje ta dubo yayanta ko lafiya dan tunda ya shigo bai ji motsin saba, jitai gabanta ya wani buga da k'arfi take abinda ya faru agidan m Bash ya dawo mata sai dai bata da damar yiwa Baffa musu hakan yasa ta fasa zaman ta juya kamar kazar da kwai ya fashe wa aciki tayi waje duk suka bita da kallo yayin da Mama ta saki wani arnen tsaki tsanar yarinyar yana k'ara tasiri aranta, duk suka bita da kallo, basu kawo komai aransu ba tunda sunsan yadda ta tsani MD.
Tana tunkaran wajen bugun zuciyar ta yana k'ara yawaita sai da tashafe kusan 5 mint kafin tayi k'arfin halin kama mabud'in k'ofar ta tura a hankali kamar mai jin tsoron wani abu,
Tunda ya dawo salla yake zaune saman doguwar kujera ya jingina bayansa jikin makarin kujeran idanunsa a lumshe bai tantan ce halin dayake ciki ba abinda kawai zai iya ganewa itace ta cika masa zuciya duk inda zai motsa ta tokaresa.
Jin motsin bud'e k'ofar yasa ya maida hankalin sa wajen k'ofar shima bugun zuciyar sa yana kara yawaita bugu ya wani irin kafe k'ofar yay da kallo, a hankali ta shigo bakinta d'auke da siririyar sallama da k'yar ya iya dai daita kansa ya amsa yana dad'a binta da kallo ta d'an kalleshi suka had'a ido bata san sanda ta galla masa harara ba sai ya saki murmushi ya sani sarai takura ta yayi gashi ita kuma babu hak'uri shi yasa.
Bata san tasowar saba sai tsintar sa tayi agabanta ya dafa kafad'anta "babyna me kike sone kika ja kika tsaya anan ki shigo mana?"
Kallo ta bisa dashi mai kama da harara kafin tace "ni ba babyn ka bace, Baffa ke kiranka yace tunda ya shigo baiji motsin ka ba lafiya kuwa?"
"Inafa lafiya an shake min wuya da mugun k'arfi na kasa koda hadiyar yawu" binshi tayi da kallo mai kama da na tausayi dan sam bata gane me yake nufi ba tace "kasha magani me yake damun ka bross?
"Ke ce, ya bata amsa cikin bazata kece damuwa ta, kece tunani na, kece jina, gani na, walwala na, kuma jin dad'i na, Maryam kece komai na" yafad'a cikin muryan daya mugun karyewa ta daga kai tana kallonsa duk yayi wani iri ga damuwa nan kwance acikin idanunshi
" Kazo muje"
"Kije zanzo yanzu"
"Ni dai Baffa yace k'afa na k'afar ka"
"To jira nayi wanka"
Daga haka bai k'ara cewa komai ba ya haye saman sa da gudu.
Cikin 20 mints ya sauka sanye cikin blue jeans da riga ruwan toka kayan sun mugun amsar sa kunsan farin mutum kuma mai kyau duk shigan da yay amsar sa yake.
Tana can yawon kalle kallen ta a falon taji ya rik'o hannunta binshi tai da kallo yadda yayi mata kyau ga wani fitinannen k'amshi dayake yi ma mugun dad'i, har sukaje bakin falon babu wanda yace da d'an uwansa komai sai itace ma da suka zo bakin falon ta warce hannunta daga cikin nasa ta wuce ciki abinta murmushi ya d'an saki kafin ya rufa mata baya
Duk su Baffa suka bisu da kallo yayin da zuciyar haj. Sailuba kamar zaiyi bindiga tsabar fitina da tsanar ganin Maryam daya Kuma mamaye ta Baffa yace "maman malam daga aike kuma sai najiki shiru?"
Rasa me zata cewa Baffa tayi sai ta d'ago ta dubeshi shima ita yake kallo, kafin ta lalubo abin fad'a yay saurin cewa "sanda taje ina wanka"
"To ku gama cin abincin akwai maganar da zamuyi daku duka"
"Nima Baffa akwai abinda nake son fad'a maka tun kafin kaje wajen Inna kuma naso binka sai bansan katafi ba"
Dafa kanta yay yace kar ki damu wannan zuwan ma sai da Inna tai fad'a sosai na rashin ganinki, laifin mamanki ne da tafiya ya tashi sai ta kawo uzurin da dole ake fasa tafiyan dake shiyasa Nassar kawai Inna tafi sani.
Yay maganar yana kallon haj. Sailuba da tayi wani kicin kicin da rai zuciyar ta nayi mata mugun sak'a.
Shima daga haka ya wuce falonsa Ammey ta tashi ta rufa masa baya dake yau ita ce da girki.
Suna barin wajen ta juyo da niyyar zuba abincin dan har ta k'agu taji neman da Baffa yake mata sai karaf idanun ta suka sauka cikin nasa ya wani yi tagumi ya kafe ta da ido, a ranta tace gaskiya wannan mutumin da bansan shi ba babu abinda da zai hana nace maye ne yadda yake da jarababbe kallon nan.
Azahiri Kuma abincin da zata ci ta d'iba a flat ta mik'e zata bar masa wajen, gane hakan da yayi ne yasa yayi saurin dafe hannunta yana binta da wani marai raitaccen kallo "dan Allah kar ki tafi ki barni"
Ya fad'a kamar zai mata kuka, binshi tayi da kallon mamaki, yayin da shi kuma ya k'ara wani marai raice mata sai ta samu kanta da kasa yi masa musu ta koma ta zauna, shima tsulum ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita "lafiya?"
Tace dashi tana kallon yadda yake wani faman shafa cikin sa d'an marairaice mata yayi yace"yunwa nakeji nima"
Abincin da ta zuba zata ci ta tura masa ta d'auki wani flat d'in yay saurin dafe hannunta yana girgiza mata kai ta d'an kafe shi da ido dan neman k'arin bayani "ki bani mana" ya fad'a yana kallonta ta d'an had'e rai shi kuma ya kafa mata naci sai da ta bashi haka kuma shima yabata suka ci suka k'oshi.
Da alama nacin MD ma kawai zai sa yasamu yadda yake so lol🤣🤣🤣🤣🤣
Maman Islam ce
بسم الله الرØÙ…Ù† الر ØÙŠÙ…
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥 BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Godiya ta musamman gareku masoyan gaskiya hak'ik'a ina jin dad'in yanda kuke min ina ina sonku domin Allah musamman ma ku d'in nan
MAMAN Jani
Ammeyn Sadik
Antyn muhseen
Ya Rahman
Mare
Jidda
MAMAN Abul
Mom Irchad
Ummey Idris yakub
MAMAN sayyadi
Shamsan
Maman sultan
Umm nawaad
MAMAN Raees
Safiya Sopy
Aisha munir
MAMAN jabir
Xeeyyah
Rashida Muhammad
Afra
Fauzi
Ummukurthum
Aishatu k sani
Zainab autar mm
Jannat Aliyu
Barira Aminu
Hykarianeg 17
Ameenatu
Khadija Muhammad
Hafsat Bala kawu
Maman Arif
Ikilimatu D Baraya
Ummu Abul
Mr maimunatu
Aisha ibarahim ummi
Zainab Muhammad sambo
Juwairiyya Lawal
Maman twins
Mama
Khadija Isa Dari
Duk wanda bai ji sunan sa ba yamin afuwan mutara a text fage ina k'aunar ku nima son so fisabilillahi.
Page 33
Tusio tasa ta goge bakinta kafin ta mik'e " ina zaki?"
Kallon yadda ya wani lafe jikin kujeran dining d'in tayi kafin ta wani tab'a baki tace "ina kaji Baffa yace yana son ganinmu?"
Kai ya d'an dafa alamun ya manta sai kuma ya tashi yace "muje" batareda tace komai ba ta mik'e ta wuce yabi bayanta suka nufi part d'in Baffa.
Tun kafin su shiga suke jiyo b'ab'atun haj. Sailuba sai faman bala i take zubawa Baffa wani mugun tsaki MD ya saki har ga Allah ya mugun tsanar matar nan haka nan, abinda ya dad'a d'aure musu kai shine yadda suka shiga suka tarar tana zuba ruwan tujara shi kuma Baffa yana lallab'a ta yana bata hak'uri, da dai yaga abin yak'i k'arewa ne ya dubi Ammey yace.
"Aminatu dan Allah na rok'eki ke ki hak'ura taje tunda ita ban isa da ita ba baza tayi min alfarma koda sau d'aya na sauke hak'k'in ki ba"
Cikin wani irin yanayin da bazaka tab'a iya fassara shiba Ammey tace "ai dama Baffa ni ba matar gida bace 'yar zaman jiran gida bace da kula da gida ko ba haka ba?
Gaskiya Baffa wannan karon bazan yarda ba nima duk abinda zai faru sai dai ya faru amma nataji wallahi haba dan masifa da bala i shekara da shekaru abu yak'i k'arewa nima wannan karon bazan hak'ura ba Baffa sai dai duk abinda zai faru ya faru.
Nan fa Ammey itama ta bud'e wuta ta rik'a zubar da maganganu masu d'aci kunsan ance mai hak'uri bai iya fushi ba to haka ne yafaru ga haj. Amina yau duk irin yadda Baffa yaso rarrashin ta botsare masa tayi.
Dai dai shigowar su MD da suka gama sauraran komai MD ya kafe Baffa da ido kafin yace "Baffa mai yake faruwa ne nakejin abinda ban tab'a jiba game daku?" ya fad'a yana kallon Ammey cikin yanayin da bai tab'a ganinta aciki ba.
"Kamar yadda aka saba ne Muhammad yauma nayi magana ne akan kujeran hajji danake fitarwa duk shekara, Sailuba bata tab'a bari na bawa Amina tabawa wani nata ba sai sau d'aya kuma ni bansan me take da kujeru har guda goma ba tunda ko ta b'angaren mu nike biyama dangi, to itama mai hak'urin yau ta botsare min tace sam bata amince ba itama na rasa yadda zanyi yanzun"
"Kawai kabawa wanda kake ganin yafi cancanta"
"Baza abawa wanda yafi cancanta d'in ba wallahi ko zata mutu wannan kujeru nawa ne dan haka banga wanda ya isa hanani wannan kujeru ba ehe, idan kuma tak'ama ce naga ubanka ma acan k'auye raba kujerun nan yake kamar babu gobe"
"Ni bana harka da jahilai marasa ilimi dan haka bani da lokacin da k'ik'ancin ki*
"Uwar ka ta kabari itace dak'ik'iya baniba dan is...........kafin ta k'arasa taji wani irin fitinannen zafi ya karad'e fuskar ta ta d'ago a firgice dan ganin wanda yayi mata wannan d'anyen aikin sai da ta wuntsula daga kan kujeran ta ganin Baffa ya kafeta da kallo yana huci, yayin da MD ya mai da kansa k'asa cikin tsantsar b'acin rai da wani irin tsanar haj. Sailuba.
Da wani irin tashin hankali ta bar wajen domin wannan ne karon farko da hakan ya tab'a faruwa iya tarihin rayuwar su dan haka abinda yayi matan yai masifar gigitaya ta sani hakan yana nufin aikin ta yana rawa kenan ai kuwa ya zama dole ta sabunta shiri
Tana barin wajen Baffa ya dubi MD yace "Muhammad na fad'a maka ka fita hanyar Sailuba matar nan jahila ce amma bakaji" da mamaki MD yake duban Baffa to shi mai yace dan kawai yace Baffan yayi abinda yake ganin daidai shine ya shiga sangarta?
Da wani irin fushi MD ya bar wajen yayin da duk suka bishi da kallo sai Maryam ma ta rufa masa baya dan sam bataji dad'in abinda maman nata tayiba.
Ammey ma tashi tayi yayin da Baffa itama ya bita da kallo haka dai duk suka watse kowa zuciya babu dad'i Nassar ne kawai ya zauna ya ci ya koshi abimsa ya kama gabansa ya tafi gidansu boy abokansa.
Sanda Maryam ta isa part d'in MD har ya gark'ame k'ofar da key babu irin bugan da batayi ba yai banza da ita kamar baikita ba.
Haj. Sailuba kuwa tana shiga d'aki a gigice ta nemi wayar ta ta kira haj. Zakiyya kamar wata k'aramar yarinya haka take kuka wurjanjan cikin tsantsar tashin hankali ta kora mata duk abinda yafaru.
Sosai ta rarrasheta tace tunda abin haka ne kawai ta shirya cikin satin nan su wuce India can ne za ayi musu aiki mai kyau sun jima suna tattanawa kafin suyi sallama, sai lokacin ta d'an samu sassauci
Maryam kuwa d'akin ta ta koma cikin damuwa tasani cewa Mama bata kyautaba ko kad'an amma Kuma ita meye laifin ta da zai wani rufe mata k'ofa.
Ganin zaman bazai mata ba kawai ta mik'e ta saka mayafinta da niyyar taje wajen Halima ko zata d'an rage damuwa, daidai bakin get suka had'u da Baffa ya hanata fita dole ta dawo gida cikin k'unci.
MD kuwa tunda da yake babu Wanda ya tab'a zagar masa uwa ido da ido sai yau hakan