Showing 15001 words to 18000 words out of 58385 words

Chapter 6 - BA JININA BACE Book Complete by Hassana Abdul'aziz Yakasai .txt

tsani ta bud'a ido ta gani irinsa.














Tun yana daurewa halayyar tata har abin yafi k'arfinsa domin halin yarinyar ya wuce tunanin mai tunani, hakan yasa yai masifar tsanar wannan mugun halin nata yarinyar da ya ginu da tunanin yadda zai jata jikinsa ya gwada mata Koda gutsuren k'aunar da mahaifinta yake nuna masa amma ina makircin uwar rik'onta bazai bari hakan ya faruba.
















Sanda Maryam ta cika shekara goma dai dai Amina ta Kuma haifo yaronta katon gaske sak Maryam har yaso yafi Maryam fari da manyan idanu, wannan haihuwa ba k'aramin gigita tunanin haj. Sailuba yayiba domin ta rigada tagama sawa ranta cewa Amina tagama haihuwa ita da k'ara haihuwa har abada, kamar yadda sabon bokan da suka sake ya fad'a Mata.
















Tun kafin suna take tunanin hanyar dazata b'ullowa wannan yaron dan bata tab'a jin abinda ta tsana sama da wannan yaron ba duk iya yanda taso had a makircin ta akan yaron idanun Baffa ya rufe abinda ya k'ara d'aga hankalin Sailuba yadda atake Baffa yayiwa Amina kyautar wani kat'on gidansa na G R A sannan Kuma yaron wanda yayima hud'uba da Abdul Nassar yabashi companyns na takalma company data gama cin buri akai tagama tsara duk yadda zata yi ace anbarwa Maryam shine yau ake bama wani banza da uwar banzan lallai Baffa ya tarowa kansa
















Ba k'aramin murna MD yai da haihuwar Abdul Nassar ba dan ko ba komai yasamu aboki duk da kasancewar sa mutum mara son hayaniya hakan bai hana sunyi wata irin shak'uwa da yaron ba.


















Haka rayuwar Nassar yaci gaba da tafiya cikin tsantsar so da kulawar Ammey sa da Kuma bross d'in sa kamar yadda Baffa yasa su dinga fad'a masa.












Sosai Nassar yataso yaga yadda akema uwarsa cin mutunci a fakaici shima ya kuwa yace baisan wannan ba dan haka duk abinda akasa Maryam taiwa Ammey sai ya rama akan Mama tun suna had'uwa suyi ma yaron duka har zuwa lokacin da Maryam din ta fara rage wasu abubuwan domin daga yanayin yadda Ammey take tafiyar da al amuranta yasa ta gano nagarta da kyaun halin Ammey yasa ta sassauta mata duk da cewa ba wai ta dena dukabane.
















Haka dai rayuwar yacigaba yayin da agefe guda MD yakasa jurewa fitsaran Maryam yasa duk abinda Masa yake kamata yayi Mata d'an banzan duka tun tana zaginsa idan ya daketa har azaba yasa ta daina sai dai tayi ta fad'a masa bak'ak'en magan ganu shima Kuma sai ta tabbatar databa da tazara mai yawa atsakaninsu ga wani tsinannen d'abi a da aka koya Mata na yawon club wanda mama takance tayi komai ba komai ubanta ya tara mata












Hakanne yasa Maryam take abinda taga dama kud'i kuwa ko nawa take buk'ata za a bata batare da bin ba asin abinda tayi daauba Kuma Koda an bata yanzun anjima ta buk'ata wanda suka fisu Bata za ai batare da wani bin diddigiba.












Hakanne yasa Ammey dauk'e kanta akansu har zuwa yanzun da Maryam ta fara jan d'an uwanta ajiki ta dai ce aun daina fad'a to bari mu gani da gaske ne ko Kuma wani shirin ne Maryam da uwarta suka Kuma yowa














Muje zuwa


Daga taku




Maman Islam
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*




☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀


FCWA


*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*


https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________🔥BA JININA BACE🔥


2021


NA


HASSANA ABDUL AZIZ YAKASAI


MAMAN ISLAM








Page 14




Cigaba


Suna shiga d'akinta Nassar yace "Adda ni nafasa game muje muyi kwallo kawai, kawai ko muyi basket kallonsa ta d'anyi tace "a a nak'i wayon saboda kasan kafini kwarewa anan ko" yace "to naji buga game d'in Allah yabawa mai rabo sa a"
















"Hello k'awata akwai matsala fa wallahi ina cikin damuwa"ta d'aya b'arin haj. Zakiyya tace "mun shigesu wane irin matsala Kuma kinsanfa bana juran irin wannan k'ananun zantukan yanzun sai kisa cikina ya murd'a"




"Hmmm kedai bari k'awata wannan tsinanniyar matar Saida tasan yadda tayi ma Maryam asirin da gashi tana neman sawa Maryam tafi k'arfi na zokiga yadda take wani jan wannan shegen yaron ajiki wallahi karkiji zuciya na"












Itama Zakiyyan ajiyar zuciya ta sauke idan bata manta aikinsu na farko ba bokan ya tabbatar musu da cewa ba ko yaushe ne suke da nasara ba dole wani lokacin a jarrabisu da rashin nasara dan matar atsaye take itama bata sanya wajen addu a sannan babanta ma tsohon mugun matsafine" kujifa?














Sosai suka shiga neman mafita wanda daga k'arshe dole suka yanke komawa wajen tsohon bokan da suka daina zuwa tun tuni.












Maryam kuwa suna d'akin har lokacin suna buga wasa da Abdul sai rinto take masa da ya cinye saita ce ba hakaba tun yana hak'ura har shima yai zuciya ya tashi ta dubeshi "ina zaka?"


"Wallahi na daina wasan sai na cinye saikice ke baki yardaba kuma ke kike min rinto nadaina shike nan" yafad'a kamar zaiyi kuka tace "to shikenan k'anina zokaji wani abu" ya rank'wafo kamar zaijin ya kuwa d'auke wayarta daya gama fakonta ya haddace password d'inta, ai kuwa ya zuba da gudu ko takan Baffa da Ammey da har lokacin suke dining bai biba ya arce waje, can saiga Maryam d'in ta biyoshi tana fad'in "wallahi inbaka bani wayana ba saina fasa baka wannan abinda nace" ganin har ya fita itama tabishi da gudu yayin da iyayen suka bisu da kallo cikin sanyin rai.
















Da gudu ya shige lambu itama ta rufa masa baya sam idanunta bai kula da dutsen ba sai data taka santsi ya d'ebe ta tafi zata fad'i tasaki k'aran firgita jinta ajikin mutum yasata sakin wani irin ajiyar zuciya.






MD wanda tun shigowar Abdul da gudu ya dawo daga duniyan tunanin daya tafi ganin Maryam ta biyoshi tana hayaniyan data saba indai antab'ota yasa ya maida hankalinsa kansu baisan ya akayi ya isota lokacin datayi sufa zata fad'iba shidai kawai yaganta ne kwance saman kirjinsa Maryam wacce sai lokacin ta bud'e idanunta ganin jikin wanda take tayi saurin tashi tare da sakin wani d'an uban tsaki, abinda yafi tsana a rayuwarsa ya fincikota da mugunta ta Kuma fad'owa jikinsa Saida tasaki k'ara saboda bigewan datayi da gwaiwar hannunsa, cikin b'acin rai yace "dawa kike? ni sa ankine da zakimin tsaki?"
Dubansa tayi taga har idanunsa ya sauya tasani Sarai idan tashiga hannunsa bazataji da sauk'i ba d'auke kanta tayi tana hararan gefe tace "ni ai ba dakai na keba da wancen nake" ta fad'a tana nuna dutsen daya tad'eta, duk da yanayin dayake ciki sai da abin yaao dariya yadan murmusa ya tun kud'eta daga daga jikinsa sai data kai k'asa ta na tashi kuwa ta galla masa harara da murgud'a baki tace dakai nakeyi me ka isa yimin yi yayi kamar zai kamota ta taka da gudu ta wuce cikin gidan.












Da yamma suka fito domin zuwa gidan malam gaba d'aya har Baffa wannan k'aida ne idan ya dawo sai yajema malam tare da dumbin alkhairansa mai tarin yawa.














Bayan sun gama gaisawa da malam Amina da Nassar sukayi cikin gidan yayin da Baffa ya tsaya anan suke dad'a gaisawa da malam anan malam yake tambayarsa ya kuwa lek'a Inna?
D'an sunkuyar da kansa k'asa yai yana sosawa cikin ladabi yace "ban Sami zuwaba har yanzu amma ina mata aike akai akai"










Malam yace "zancen banza kenan ance maka wai abin hannunka ne maganin matsalar ta karfa kamanta Kai kad'ai ne d'an da Allah yabata a duniya ina mai tabbatar maka tafi buk'atar ka akan duk wani abu da kake da Kuma Allah ne kad'ai yasan halin datake ciki akan hakan, dan haka nake umartarka daka daure kaje"












Shiru yayi cikin d'acin rai yarasa wannan masifa yarasa abinda yake damunsa shida mahaifiyarsa amma zuwa inda take ya gagaresa meke nan meyake faruwa da rayuwansa ne?




















Maman Islam ce
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*




☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀


FCWA


*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*


https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥BA JINANA BACE🔥
2021
NA
HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI
MAMAN ISLAM


Page 15




Sun jima sosai a wajen malam yana dad'a fad'a masa maganganu masu sanyaya jiki da karyar da zuciya sosai yaji babu dad'i shi da kanshi yana matuk'ar kewan mahaifiyarsa tsohuwar Allah ta ala amma ya kasa sauke hakkinta dayake kansa tsayin lokaci, har hawaye Saida yayi malam ya rik'a lallashinsa tareda nuna masa kuskurensa.












"Adda zo muje gidan su anty Halima dan Allah" hararansa tayi tace "bazanjeba ka manta dazu kasa Baffa ya hanani zuwa sayan kayan kwalliya Kaine kace na cika ta adin kud'i"


"Kiyi hak'uri dan Allah Adda na daina" da k'yar yasamu yasha kanta suka fito, yamma ce sosai ga uban hadari bak'i k'irin har tace su koma Nassar ya nace suka fito dai dai nan motan MD ya shigo sanye cikin kakinsa da alama ya dawo atafiya ne d'an tun ranan data k,wace suka had'u alambu basu k'ara had'uwa ba sai yau da murna Nassar yai wajensa yayin da Maryam ta d'auke kanta kamar bata gansa ba.














Kanta na k'asa batasan ganinsa, duk da kasancewar Nassar ya d'auke hankalin Shi da surutu amma dukkan motsinta yana ankare ta gefen ido yake k'are mata kallo yana mamakin yadda take da d'an Karen d'aukar Kai da mai da kai ba komaiba an riga an gama da ita ranan dayabar garin yanaji ana fad'a da ita akan ta zagi mai gadin kusa da su mama tana goyon bayanta akan wai da abin daya mata hakanan Maryam bazata zageshiba sai da dalili wannan abu ya bala in b'ata masa rai.








Sai dai masu Karin magana sunce hannunka baya rub'ewa ka kayanke ka yar dole zai koya Mata tarbiyyan da aka gaza bata tun farko amma yasani fitsara ne zaisha kala kala ita Kuma taci bak'ar wahala.














"Kira min Addanka Nassar" yafad'a cikin rashin sonaganar sa, sai da Nassar ya k'ara kallon MD dan mamakin aiken daya masa "bazaka bane" yafad'a cikin daka tsawa da gudu ya k'arasa "Adda kizo inji bross" wani banzan kallo Maryam ta watsawa Nassar kafin taja tsaki tace "ina wasa dakai ne dazaka zomin da wannan banzan sak'on?
To ka koma kace bazan"""""""""kafin tak'arasa taji d'all asaman leb'b'an ta da mugun k'arfi da sauri ta dafe bakinta tana kallon sa yadda yai bala in daure fuska saitaji wani irin shakkarsa ayau d'in, shikam k'ara tamke fuska yayi yace "wato ke maraya kunya ko kullum iskancinki k'ara gaba yake to ni d'in nan sai na gyara miki zama ke k'aramar mara kunyace wallahi kuma ku koma babu inda zaku fita da wannan hadarin"












Maryam wadda har idanunta ya fara ciki da kwalla ta juya batareda ta kalleshi ba har yana mamakin rashin mai da raddinta dan yasan hali saidata tabbatar takai tsakiya kafin ta juyo ta galla masa harara tace "kuma sai Allah yasakamin ban yafe ba" ya d'an taka kamar zai bita ta shige da gudu,
Murmushi ya d'an sosa kansa aransa yace wannan saitata ba k'aramin aiki bane andai riga da an cuci uwarta ne an lalata Mata tarbiyyan d'iya.












Tana shiga falon taci tuntub'e da k'afar Ammey da ta mik'e tana zaune saman kujera saura kad'an ta fad'i Ammeyn ta tarota "ke lafiya kike wannan uban gudun saikace wata wacca aka biyo?"
Maimakon amsa saita fashe da kuka Ammey ta d'ago kanta saita ga lebanta a kumbure gashi har sun d'an tsatstsafo da jini "waya dakar miki baki har ya kumbure haka?"kasa bata amsa tayi sai sabon kukan data fashe da.




Nassar ne yace "wallahi Ammey bross ne ya dakar mata baki da k'arfi saikace yasami sa ansa"
Hararan Nassar Ammey tayi tace "haka nan dai bazai daketaba da abinda tayi masa inba hakaba bazai tab'a taba"






Hararan Ammey Maryam tayi sannan taja tsaki tabar wajen dama rashin kunyar ta bawai ta dainayi mata neba in babu Nassar awajen tana d'an tab'awa da kallo duka suka bita yayin ta shige d'akinsu mama tana can gidan haj. Zakiyya ta rasa tsiyar da suke k'ullawa agidan wannan haj. Zakiyyar hakanan ta tsani matar ko gidan ta zo sai maman tayi da gaske take gaidata.










Bayan wata uku






Sakamakon jarrabawan su ya fito ba k'aramin farin cikin sakamakon Baffa yayiba haka Kuma haj. Sailuba tasa dole yasai mata mota matsayin gift d'in cinye jarrabawan datayi ko kad'an hakan baima Ammey dad'i ba amma bata da ikon magana tunda anyi mata iyaka da hakan amma kullum tana kaiwa mahalicci kukanta ba dare ba rana tana sane da cewa baya bacci tana fatan ya bimata hakkinta akan yadda ake d'ora mata rayuwar d'iya.










Haka ma muhammad baiso akaba Maryam sarkin rawar Kai motaba ta mama datake fita da itama bason ransa bane amma Baffa yace yayi hak'uri ya riga da yayi mata alk'awarin intaci jarrabawan duk abinda take so zai sai mata.




















Hakama b'angaren cigaban karatunta Baffa yace ta zab'i duk k'asar datake son yin karatu' tace ita tace ita Dubai take so tana son gadon Baffa amma Islamic medicine sosai hakan yayiwa Baffan dad'i sai dai wannan karon Muhammad yayi nasara Dan cewa yayi k'anwarsa mace bazataje wani k'asa karatuba anan kusa dasu zatayi.








Wai Maryam batasan sanda ta fashe da wani mugun kuka ba tace "ai dama na dad'e da sanin cewa baka k'aunar mu nida mamana wai ma ina ruwanka da rayuwana ne da zakabi ka takura ka addabeni ni bana shiga huriminka amma ni duk kabi katakurawa rayuwata yadda ka tsane ni haka nima NA TSANEKA NA TSANEKA NA TSANEKA haka maganar ta yayi ta amsa kuwwa a kunnen tunda yake bai tajin maganar daya masa d'acin wannan ba sosai abin ya dake shi da sauri ya tashi da nufin binta Ammey ta dakatar dashi haka ma Baffa sukace ya k'yale ta yanzun tana cikin zafine.










Maryam bata san kukan rashi ba a rayuwarta an d'ora tane akan cewa ubanta yana da komai dan haka duk abinda take so zata samu hakan ne yasa tai masifar saka ranta da tafiya Dubai yayin da Mama take dad'a ingizata wannan dalilin yasa taji ta Kuma tsanar MD aranta fiye da yadda ta tsanesa abaya.












A b'angaren MD kuwa tunda ya koma d'akin sa maganar Baffa yake tayi masa Kai kawo "Muhammadu ka taimakemu kaja Maryam a jikinka ka rage wannan 'yar tsamar dayake tsakaninku domin duk duniya baku da kamar junanku Kai kafi kowa sanin haka sannan in Mai k'ara jadadda maka alk'awarin d'an uwana Hassan bazai tab'a tashi a banza babkoda k'asa ta rufe idonsa babu abinda za a fasa.










Sosai abinda Maryam d'in ta masa ayau yai masifar tsaye masa arai bai tab'a jin d'acin abinda take masa irin na yau d'in ba ya jima yana Kai kawo kafin ya samu Kiran gaggawa daga office dan haka ya shirya cikin sauri ya fice










Tunda ga ranan bai k'ara had'uwa da itaba dan ko fitowa tayi ta jangoshi komawa take da gaske bata son ganinsa wani b'acin rai take tsintar kanta a ciki duk lokacin data yi arba dashi.












Shi da kanshi ya nema mata makarantar da ransa yake so sai da ya gama mata komai sai sa hannun da yazama dole ita zatayi da kanta sannan ya kawowa Baffa komai sannan yacewa Baffa indai yana gari to shine zaina kaita ya kuma d'auko ta hakan yasa hankalin Baffa ya fara kwanciya.




























Maman Islam CE
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*




☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀


FCWA


*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*


https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥BA JININA BACE🔥

2021
NA


HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI


MAMAN ISLAM




16


Koda Baffa yazo musu da maganar makarantar tsalle sukai suka dire kamar had'in baki sukace su indai abu daga hannun MD ya fito basa sonsa, ranan haj. Sailuba taga ruwan bala i wajen Baffa bata tab'a tunanin ya iya jaraba hakaba sannan a k'arshe yace matuk'ar tasaka Maryam ta bijirewa makarantar sai tasha mamakin sa badan tasoba ta lallab'a Maryam ranan Monday tayi shiri cikin tsananin fushi.












Cikin tashin hankali ta Kira haj. Zakiyya take fad'a mata yadda sukayi da Baffa da irin wutar daya bud'e mata abinda bai tab'a yimata ba tace "ni abinda yasa bana son kusancinta da wannan tsinannen yaron saboda" banji abinda tace mataba saijinai haj. Zakiyyar tana cewa"muci gabada shirinmu k'awata komai zai tafi yadda ya kamata itama Deedah can zataje dole ko bata so domin aikinmu yafi tafiya dai dai Kuma dole zasu zama k'awaye na irin mamakin nan ta hakanne aikinmu zaifi tafiya.












Haka dai sukaci gabada kulle kullensu wanda su kad'ai sukasan abinda suke shiryawa.
















Zaune suke afalon suna d'an tab'a hira jefi jefi dan matuk'ar Baffa yana gari bazaka tab'a gane asalin halin Sailuba ba shiyasa Baffa yake ganin har tafi Amina son Maryam baisan irin wainar da ake toyawa agidansaba kuma bai tab'a ganewa ta kalan halayen yarinyar ba domin son dayake mata da kuma muguwar kisisinar haj. Sailuba bai bashi damar gane abinda take tafiyar dashi na rayuwarta ba domin ta toshe duk wata hanya da zai gane hakan da asirinta da kuma kissa.












Koda tagama shirin ta cikin wani bluen swiss mai matuk'ar kyau da tsada kasancewar ta mayyar kwalliya ba k'aramin ado ta tsarawa kantaba saikace wacce zata gidan biki.










Kanta tsaye b'angaren Baffan ta wuce dan har yagama shirinsa yau zai koma wannan karon China ya nufa dan shigo da wasu kaya dan haka shima cikin shiri tasame shi, ta d'an had'e rai tace "Baffa ina kwana?"
"Kin tashi lafiya merona?"




"Lafiya tace ganin shi cikin shiri tace Baffa tafiya zakayine?"
"Eh Maryam Kinga wannan karon na dad'e dayawa ga kayan dana zo dasu saura kad'an dan haka daga China zan wuce Dubai dan shigo da sauran kayan harda dogayen rigunan dana tab'a kawo miki to suma na d'an gwadasu suma naga sun tafi har ana ta cigiyarsu dan haka suma zan siyosu" sosai hakan yaima Maryam dad'i arai sai dai wannan karon bata nuna rawan kantaba tace "Allah ya k'ara bud'i da d'aukaka Allah ya kare mana ku Baffa daga dukkan abin ki dan fiyayyen halitta amen"












Sosai Maryam ta d'auko wasu daga hallayar mahaifiyar ta na yaba kyauta duk kankantar abu da kuma kyauta ga duk wanda take tareda dashi sannan bata da k'yamar wanda take ganin tafishi ko natane wannan halayyar yana matuk'ar burgesa.














"Baffa ya maganar motana kaga yau zan fara zuwa school Kuma bani da ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login