Showing 18001 words to 21000 words out of 58385 words
Chapter 7 - BA JININA BACE Book Complete by Hassana Abdul'aziz Yakasai .txt
sisi a account d'ina mama ta rance bansan abinda mama take da kudiba ita bata ajiyeba kuma bata barni na ajiyeba saikace mai caca"
Sosai maganar ta yabawa Baffa dariya yace karki damu my dear zan bud'e miki sabon account komai da komai da sunana ATM kawai Zaki amsa duk sanda kikaso ciran kud'in sannan yanzun zan miki transfer dubu d'ari biyar sai ki kiyi amfani dashi kafin na dawo motarki kuma so nake ni da kaina na zab'o miki mai kyau da tsada" tace "Baffa ni kaga kalar da nake so ta fad'a" tana nuna masa fuskar wayarta zaro ido Baffa yayi sannan yace "wannan kikeso MAMAN malam tab' wannan koni bazan iya lale million 25 nasai mota dan fariyaba anayi wutar duniya Maryam nasai miki ta 5 million inba hakaba sai dai ki hak'ura wallahi"
Ganin bazatayi nasaraba tace to Baffa amma kud'in dakace zaka zuba min yayi kad'an kaga wancan karonma kafin ka dawo har na dawo abin tausayi"
"Naji zan k'ara Miki d'ari biyu akai" tace "na gode Allah ya tsare mana kai kaje lafiya ka dawo lafiya"
"Amen ya Allah dota" daga hakan Baffa ya sallameta bayan ya bata dubu dari a hannunta kafinma ta k'araso ta b'oyesu ajakar ta har sanda ta sakko suna falon ta d'an kalli mama tace "mama bani kud'in makaranta zan wuce"
Maman ta d'an dubeta tace"Baffa bai baki bane?"
"Ya bani sun min kad'an"
"Je cikin jakana inajin baza a rasa canjiba" da sauri ta shige d'akin ta fito tana k'irga kud'in, sannan ta dubi maman tace "mamana na d'auka duka dubu ashirin da biyar ne" jin abinda tace sai da Ammey ta d'ago ta dubeta suka had'a ido ta kuwa galla mata harara ta d'auke kanta, mama tace "to Maryam ki kula da kanki kiyi abinda yakaiki domin babu mamaki ya kasance wannan shine zai kasance gatanki anan gaba"
"Ban gane me kikeson ceminba mama banason irim wannan maganan dan Allah mama"
Irin wannan maganan ya zama dole Maryam domin da sannu zaki iya rasa wani abu mai muhimmanci arayuwarki ko mu ko dukiyar ko dukanmu"
Yanzun ba iya Maryam ce take kalloan maman tata ba harda haj. Amina dataji gabanta ya tsinke take ta hau karanto hasbinnallahu aranta yayin da Maryam tabar gidan cikin sanyin jiki.
A jikin mota ta hango MD sanye cikin kakinsa da alama shima daganan office zai wuce ganin yadda yai masifar had'e rai sai da gabanta ya fad'i amma dake itama jan wuya ce sai ta had'e nata ran tak'arasa zata bud'e bayan motar tsawan daya buga mata yasa batasan lokacin data bud'e gaban ba sai tsintan kanta tayi kawai a zaune jikinta na rawa.
Sai da ya daidata zamansa sannan ya dubeta yace "ke baki iya gaida mutane bako, ita mahaukaciyar 'yar rainon naki bata koya miki girmama manya bane?"
D'auke kanta tayi gefe tana k'unk'uni tare da hararan waje ya wani fincikota da k'arfi har Saida kanta ya bugu da gwaiwar hannunsa "me kike cewa ina wasa dake ne ko?"
Shiru tayi batare data tankasa saima hawayen daya ciko mata abinda tunda yake da Maryam bai tab'a ganina, karaya a tare da ita lallai duk abinda yasanya ta a wannan yanayin ba dan k'aramin abu bane.
Tunda yaga haka sai ya fasa hukuntatan ya tunkud'eta ta koma mazaunin ta ko kallonsa bata kumayiba har suka Isa makarantar ya fito itama ta fito har lokacin jikinta a sanyaye duk da rashin jinta sai yaji tausayin ta ak'asan ranshi amma Koda wasa bai bari hakan ya nuna akan fuskar Saba, har ta juya ya kirata ga mamakinsa saiyaga ta dawo ta tsaya a kusa dashi sosai yasan cewa da abinda yake damunta domin ya jima da sanin cewa indai tana cikin yanayin damuwa to ita d'in rak'umi da akalace sai yadda kayi da ita.
Dubu biyar yabata kamar bazata karb'a ba sai Kuma ta karb'a batareda ko kallon inda yake ba bare yasa ran zata gode tayi gaba abinta murmushi kawai yayi yabi bayanta suka jera yayin da idanu sukayi kansu duk inda suka gifta sai an kallesu an k'ara saboda tsabar kyau da kwarjinin su.
Sai da ya rakata ta gama komai kafin ya karb'i wayarta zaro ido tayi tana kallonsa nombobinsa ya saka ya kira ya d'auki nata daga haka ya mik'a mata wayanta yace "Allah yabada sa a"
Har ya shige motarsa tana tsaye tana kallonsa yana shiga ya juyo ganin tana wajen harara ya galla mata kafin yaja motar yabar wajen ajiyar zuciya tasaki tana juyowa wata matashiyar budurwa wacce batafi sa artaba tana tana k'arasowa inda take, tayi tareda mik'a Mata hannu sukayi musabaha tace "ni sunana Maryam Abdullah Abubakar kefa?"
Zaro ido Maryam tayi tana kallonta kafin tasaki wani k'asaitaccen murmushi tace "ni Kuma sunana Maryam Baffa Abubakar" itama Maryam kallonta tayi da mamaki tace mata" badai Baffa Abubakar mai gidajen mai ba?" Jinjina mata kai Maryam tayi sannan tace "shine kina wane b'angaren ne?"
Tace "Islamic medicine" itama Zaro ido tayi tace ai nidake b'angaren mu d'aya tace suka tafa tareda rik'e hannun juna suna murmushi Maryam Abdullah Abubakar tace "da alama kema sabuwace ko?"
"Eh yau na fara zuwa "
"Ni kuma jiya Kinga Ashe bani kad'ai nayi missing 2 weeks ba" Maryam tace "au ke jiyama kikazo Kennan?"
"Eh wallahi" haka dai sukayi ta hira har suka k'arasa cikin ajin.
Ranan basu hutaba daga wannan malamin ya fita wani zai shiga wuni gudana na ranan farkonta amakaranta bata da wani huta, Koda ta koma gidama agajiye take wanka kawai tayi ta fito neman abinci dan wata fitinanniyar yunwa takeji ko samun damar cin abinci basuyiba.
A dining ta had'u da Nassar shima shigowarsa Kennan dan shima nasu makarantar tun safe sai karfe shida suke dawowa shine makarantar da Maryam tagama wanda acan tayi sauka tareda sauran litattafai na addini Arabic ne da boko a had'e amma akwai mugun tsada.
Sun fara cin abincin kenan MD ya k'araso wajen sanye da kayan shan iska tree queter wando da riga mai yankakken hannu irin iya kafadan nan farare kar.
Zama yai yana opposite d'in Maryam yace "d'an zubamin abincin nima yunwa nike ji sosai" yayi hakanne ak'ak'arinsa nason janta ajiki kamar yadda Baffa ya buk'ata, kallonsa tayi da mamaki dan a saninta ko abinci yazo ci yagansu ita da mama a dining d'in ya hak'ura yau Kuma ya da ahaka sai dai ko kallonsa batayi ba taci gaba dacin abincinta.
MAMAN Islam CE
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM
Page 17
Kafe ta yai da manyan idanunsa yayin datai bala in d'auke kanta tayi kamar bata san da zamansa awajen ba ganin haka yasa yajanye nata abincin yafara ci shima cikin d'aure fuska.
Dagowa tayi ta dubeshi ta ko ina bataga alamar wasaba dan haka takai hannu zata d'auki ruwa shima ya dafe hannun batareda ya kalleta ba haka Kuma bai daina cin abincin saba janye hannun ta tayi ta mik'e batare data tanka Masa ba tabar wajen' bin bayanta yayi da kallo har ta shige d'akin ta, kai tsaye toilet ta shige ta d'auro alwala tazo tagabatar da sallar magriba bayan tayi addu o i sosai sannan tafara karatun alqur ani mai girma har zuwa lokacin da aka kira sallar isha sannan ta rufe qur anin tayi ta addu o'i har zuwa sanda aka shiga masallaci tabi jam 'i daga nan cikin d'akin ta duk abinta bata sanya da addu a sam bata da wasa a wannan fannin.
Nassar ne ya lek'o ganinta ninke sallaya ya koma da gudu tana kiransa amma bai dawo ba, can kamar wajen mintuna uku sai gashi ya sake dawowa da sallamar sa ya shigo ta d'ago tana mallonshi tace "da gulmane yasa ka lek'o ka koma kamar w""""""""""" ragowar maganar ne ya mak'ale sakamakon ganin wanda ya biyo bayansa take ta maida kallonta ga Nassar tana hararan sa murmushi ya mata tareda salute nata ya juya jin kiran da Ammey tayi dan haka ya wuce da d'an tsallensa.
Juyowa tayi asanyaye har yayiwa kansa zauni asaman kujeran gefen gadonta "k'araso ki zauna hira nazo tayaki" wani kallo ta watsa masa amma batace komaiba sai uban bugu da ziciyarta yakeyi sai kawai taci gabada gyaran kayanta data soma tunda safe batasan tashinasba sai jin hucin numfashin sa tayi daf da ita a d'an firgice ta juyo saura kadan ta fad'a jikinsa saboda yadda ya matsota kamar zai shige jikinta tana k'ok'arin janye jikinta yayi saurin dafe kafad'unta ya kafeta da idanunsa mai firgita masu kallonsa d'auke kanta tayi gefe tana tura baki tareda k'unk'uni "me kike cewa nida nazo muyi hiranmu nayaya da k'anwa shine zaki shareni ki hau aikin nasan ba dan Allah kikeyinsa ba"
Bata iya tace masa komaiba saboda kusancin dayake tsakaninsu hakan yasa takasa wani kwakwaran motsi har jikinta ya soma d'an rawa rawa, wani murmushi ne ya kwace masa ganin tsoro k'arara kwance cikin idanunta,sakinta yayi ya koma inda ya taso yace "zoki zauna labarin abinda ya faru a makaranta yau zaki bani, sannan me da me aka koya muku duk abinda baki gane ba Kuma ni zakizo ki tambaya"
Ita dai tsabar mamakinsa ya hanata tankawa domin tasani cewa duk duniya babu wacce yatsana sama da ita da mamanta gashi yanzu Kuma yazo yana wani shige mata anya ba wani muguntar yake shirya mataba Kai ita Kam tana kokwanton wannan shige matan da yake.
Shi Kam duk yadda yaso janta da hira takasa sakewa dashi saima shakkunsa dayake hangowa a kwayan idanunta amma babu komai shima duk da badason ransa yake biye matanba zai daure yaci gaba har sai yaga ta saki jiki dashi.
Washe gari da wuri tayi shiri ko Kari bata tsaya tayi ba duk a shirinta na tserewa MD bata son abinda zaina had'a dashi dan ta bala in tsanar say wallahi har cikin zuciyar ta, sai dai ta makaro domin tana fitowa ta hangoshi jikin motarsa a tsaye ga draiver agefensa shi Kuma hankalinsa yana kan wayarsa yana faman latsawa.
Har ranta taji sanyi dan tayi tunanin shi zaisa yakaita dan haka a nutsenta ta k'araso tazo d'an gefensa taja ta tsaya batareda ta tankawa kowa cikinsu ba mai gadin ma datake gaidawa yau dan karta gaida Muhammad yasa taki gaidashi, shi Kam ko ajikinsa saima mota daya bud'e mata yace shiga, babu musu ta shiga driver ya shiga ga mamakinta sai gani tayi ya zagayo tadayan b'arin ya shigo', d'ago kai tayi da niyyar kallonsa suka had'a ido d'age mata gria yayi "ya dai?" ya yace yana kallonta d'auke kanta tayi kamar bataji me yace ba tunda suka shiga ya maida hankalinsa Kan computer yanason k'arasa wani aiki kan ya isa office.
Yau ta riga Maryam zuwa dan da wuri ta fito yau ma kamar juya 5k yabata batason dogon magana yake had'a ta dashi dan haka yauma amsa kawai tayi ta wuce yabi bayanta da kallo har ta b'acewa ganinsa ajiyan zuciya ya sauke sannan ya juya ya shiga mota driver yaja.
Tafiya take a nutsa tana tuna maganar da sukayi da mama yanzun kafin ta fito inda take ce mata"Maryam kiyi yadda kikeso kiyi abinda kikaga dama rayuwa bashi da tabbas inke kece yau gobe wanin kine abinda yake hannunka zai iya kwacewa ya koma hannun wani sannan rayuwa takan sauya mai bud'i ya koma talaka, shi kuma talaka ya koma me k'udi dan haka kiyi amfani da lokacin ki sannan kiyi amfani da damarki dan duk lokacin daya kubce miki bazaki sake samun irinsaba" sosai maganganun maman yake tsinkar Mata zuciya tabbas tafi kowa sanin halin mama bata maganan banza tunda ta dage akan wannan akwa k'arkarfan dalilinta haka nan yauma dazata fito dubu hamsin ta bata duk da wannan ba komai bane awajen maman amma tana mamakin yadda take bata kud'ad'e akai akai har dubu d'ari biyar tana bata musamman intasan tana da wani casu ko shagalin k'awayen ta' tana tsaka da wannan tunanin wanda yai matuk'ar d'aukan hankalinta taji tayi karo da abu kafin ta d'ago dan ganin waye an d'auke ta da wani matsiyacin mari wanda yasa saida tasaki jakarta da wayarta suka tarwatse awajen amatukar fusace ta d'ago sukayi ido biyu "me na maka dazaka mareni?" tayi masa tambayar hannunta dafe da kuncin ta "ubanki Kika yimin dan uwarki hanyar ta ubankice da zaki taho kina mana rangaji har ki buge mutane"
Itama fusata tayi tace saidai ubanka dan uwarka hanyar ta inaga naka ubanne ya ginata d'an iska wawa jaki dabba kuma wallahi ina mai tabbatar maka sainaga waye ubanka ak'asar nan sanaga g"..........kafin ta k'arasa ya Kuma d'auke da wani mugun marin take jini ya balle mata ta hanci da gefen bakinta durk'ushewa tayi awajen saboda jirin daya fara kwasar ta shima tsuganawar yayi agabanta ya d'ago hab'ar ta ya kalli cikin kwayar idonta yace kije ki turo duk uban da kike tak'ama dashi"
Duk da bak'ar azabar daya gauraye mata fuska haka bai hanata "furta cewa zaka gani ina mai tabbatar maka cewa saikaga gatana wallahi zakasan ni katab'a saikayi nadamar zuwanka duniya yau" ina jira 'yan mata ya fad'a tareda barin wajen take duk mutanen da suka cika wajen suka watse basuyi mamakin d boy ba domin takadirin d'an iska ne ya addabi kowa amakarantar gaba d'aya kowa tsoronsa yake hatta da malamai ma basu da ikon hukunta KAMAL ABBA AL HASSAN d'a d'aya tilo ga mahaifinsa alh. Abba AL HASSAN wanda yasamu dukkan dama da sake yake yadda yadda dama arayuwarsa.
Saida kowa ya watse sannan Maryam ta k'araso wajen d'ago fuskar Maryam tayi yadda taga yayi kaca kaca da jini ga gefen idonta har yayi kwanciyar jini batasan sanda ta fashe da kukaba tace "ke kuwa name sake me ya had'a ki da wannan azzalumin d boy d'in wanda bashi da mutunci ko kadan jifa yadda yadda ya mayar miki da fuska?"
Bakin ciki bai barta ta ce komaiba sai wayanta data Mik'o mata bayan ta cire code "kiramin mamana" shine kawai abinda Maryam ta iya cewa daga haka ta yanke jiki awajen ta fad'i a sume, take Maryam ta Kuma rud'ewa jikinta ya kama rawa garin ta kira mata maman ta dannan no MD wanda yai save da MY LOVELY BROSS yayi hakanne dan tsokana sai akayi rashin sa a ko dubawa ma batayi ba.
Shiganea office kenan babu dad'ewa kiran yashigo saida yai matuk'ar mamakin ganin kiran nata domin yasan ba k'aramin abune zai saka Maryam kiransa zaima iya cewa tunda suke da ita bata tab'a kiransa ba, kamar kada ya d'aga sai Kuma yace baisan dalilin kiranba bari ya d'aga yaji ko wani abunne.
Memakon muryanta muryan wata daban yaji tana kora Masa abinda ya faru cikin tsantsar tashin hankali ransa ne yai wani irin mummunan b'aci take jijiyar kansa tayi wani irin rud'u rud'u tsabar azabar fushi mik'e wa yayi a fusace yana kiran waya yai waje ko takan driver bai biba ya figi motar da mugun gudu yayin dayai magana cikin d'acin rai ta waya.
Cikin kankanin lokaci ya isa makarantar har lokacin tana jikin Maryam tana faman girgizata yayinda mutanen da suka dad'a dawowa ganin Maryam ta sume wasu na bada shawarar akaita asbiti wasu na fad'in akaita gida tunda ansa mata ruwa a fuska bata farko ba.
Cikin takun izza da isa ya k'araso wajen fuskar nan tasa babu d'igon rahama ya k'araso mutane suna ganinsa sanye da kaki tare da rubutun matsayin sa ajikin wannan d'an k'arfen da suke rubuta matsayin mutum ajiki an rubuta LIEUTANANT GANERAL MUHAMMAD BAFFA ABUBAKAR kafin kice me mutanan sun watsa, bai tsaya bin ba asiba ya sab'i 'yar uwarsa Maryam ta rufa masa baya.
Daga taku har kullum MAMAN Islam CE
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*
☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀
FCWA
*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*
https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥BA JININA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMANA ISLAM
Page 18
Asbiti mafi kusa ya nufa da ita ransa amasifar b'ace aransa yana ayyana irin hukuncin da zaiwa wannan yaron dan yasha alwashin saiya gane kurensa tunda ya tab'a masa 'yar uwarsa.
Acan makaranta kuwa anfita da Maryam Kennan wani abokinsu ya k'araso wajen su d boy yace "abokina kaga yawan sojojin da sukazo suka tafi da wannan yarinyar kuwa?"
Wani banzan kallo d boy ya watsa masa "to sai me dan tasan wani daga cikin sojoji Allah yasa bakin bindiga tasani kafa riga kasan koni waye Man kaf k'asar nan mutum bai fi biyu zuwa uku ba suke da damar iya hukuntani dan haka zanci haba da yin yadda naga dama ni kad'ai ne awajen ubana kuma yatara min shegun so kaga dole na warwasa son raina"
"Kasan d'ayar wa daka kuwa?"
"Koma 'yar uban waye dole gobe taji tsoron bin hanyar danabi"
Man bai tsaya sauraron ba yace "yar gidan BAFFA ABUBAKAR ce fa"
Duk da cewa gabansa yayi mugun fad'uwa amma Saida yace "wane banza ne haka har girman ikonsa yakai na ABBA AL HASSAN be?" Kafin ma Man yabashi amsa moticin da suka shigo na sojoji kusan guda shida suka faka agefensu ak'alla sunkai su ashirin ko ma sama su kansu malaman makarantar tunda sukaga wannan gangamin sannan ba wani taro suke ba suka tabbatar babu lafiya.
K'arasowa sukayi inda su d boy suke wani daga cikinsu yace "waye kamal d boy anan wajen?"
"Lafiya kuke nema na ko naci ban biyaba ne har aka yo mun gayyar masu gadi haka"
Wata irin damk'a d'aya daga cikinsu yayi masa turoshi gaban sauran da mugun k'arfi har saida yai baya zai fad'i suka wani talle masa k'eya suka cakume gefen wandansa suka jashi zuwa jikin motarsu.
"Kunsan koni waye kukema wannan wulak'ancin? wallahi zakasan ni kuka tab'a dukanku sai kun rasa aikinku sai kunyi nadamar abinda kukayimin" duk cikinsu babu wanda ya tankashi har suka figi motocinsu da mugun gudu sukabar wajen take hayaniya ta kaure kowa da abinda yake fad'a wanda ya raina kuwa hakan ya musu mugun dad'i ko ba komai an karya alkadarin sa.
"Ba wani mummunan rauni tajiba b'acin raine yasa ta suma amma mun shawo kan matsalar sai dai gaskiya ku dunga kiyaye shigarta irin wannan b'acin ran dan