Showing 12001 words to 15000 words out of 58385 words

Chapter 5 - BA JININA BACE Book Complete by Hassana Abdul'aziz Yakasai .txt

damuwa da al'a muranta














Hakan kuwa akayi duk yadda taso ganewa bata bata damar hakan ba haka ta rik'a daurewa tana nuna babu komai duk da kuwa irin bak'ar azabar datake sha wajen cimaka da kuma rashin son wani k'amshin haka ta dinga daurewa har zuwa lokacin da cikin shiga wata bakwai bai fitoba amma komai nata ya k'aru domin Amina macece mai matuk'ar kyau da diri gata fara tas babu ta inda ta baro mahaifiyar ta bafulatanar asali mazauna wani daji.
















Bayan wata guda lokacin cikin ya shiga wata na bakwai Kuma cikin kariya da k'udura na Allahu S W T A daga Baffa har Sailuba babu wanda Allah yasa ya gane cewa Amina tana da ciki, yayin da Baffa yadamu sosai har yana cewa kodai wani abun tayi dan karta haihu dashi?










Tun bayan da cikin ya shiga wata na biyar ta daina duk wani laulayi sai dai dan banzan kwad'ayi kasancewar Koda yaushe itace a kicin tana bauta da aiyukan gidan hakan yasa duk abinda ranta yake so shi take dafawa taci son ranta kayan kwalam kuwa Baffa baya rabo da kawo musu dake ita Sailuba tafi ganewa ta narki abinci aci kaji da su kifi duk wannan abubuwan basu dameta ba haka Amina zatayi taci ta kuma bawa duk mai rabo dan itama mutum ce mai yawan kyauta kamar Baffa, sannan kuma duk wani irin kyau da shek'i data k'ara hakan baisa Sailuba ta ganeba kasancewar dama can ita d'in Mai kyaun ce, Baffa ne kad'ai ya kula da hakan saidai bai tankaba domin ya lura da ita a y'an kwanakin wani bin sai tayi ta k'unci irin dai abubuwan da ba a raba mai tsohon cikin dashi.


















Ranan wata laraba Amina ta tashi da matsanan cin ciwon mara cikin dare Allah yasa Baffa ad'akin ta yake ganin irin murk'ususun wahalar datake yasa yayi tunanin ko wani cikin tasamu zai fita dan haka yadda take kuka tana fad'in ya taimaka mata haka shima yake rok'on dan Allah karta bari wannan karon ma yayi asaran cikin dakyar ta iya bud'an baki tace"dan Allah ka taimakamin Baffa ba bari bane wannan karon haihuwa zanyi d'a zan haifa Baffa da sam bai gane abinda take cewaba ya fita da gudu zuwa d'akin Sailuba dagashi sai gajeran wando ko riga babu ajikinsa haka ya fice yatasota tasha mamakin ganin yadda Amina take murk'ususun ciwo wani b'oyayyen murmushi ta saki tana fad'in aranta magani yabi jiki Kennan, ita ta taimakawa Baffa yasa kaya yasunkuci Amina da gudu yayi waje sam kasancewar sa na likita bai kamata ace har irin haka yafaru a gidansa ba matarsa da suke kwana su tashi tare har tasamu ciki ya kai tamakin haihuwa duk bai saniba, amma idan mukayi duba da cewa Allah shine me yadda yaso Kuma asanda yaso sai muga hakan ba abin mamaki bane.












Labarin yafara sauyawa ne daga lokacin dayagama dubata ya tabbatar da abinda ya gani bai k'ara tabbatarwa sai da yayi mata scainin, tashin hankali yatad'a a rud'e domin ganin dan mutum muraran yana neman hanyar isowa wannan duniya mai cike da abin al'abi da mamaki.










Kasa control d'in kansa yayi yafashe da wani k'arkarfan kukan dayasa Sailuba danno kai cikin d'akin da mugun gudu zuciyar ta kamar takarda tsabar haske tasani wannan kukan na Baffa yana nufin wannan karon ma sunyi messing babynsu saidai kuma abinda tagani ba k'aramin kad'uwa tayiba domin har lokacin bai kashe na'urar ba ga babyn nan wanda basu gane wane jinsi bane na ta wutsulniya sosai ta daskare a jikin k'ofa zuciyar ta yana wani irin masifaffen bugu.












Wani irin juyi Amina tayi gami da sakin wani k'arkarfan nishi da gudu Baffa yatarota dan saura kad'an ta fad'o daga gadon tarotan yayi daidai da sallamar babyn izuwa duniya wadda ta fad'o ita da mahaifar gaba d'aya rasa yadda zaiyi yayi sai kawai ya zube gwaiwoyinsa ak'asa yayi sujjada shukuriyya kafin yayi saurin Kiran ma aikata suka shigo dakayan karbar haihuwa shi ya gyara matarsa da 'yarsu takafin ya rungumeta ajikinsa yana tofe ta da addu o I kala kala.










Wani abin mamaki tun kafin Baffa ya sanarwa kowa haihuwa Muhammad yafara sanarwa haihuwar Wanda a yanzun yake shekara ta uku amatakin karatuntasa Wanda yakeyi Kuma zab'in Baffansa yayin da ak'asan ransa Kuma yasha alwashin bayan ya gama zaije yayi na soja wanda shine zab'i da ra'ayinsa amma yanzun kam zab'in mahaifinsa yabi yake Wanda ya zabar masa.












Hakanan ya tsinci kansa da wani irin farin cikin kasancewar ganin Baffansa cikin tsantsar farin ciki, haka ma Inna ana fad'a mata haihuwar da kanta ta taso abinda bata tab'a yiba wato kwana agidan Baffa wannan karon cewa tayi ita zata kula da maijegon da'yarta wannan karramawa ta Inna ya k'ara mata kima da mutunci a wajen iyayen Amina.












Ranan suna kuwa Saida Muhammad ya yabaro makaranta yazo suna yasha fad'a wajen Baffa domin a lokacin suna shirin jarrabawane, a lokacin murmushi yayi yace kasa daurewa ne.












Tunda yai arba da kyakykyawar yarinyar yaji ta masifar shiga ransa shikenan Kuma ya tare a d'akin domin kullum ya fito daga b'anga rensa yana d'akin Ammey kamar yadda itama Baffa yasashi fad'a mata har zuwa sanda yakoma makaranta dakewar MARAYAM kamar yadda taci sunanta wanda take Ammey tace sunan mahaifiyar malam ne hakan kuwa yayiwa malam dad'i kulawa ta musamman yake bawa yarinyar kullum sai ankai Masa ita ya tofeta da addu o in tsari












Sailuba kuwa










Takuce maman islam
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*




☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀


FCWA


*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*


https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
BA JINANA BACE
2021


NA


HASSANA ABDUL AZIZ YAKASAI


MAMAN ISLAM












Page 12




Haka rayuwa taci gaba da tafiya, yayin da Sailuba sukayi amanna da malaman tsubbu wani lokacin suyi sara kan gab'a wani lokacin kuma sai b'ata lokaci da nesan ta kai da mahalicci.










Wata rana Sailuba takaima k'awarta haj. Zakiyya ziyara anan ne take cewa "k'awata ni kuwa me zai hana ki karb'i Maryam?"










Wani d'an iskan kallo ta watsa mata tace "amma k'awata basiranki ya gude ne ko?kirasa yar da zakice na karb'a na raina da hannayena masu albarka"












"Hum k'awata kenan inbaki saniba ki sani rainon wannan yar shine zai baki duk wani abu da kike nema kuma ta hakane zaki cimma burinki akanta sannan zokiji" tajawo tayi mata rad'a, bushewa sukayi da dariya suka tafa sun jima suna kulle kullensu kafin su sallami juna.


















Haka Maryam taci gabada samun kulawa daga ta ko wane fanni kamar yadda Nanne ta buk'ata haka dole Ammey ta cire kunya take kula da yarinyar ta domin ta kula abokiyar zamanta ba irin wannan matan bane da suke son jan d'an wani jikinsu.












Sai dai abinda yai masifar d'aga hankalin Amina shine sanda Maryam ta isa yaye kawai tace ita Maryam takeso abata tunda ita an tabbatar da bazata k'ara haihuwa ba, ita kuma Amina yanzune ma ta soma Kuma babu wanda yasan iyaka ci sai Allah dan Allah ya rok'ar mata ita ta temaka tayi mata wannan sadaukarwar.












Wani irin masifaffen tashin hankali ne yakawowa ziciyarta farmaki take tafashe da wani fitinannen kuka mai mugun k'arfi wanda yasa duk suka maida hankalinsu kanta yayin da Baffa yake dubanta da masifar mamaki Sailuba kuwa wani b'oyayyen murmushi take saki azahiri Kuma hawayene yake ta rige rigen fitowa daga idanunta ta bala in kalar tausayi ta taso ta durk'usa agabanta tareda rik'o hannayenta tana wani irin kuka mai cin rai tace.
















"Dan girman Allah badan halina ba dan soyayyar da kikewa annabinmu muhammadur rasulillah (S A W) ki taimaka kiyimin wannan sadaukarwar na miki alk'awarin Maryam bazata tab'a sanin zafin cewa bata tareda mahaifiyar taba zan rik'eta da gaskiya da Amana zan kula da ita fiye da yadda bakiyi tunaniba kiyimin wannan temakon 'yar uwata" ta k'arashe tareda zubowar wasu hawayen Mai uban yawa.
















Wani irin tausayin tane ya rufe Baffa yasawa ransa Koda wannan ce kad'ai kwansa a duniya ya baiwa Sailuba ita halak malak ko ba komai Sailuba 'yar uwarsa ce jininsa Koda baya raye ita mai rik'e masa 'yarsa ne.










Ta ko Amina wani mugun kallo ta watsawa Amina kuma tasaki wani mugun tsaki mai k'arfin gaske tace"Allah ya baki naki kema maman Maryam shine sunan data rad'a mata tun bayan haihuwar Maryam amma kisani kome zai faru bazan iya baki 'yata ba domin wannan ai zakunci ne ace an rabani da d'iyata wannan sam bazai yiyuba wallahi" ta k'arashe tana kuka bil hak'k'i domin yanayin kallon dataga Baffa yana mata shi yake nuna jin d'acin kalamanta, batareda ya k'ara duban inda takeba yacewa Sailuba










"Karki damu insha Allahu babu wani abu dazaki nema kirasa shi matuk'ar yayanki Baffa yana raye dan haka bazakiyi kuka rayuwarkiba" daga haka ya tashi ya d'auko Maryam dake d'akin uwarta tana baccinta hankali kwance ya dawo inda suke har lokacin Sailuba bata bar kukan datake ba yace.










"Gata nan na baki amanar ta ki kulamin da ita karki bari wani abun yasameta Kinga itake nan abinda Allah ya mallakamin a halin yanzu wannan kyautar ba kowa Allah yakewa irintaba nasan ko babu raina ke mai rik'e min 'yatane dan haka bana so kisawa ranki cewa bake Kika haifi Maryam ba haka banaso tasan cewa bakece mahaifiyar taba"












Cikin wata irin razananniyar k'ara Amina ta sulale awajen ta fad'o k'asa sumammiya take suka yo kanta cikin tashin hankali suna jijjigata Baffa ne ya tashi da sauri ya kawo ruwa suka shafa mata take ta kawo ajiyan zuciya, zumbur ta mik'e tana wani irin kuka mai cin rai d'akinta ta shige da gudu yayin da Sailuba ta kalleshi tace " Baffa ko mu maida mata da 'yarta kar wani abun Kuma yazo yana dasamun jifa abinda takeyi"
"Karki damu zata rage kinsan dole ne taji babu dad'i ace 'yarta guda d'aya tak an kyautar wanda bamu da tabbacin cewa tana da wani Kwan takakke bayan wannan musamman idan Kika duba irin yadda ta ringa samun cikin yana zubewa"














Ita ko Amina tana shiga d'akinta ta fad'a saman gado tana wani irin masifaffen kuka mai matuk'ar cin rai tasawa ranta kome zai faru wallahi bazata bawa wannan matar yar taba matar da bataso zuwan yarinyar duniyaba duk wani irin tuggu da ta dinga had'a mata wanda ya dinga sanadin zubewar gudan JININTA tana sane mutumin kuwa da baya son ganin kwanka sanyin idaniyarta a duniya ai baka da mak'iyi sama dashi mayafinta ta zara kawai ta fice agidan tana kallonsu har lokacin suna dining Baffa yana rarrashin Sailuba datace zata dawo mata da yarta.












Kai tsaye gidan su ta nufa tsabar rud'anin data shiga bai barta ta kula da malam dake zaune saman dakalin k'ofa ba ta shige d'akin Nanne wace fitowar ta kenan a wanka tana shirin zuwa duba surukar shamsiyya wacce ta sha ciwo Umma taje ta sake zuwa ita sai yau Allah ya nufa dake a tsarin malam baya yarda su fita rana d'aya sai dai d'aya taje d'aya ta jira.














Tagama zura hijabinta Kennan juyowar da zatayi taji fad'owa Amina jikinta tana wani irin mugun kuka mai masifar cin rai, take jikinta ya kama rawa ta rik'e ta da kyau tana tambayarta ta abinda ya same ta cikin tashin hankali domin tasan duk abinda yasaka Amina kuka to lallai abin yakai intaha.














Amina ta kwashe duk yadda sukayi da su Baffa ta fad'a mata cikin kuka ta k'ara da cewa 'Kuma Baffa yace ko kallon yarinyar kar na K'ara you amatsayin 'yata.










Wani fitinannen kallo Nanne ta kafe Amina dashi yayin da ziciyarta yake wani irin tasa tace










Taku ce maman Islam
بسم الله الرحمن الر حيم
*__________________________________*




☀ *FIRST CLASS WRITER'S ASSOCIATION* ☀


FCWA


*{Home of qualities and trusted writer's of The nation}*


https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp
*________________________
🔥BA JINANA BACE🔥


2021
NA


HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI


MAMAN ISLAM






Page 13


"Yanzun shi Baffan ne ya d'auke 'yar yabawa kishiyarki akan me shi ya haifa Miki yar ko su sukayi Miki rainon da nak'udar wallahi bazai sab'uba bindiga a ruwa" sosai Nanne ta hau fad'a ta inda suka shiga bata nan suke fitaba sosai ranta yai azabar b'aci ganin fad'an bazai fisshe taba ta finciki hannun Amina tana fad'in"zo muje gidan dole su baki yarki haka akeyin kyauta da abun wani mugunta"






Tana bud'e labulan suka gabza karo da malam dayagama jin komai tayi saurin ja baya tana had'e rai danma kar ya dakatar da ita dan daga kallon irin kallon dayake binta dashi tasan cewa yagama jin komai " muje ciki ko?"








Shine kawai abinda malam yace yana rab'a gefenta ya wuce had'e rai ta k'ara yi tana hararan bayan sa sai dai babu ikon musu dashi dan tun farko basu sabar Masa da hakan ba.






Waje ya samu ya zauna saman kujera mazaunin mutum d'aya yayin da Amina ta zauna agabansa ta sunkuyar dakanta k'asa ita Kuma Nanne ta zauna gefen gado fuskar nan babu alamun annuri ta masifar cin magani dan ma kar malam yace zai hanata zuwa d'aukar ma 'yarta mataki.










Gane take takenta ne yasa malam sakin murmushi yace "Zahra kenan Zahra'u manya Zahra'u sarkin rikici dan Allah Zahra in kin girma kisan kin girma inbanda abinki ina ruwanki da harkar yara 'yar nanfa tasace yana da iko akanta dan me Zaki goyi bayan rashin gaskiya to ban amince Miki zuwa ki zubar min da kima a inda nake da Martaba da daraja dan haka na kashe wannan maganar ke Kuma" ya fad'a yana nuna Amina karna sake hanin kinsa k'afa kin baro d'akin ki akan wani dalili mara tushe 'ya dai tasace Kuma yayi abinda yake so da ita ace danme kar naji kar na gani kinji ko" sosai malam ya rik'a yi musu nasiha har zuwa sanda yai shiru Nanne ta sauke ajiyar zuciyata tace "nifa malam bawai ina goyon bayan Amina bane saboda anbama kishiyarta yarta ba domin da ace suna zaune lafiyane to da hakan mu kanmu saiyafi Mana dad'i amma kishiyarta muguwar makirace datasan kan kissa ta mugunta" nan Nanne ta rik'a bawa malam irin labarin da shamsiyya ta fad'a mata da irin bautuwar da Amina take a siyasance a hannun Sailuba.












Ajiyar zuciya malam ya sauke yace "karku damu domin komai na Allah ne Kuma duk abinda yake damuwa hukuncin Allah ne dan haka kusa aranku duk abinda zai samu mamana daga Allah ne domin babu wani abu dayake samun bawa face da sanin Allah"










Sosai nanma ya kwantar musu da hankali sannan yayima Amina nasiha da hak'uri a duk halin data tsinci kanta hak'ik'a Allah baya barci, yace Nanne taje ta rakata Kennan Baffa yayi sallama' bayan sun gaisa da malam kafin yace komai malam ya soma bashi hak'uri abisa shirmen Amina har Saida kunya ya kama Baffa ya dinga sunne Kai yana dad'a bawa malam sannan yace adad'a bawa Amina hak'uri domin ansan anyi mata ba daidai ba amma yayi hakanne dan samun had'in kansu.
Malam yace babu komai Allah yabada wasu masu albarka.














Tunda suka dawo gida Amina tayi masifar d'auke kanta daga garesu ta daina kulasu duk wani aikin gidan ta ajeshi tsakanin ta dasu sai ido hatta kicin na falonta take shiga, sosai hakan yake sosa ran Baffa shi da kanshi yasan cewa basu kyauta mata ba sun nuna son ransu kuma zata na ganin cewa dan Sailuba 'yar uwarsa ce shiyasa ta nuna son Kai acikin al'amarin.
















Da k'yar yasamu yasha kanta suka koma dai dai haka ma mama kamar yadda ta rad'a wa sailuba suka koma daidai amma Kuma bata Kara yarda tayi mata wannan uwar bautar ba.












Wata irin sangartacciyar rayuwa aka koya Maryam wani irin mugun gata ake gwada mata wanda babu wanda ta ragawa rashin kunya wa kowa sai anyi magana Sailuba tace ai yarinyace haka rayuwa taci gaba da tafiya an mugun tab'ara Maryam duk girman mutum bai wuce ta zageshiba.












Koda Nanne ta kula da yadda Amina ta watsar da Maryam da al amuranta fad'a ta Mata tace yau idan akace Maryam ta lalace kafin kowa yaji ciwon haka kece zakiji domin kece kika san zafinta ita adirenta ta ganta dan haka ita hakan bazai tab'a damunta ba domin batasan ciwontaba haka Nanne tayi ta mata maganganu tare da nuna mata illar kawar da kanta da tayi daga kan Maryam.










To Kuma duk yadda taso Jan yarta ajiki tareda nusar da ita hakan ya faskara see domin Sailuba ta wuce tunanin mai tunani akan komai musamman ta fannin makirci ta kware fiye da zaton me karatu.














Haka rayuwarta yacigaba a tab'arb'are babu kwab'a babu harara duk abinda take so shi ake mata a ta gefe guda kuma tun bayan da ta Kuma haifar yara maza guda biyu duk basu zo da raiba bata sake Koda b'atan wataba sosai abin ya dameta ga matsalar Maryam da Allah yayita da fitinar tsiya ga shegen rashin kunya ga d'an banzan tsokana abin ya masifar damunta amma sai takema yarta addu ar Allah ya shirya.












A b'angaren Sailuba kuwa tunda taga daga Kan wannan yara anja kusan shekara bakwai Amina bata k'ara Koda b'atan wataba hakan ba k'aramin faranta ranta yayiba dan haka ta watsar da duk wani nema da take akanta ta maida dukan wani asirinta akan iya Baffa shi kad'ai riba biyu ga Baffan ta ga Kuma Maryam data b'atar da duk wata hanya da zata gane cewa Amina ce mahaifiyar ta.














Lokacin da MD ya dawo ya tarar da irin tab'arb'are war da rayuwar Maryam yayi ga fitsara ga raini wa kowa ba k'aramin tashi hankalinsa yayiba ya dinga bin Ammey yana fad'an bata kyautaba databar rayiwar Maryam awajen wacce batasan ciwon haihuwaba amma sam Ammey tak,'i kula hakan tama daina sauraron say domin tasan cewa kotayi magana babu abinda hakan zai haifar sai fitina Kuma tun wataran da taga abin yana yawa tayi ma yarinyar fad'a ta zageta ta kuwa kamata ta zane ai kuwa ranar taga ruwan bala I a wajen Baffa dan rufe ido yayi ya tujareta har da mata iyaka da yarta abin ya k'ona mata rai sosai har Saida tayi zazzab'i saboda bak'in ciki shi kanshi Baffa da yaga kamar bai kyautaba yasa ya dinga rarrashin ta daga baya.
















Da farko MD yaso jan Maryam ajiki amma Sailuba bata bada damar hakan ba domin da kanta ta dinga tusa tsanar Muhammad a zuciyar Maryam har taji duk duniya babu wanda ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login