Showing 27001 words to 30000 words out of 82249 words

Chapter 10 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

Advertisement

matsala.
Zuciyar hajiya hauwa ta karfafa sosai tace,
"wannan shawara ce mai kyau tashi mune.
A daidai wannan lokacin babbar aminiyar ummi
wato jiddah tana wurin ummi ta je yimata
sallama don lokacin tafiyarta london karatu ya yi.
Suna zaune dakin ummi su biyu fatima tashigo
sanye da doguwar rika baka after dress ta yi
mata kyau sosai, malam musbahu ne yasayo
mata da sukaje kaduna da malam, suka gaisa da
jiddah. Ummi tace "kinyi kyau mutuniyar bari in yi
miki hoto ,Allah yasa dai angon ya ganki na san
zai yaba wannan kwalliyar.
Tayi wal da ido tace "shi ne ma ya aiko ni da
kwan zabi yace in kawowa hajiya sunje kauye da

malam sukayo tsaraba, bari ma inje yana jira na
anjima zan dawo insha Allahu.
Ummi tace "muje kitchen in ba ki wani lemo dana
hada hirar taku za tafi armashi idan kunayi kuna
sha..
Fati tace "kai antina kina shagwaba mu dayawa.
Tace "haka yadace.
Bayan tafiyar fati tadawo daki gun jiddah tace
"Allah ya sani ina matukar son yarinyar nan
fatima sbda kyaunta da halayenta masu kyau.
jiddah tace "ai na ga alama za a iya dawo da ita
gidan nan idan tafiya tayi tafiya.
Tace "ai da za ta dawo din ai da na ji dadi mama
da abba ba su da matsalar komi gdansu gdan
jama'a ne suna son suga mutane suna ta zuwa
gdan nan.
Ta ce "ai hakan yana da kyau shin kuna waya da
khalifa?
Tarike baki tace "wane ni?
Tunda yatafi suke waya da iyayansa bai taba
tambayata ba, gaskiyar magana jiddah ina ci
gaba da zama a gdan nan ne dan inajin dadin
zaman gdan a dalilin kirkin mama da abba amma
ba na jin zan samu khalifa ya fi karfina.
Jiddah tace "ni abinda yake hada ni dake saurin
karaya har yanzu dasauran batu, idan da rai da
rabo idan kikayi hakuri watarana za ki cimma
nasara akan khalifa, kidaure kici gaba da zama a
gdan nan a matsayin mai yakin neman zuciyar
masoyinki idan kika ci gaba da kyautata masa zai
iya auranki musamman dayake kin shiga zuciyar
iyayansa duka biyun.
Tace "toh Allah yasa inafa cigaba da addu'a na
san bbu abinda yafi karfin Allah.
Jiddah ta mike da niyyar tafiya ta ce "ina takaici
da zanyi wannan tafiyar ni kadai ba tare da ke ba
soyayyar khalifa ta nisanta ki da kowa.
Suka fito suna ci gaba da tattauna maganar
shawarar da bata wuce abinda yashafi khalifa ba
daga karshe ummi tace "jiddah soyayyar khalifa
tayi min yawa a zuciyata abin har tsoro yake ba
ni ,ina ta kokarin ganin na fidda shi a zuciyata
don in huta amma abin ya ki yiwuwa, ina jiyewa

kaina abinda zan iya aikatawa akan kowa idan
narasa shi, idan na rasa khalifa bai auri wata
macen ba nasan zan iya hakura abu daya ne ba
zan taba iya hakura akaiba shi ne khalifa ya auri
wata macen, ina nufin idan zai zauna haka ba na
ganin mace a tare dashi shike nan.
Jiddah taja tsaki tace "ni wannan shirmen na ki
ne ba na so, wadannan maganganu? ba za
subaki khalif ko su hanaki shi ba.
Tace "ni fa ki sani haka jidda ina gaya miki ne
dan ki san abunda ke ckin zuciyata wannan shi
ne abin tsoron.
Bayan tafiyar jiddah gdansu fatima tanufa ta
iskesu ita da musbahu a zaure suna hira, wani
yaro yashigo da sallamarsa yace "wai wani a
waje ya ce don Allah wadda tashigo yanzu tazo.
Ta tsuke fuska tace "kai tafi kace ba za tazo ba.
Malam musbahu yace "haba ummi bai dace kiyi
haka ba mu maza ba ma son muga anawa yan
uwanmu haka.
Fatima tace "malam ko kaje mana kaji me ke tafe
dashi.
Kafin malam yadawo suka shige cikin gida
innarsu fati ta je unguwa a tsakar ida suka zauna
kan tabarma, fati ta bata rai tace "ummi duk
abinda nayi kina bata rai akan banyi daidai ba
meyasa ke nake ganin ba kya iya sauraron duk
masu kaunarki? shin ke abunda kikeyi daidai ne?
ko kuma dan komi ke ce kika iya;?
Malam musbahu yashigo cike da fara'arsa yana
fadin "don Allah ummi kizo kugaisa da mutumin
nan na san shi mutumin kirki ne sosai.
Tace "don Allah malam kasallame shi yatafi kace
an yi min miji kun taba ganin na saurari wani?
Yayi dan jim sannan yace "to ba zan matsa miki
ba amma zan shawarce shi akan yanemi shawra
a gun abbanku.
Bayan fitarsa fatima ta ci gaba dayi mata kallon
tuhuma ranta a bace take fadin "baki ba ni amsar
tambaya ta ba.
Ummi tayi murmushi tace "fati knan kin more
mijinki ma ya mori mace duk abinda kikayi kyau
yake maki batan ran ma da kikayi yanzu bakiga

yadda kika kara kyau da haduwa ba.
Fatima takara fusata tace "ni ba wannan na
tambayeki ba dole sai kin ba ni amsa ta gaskiya
bisa tambayar dana yi miki idan kuma ba haka
ba nima na daina yin abinda ki ke umarta ta.
Ummi tana dariya tace "idan kin kwantar da
hankalinki ko baki bata rai ba zan fada miki
komai.
Ta mike zaune suna fuskantar juna tace "fatima a
cikin rayuwa bbu abinda ba ya samun mutum
wani yasamu yadda yakeso wani akasin haka,
wanifarkonsa yana ckin jin dadi karshensa
wahala, yayin da wani zai taso ne cikin wahala
karshensa yasamu jin dadi, fatima ni kam bbu
wanda zanso a rayuwata bayan mutum daya da
zuciyata ke muradi.
Waye wannan?
Na san ko baki san khalifa a ido ba hotunan da
kike gani a gdansu zai sa ki shaida shi idan kin
gan shi a fili, khalifa shi ne mutumin da zuciyata
ta rataya da soyayyarsa, wannan shi ne dalilin
dayasa ba na kula kowa dalilina shi ne duk
wanda na kula bata mai lkaci zanyi domin
zuciyata ba za ta so shi ba, me ye amfanin in
yaudari mutum in nuna amincewa na gare shi
alhali zuciyata tana tare da son wani, in dai ba
yaudarar mutum zanyi ba to gwara in kyaleshi
bbu wanda zan mallakawa zuciyata bayan shi,
bbu wani da namiji da zai samu farin ciki a tare
dani sai shi domin shi ne nake da kwarin guiwa
dazan farantawa zuciya ko ina so ko ba na so
sbda karfin kaunar danake masa ba mai
misaltuwa bace, son danake masa ba zai bari in
yi abinda zan bata masa rai ba, wannan shi ne
dalilin dayasa nake ta burin ace shi na aura don
in samarwa kaina farin ciki da kwanciyar hnkali a
auran, kuma insamu tsira a gaban Allah idan nayi
mai biyayya, fatima ina zaton wannan shi ne
dalilin dayasa ake ba ma'aurata daman zabar
wadanda suke so yayin neman aure, wanda
zuciyar mutum ta aminta tana so shi take iya bi.
Fatima tace "toh ummi an yi maganar auranku ne
da khalifan kan tafiyarsa ?

Tayi murmushi "fatima in banda khalifan iyayansa
ma basu san ina masa wannan son ba, ya
gargade ni akan kar in sanar da iyayansa
ballantana a matsa masa kan ya aureni, khalifa
ba ya so na ni ce dai zuciyata ba ta iya hakuri
dashi.
Fatima ta girgiza kai"anya kuwa za ki ce kai
tsaye bai son ki ummi ? shin meye abin ki a tare
dake, ko halayyarki ta arziki ta sa mutum yaso
ki.
Tace "Allah sarki fatima ke ce kime ganin haka, ai
ita soyayya ba ruwanta da kirki ko rashinta, idan
kana son mutum to kana sonsa idan ba ka so
kuma ba za ka so shin ba koda ya fi kowa kirki.
Fatima tace "to yanzu meye abinyi ummi ni bar
na ji na tsani khalifan sbda rashin tausayin daya
nuna miki, bai dace ka watsawa wanda yake
sonka kasa a ido ba ya dace yatausaya miki, ni
kam ina bakin cikin wannan damuwa ta ki inama
inada halin taimakonki wlh da sai inda karfina
yakare.
Ummi tace "fatima idan kika biyewa damuwata za
kiyi tazama cikin damuwa ne domin kuwa
damuwa ba ta kare mini don lokacin dana fara
son khalifa nake kuka nake zama a cikin
damuwar da har sai da nasaba da ita, inata
kokarin raba kaina da soyayyarsa don in huta
amma ko yaushe soyayyarsa karuwa take a
zuciyata abin ko sauki ba ya yi, tunda har aka kai
wannan lokacin khalifa bai waiwayeni ba ba zai
tausaya min ta fuskar soyayya ba kuma dagaske
yake bai sona, ban isa in tursasawa khalifa ya
aureni ba dole knan in hakura da auransa, amma
ba zan iya hakuri dashi ba, ba zan auri ko wanne
namijj ba ba zan hakura da khalifa ba.
********
Khalifa ya fara karatu mai zafi a kasar germany
cike da zuciya mai karfi da cikawa mahaifinsa
burinsa na ganin ya zamo cikakken likita dan
yataimaki al"umman musulmai, Anisa tana tre
dashi a gdansa ta zamo tamkar kukunsa itace
abincinsa na safe da yamma a bisa ka'idarsa na
cin abinci guda biyu kamar yadda ya tsarawa

kansa, ko kusa Anisa batayi niyyan zaman gdan
khalifa ba illa soyayya data rinjayi zuciyarta
wadda ba ta barinta tayi tasiri a tare dashi, duk
abinda yace mata dashi take amfani, yana
matukar gamsuwa da nau'ikan abincin da take
shirya masa kuma yana yaba mata tare da nuna
mata jin dadinsa, lamarin dayayi mata dabaibayi
knan take jin cewa data sabawa dr. khalifa gara
ita ta matsawa kanta, babbar abin mamakin shi
ne duk irin yadda ake neman soyayar mace ga da
namiji zuciyar anisa ta gama nisan kiwo a ckin
son khalifa amma a takure take da zaman gdan
na sa sbda bbu abunda yake hadata dashi sai
hirar duniya ba batun soyayya, idan gari yawaye
tagama masa abin karyawa zai fita zuwa
makaranta itama za taje ta ta, idan tadawo sai
tayi abincin yamma, in dare yayi zai shirya ya
dau ado yafice yawon zaga gari yayin dazai barta
a gida kamar wata yar jiran gdansa, sai ya gama
gararin ta zai dawo yabarta a falo yashige
dakinsa, anan take kwana, wani lokacin tanaji
zaiyi ta hira da yammatansa taci kukanta tagaji
tahakura, idan tayi yunkurin barin gdan sai taga
wata dai sabuwar damuwa ce za ta hada kanta
da ita idan ba ta ganinsa.
Yau ta tashi da kasala zuciyarta bbu dadi tahada
abincin safen kamar yadda tasaba tashiga falon
fuskarta bbu walwala, dr. khalifa na zaune teburin
cin abinci bai fara cin abincin ba magana yake a
waya tazauna tana mai kallo, a kullum shi me
kyau ne amma kyaun dayayi yau na daban ne,
wani irin abu taji ya kara turnike mata zuciya,
idanuwanta suka kada jajur tazauna kan kujera
taci gaba da kallonsa yanata hirarsa a waya cike
da nishadi abubuwan dayake fada suka cigaba
dasa zuciyarta a wani yanayi tadinga jin cewa
meye amfani zamanta a gdan khalifa kullum ranta
na baci, bata san inda tadosa ba, ya kamata
tayiwa kanta fada.
Bayan ya kashe wayar ya kawo ganinsa gareta
yace "ya akai sister an tashi lfya ko,?
Wani irin kallo tayi masa wanda bai taba gani ba
tare da ita yataso zuwa gabanta yatsaya

hannayensa zube ckin aljihun wandonsa yana
kayataccen murmushin nan na sa mai kayatar da
zuciyarta amma yau takaici ne yakara rufeta,
hawaye suka taru a idonta tai sauri tashige daki.
Khalifa yatsaya shiru yana kallon kofar dakin nata
cike da mamakinta, ko dayake bai kamata hakan
yazamo abun mamaki ba gareshi don yanada
tabbacin son da Anisa ke masa ne yasa tayi
shahadar zama a gdansa tare da sadaukar da
kanta gun hidimar dafa abinci da gyara mai gida,
hatta gadonsa ita ke gyarawa za tawanke mai
toilet tagyara mai kayan sawar sa da komi na sa,
in banda ya dage akan bai so tai masa wanki da
gugar kayansa da tuni ita ke wankewa don har ta
fara ya yi mata jan ido yace ba zai yiwu ba
ayyuka za suyi mata yawa, ita ba lada zai biyata
ba ballantana yadinga biyanta kudi ,damuwarsa
itace bai san dawani ido zai dubeta ba ranar data
gaji ta bayyana mai batun soyayya da bakinta
tare da bukatar aure, alherinta yanada yawa a
gareshi.
Bai jima da fara zuwa makaranta ba yasamu
aboki guda daya mai suna Faisal wanda yafito
daga gda Nigeria jihar kaduna, Faisal tantirin
matashi ne mai budaddan ido yadda khalifa ke da
farin jinin yammata haka faisal yayi fice a wannan
fannin, sa'ar da akayi shine faisal na da kokarin
karatu, wannan shi ne dalilin dayasa khalifa yaji
dadin abota dashi bayan haka faisal ba bako bane
a kasar germany ya saba zuwa kuma yanada
yammata da yawa, tun da suka fara abota khali:a
yasaki ransa sosai ko yaushe suna tare sai
lokacin barci suke rabuwa anan fa 'yammata
suka fara kawo kansu ga khalifa, son karatu
dayake yasa bai son su shiga jikinsa sosai don
kada su shagaltar dashi.
A yammacin jiya bayan sun kammala da
makaranta wata budurwar khalifa mai suna
shukura dasuke cewa 'shu baby'ta nace akan sai
ta biyoshi gdansa yau dai ta tayashi kwana tace
in kuma bai sonta yafito yagaya mata, yace
"nikam ba na bukatar kwananki a gidana kiyi
hakuri.

Tace "ni na rasa dalilin dayasa kake min haka ko
dai matar aure gareka a gdan.
Faisal ya ja tsaki yace "ke ce kika kwallafa ranki
kan wannan wahallaln ina mamakin dabi'unka
khalifa har yaushe kanada matsayi irin wannan a
rayuwa za ka takura kanka.
Khalifa yace "faisal na fi shu baby bukatar ta a
gidana ina kaucewa hakan ne sbda Anisa.
"Anisa ?
Faisal yafadi ckin mamaki.
Ya amsa mai da fadin "Anisa mana, anisa ta
cancanta in kaucewa abinda zai bata mata rai
tana hidima dani sosai.
Faisal yace "ka ga tunda ba ka iya debe kewar
rayuwa da ita kasallameta daga gdan mana
kadauki yaron gda wanda za ya dinga maka duk
hidimar da Anisa ke maka tunda ba kudin dazaka
biya karasa ba, yaya za ayi kazauna kana
shakkar sakewa a gdan ka sbda Anisa, gskiya
kasauya tunani.
Tausayin anisa yakeji sosai a ransa shi kansa
yana bukatar mai debe me kewa a gidan ba zai
yiwu yadinga kwana shi kadai a gado ba bayan
yanada ikon yin hakan.
Yayi ajiyar zuciya yamike da niyyar yaci abincinsa
yabar gdan, sai yakasa yanufi dakin data shiga
yabude tana kwance rub da ciki bisa gado tana
kuka, yahaye gadon yakwanta kusa da ita yana
shafa bayanta da fuskar ta cikin muryar nan tasa
mai taushi da kayatar da zuciya yace da ita
"bansan dalilin wannan kukan naki ba Anisa in
dai ina da matsayi a gunki na hadaki da Allah ki
bayyana min damuwarki.
Tabude idonta zuciyarta a karaye tace "Abbakar
ba za ka iya min maganin damuwata ba da za ka
iya da bamu kawo wannan lokacin cikin wannan
yanayi ba.
Yace 'haba anisa Allah musuru gareni da zan san
damuwarki har in magance miki ita alhali baki
sanar dani damuwar ta ki ba.
Tamike zaune tana goge hawayen dasuka cigaba
da zubo mata tace "Abbakar meye dalilin zamana
a gdan nan?

Ya amsa "kauna.
Me yasa kace kauna?
Ya amsa "Na san babu abinda zaisa ka zauna da
mutumin da ba ka kauna, dan haka kaunar da
kike min ce tasa kika zauna tare dani.
Bayan wannan za ka iya rantse min da Allah akan
cewa bakasan wani abu a zuciyata ba game da
kai.
Yace "to in banda abinki anisa akwai wanda
yasan abinda ke cikin zuciya bayan Allah?
Ya matso jikinta sosai yakamata yarungume yayi
mata kiss yace "kidaina sawa zuciyarki komi
game dani kidaina bari ranki yana baci duk
abinda kike bukata zan miki.
Ya yi hakan ne dan yahanata fadin abinda yasan
tana daf da fadinsa, yashga shashafa mata
bayanta da cinyoyinta nan da nan jikinta yayi
sanyi tadinga jin wani irin abu na yi mata yawo a
jiki, so ya yiso a zuciyarta kallon kyakyawar
fuskar khalifa ya hanata ta hanashi aiwatar da
abinda yake mata alhali nasihohin mominta na ta
kai kawo a zuciyarta, zuwa can khalifa yadinga
fidda numfashi dasauri dasauri yana cakudata
yadda yaso, abin yafara ba ta tsoro tayi kokarin
janye jikinta daga na sa yayi wuf yakamota yana
fadin "kar ki gujeni a wannan lokacin ke ce kika ja
ra'ayina ba zan iya hakura dake ba ki daure
kibani hadin kai zan maki maki duk abinda kikeso.
Ya kwantar da ita bisa gado yadanneta da
faffadan kirjinsa yarufe ta ruf yana mata kiss,
gabadaya hankalinta ya tashi sosai sai jikinta
yake rawa, a haka dai khalifa yasan ta diya mace
yayi mamakin yadda yasanta a matsayin sabuwar
budurwa wadda bata taba sanin da namiji ba,
dama "yammata suna kaiwa wannan lokacin da
budurcin su?
A DAREN FARKO
15
yamike yayi wanka yafito falo cike da nishadi yaci
abincinsa bai koma dakin ba yafita abin da
yasawa ransa shi ne ashe yanada abar hutawa a
gda tun farko yaki ba ta kai .
Anisa tayi kuka tayi kuka har taba uku lada,

zazabi da ciwon kai suka rufeta takasa tashi,
takira number ramat tace "ke ni fa ba zanzo gdan
wannan abin jin kan tsiyar ba ke dai da kike
mayen sonsa kikaga za ki iya zaman gidansa sai
kiyi tayi, ni dai ina ba ki shawarar kidauke ranki
akan khalifa ba za ki iya mallakarsa ba ke ko kin
mallake shi wahala za kisha dan namiji ne me
garari da tsada.
Anisa ta jefar da wayar taci gaba da kuka sam
dawani ido zata dubi mominta ko da ta san cewa
ba za tasan abinda yafaru ba abin takaici ne ace
ta karya alkawarin datayi wa momin ta ta na
cewa za ta rike mutuncin kanta, shin ina
makomarta a gun khalifa, shin meye amfanin
zuwanta germany ne?
****
Bayan tafiyar jiddah london karatu abunda su
hajiya sude suka maida kai shi ne yawon gdajen
malamai da bokaye wai su burinsu khalifa yaso
ummi ko ta halin kaka, mafi yawan malamai na
bayyana musu cewa khalifa fitinannen yaro ne
mai jarabar kwadayin mace amma bbu batun aure
ko kadan a zuciyarsa, haka shi mutum

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login