Showing 81001 words to 82249 words out of 82249 words

Chapter 28 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

yazauna
da matarsa, kina ji har cewa take sai ta zamo
ajalina.
Inna tace "ke ba komi irin barazana ce yau kika
fara jin inda akai irin wadannan abubuwan, to ki
dogara ga Allah matar usman ba kowa bace akan
wasu matan don duk abinda kayi wani ya ninka
naka kuma anga karshensa, haka duniya tagada,
duk wannan abinda tayi ta yi ne don a tsorata
ace an fasa idan an fasa din taci galaba daga nan
ta samu damar takawa yadda take so, ki kwantar
da hankalinki addu'ar da muku da wadda kikeyi
insha Allah za tabaki kariya ba abinda zai sameki
sai alheri, ba na son ki gayawa kowa ma.
*****
Jikin fatima yayi sanyi sosai har dare ba ta da
kuzari, lokacin da usman yazo ma haka tafito
masa fuskarta ba walwala sai yaji duk abin
duniya ya yi masa zafi.
Yace "fatima meke faruwa ne akwai damuwa a
tare dake don Allah ki gaya min,.
Tadago tayi mai wani irin kallo tace "dama haka
matr ka take?
Gabansa yafadi yace "me yafaru?

Ta labarta masa duk tijarar da farida da kawarta
sukayi musu, ransa yabaci yace "na ji dadi
datazo har gda ta nuna muku mugun halinta, ai
da farko na fara gaya mikikikace ba kya son ji,
don Allah kiyi hakuri zan dauki mataki a kanta,
barazaana ce kawai don ta tsorataki babu
abunda ta isa tayi miki ke ba a garin ma za ki
zauna ba a ina za taganki ballantana tayi miki
wani abu.
Ganin fatima ta ki sakin ranta hankalinsa ya dada
tashi, sai kawai gani tayi ya durkusa a gurin yana
bta hakuri, tace "haaba haba usman ba girmanka
bane.
Yaki mikewa tsaye yace ba zai tashi ba sai ta ce
ta hakura, dasauri tace "na hakura na hakura.
KARSHE
karfe sha daya aka tabbatar musu da cewa an
daura auran usman da fatima, farida tayi kasa
tana birgima tare da fadin "ahikenan na shiga uku
na gama yawo.
Isha ta daga ta tace tashi baki shiga uku ba,
fatima abin da za ayi shi ne idan usman yadawo
gdan nan kinuna masa kuranki da nadamarki, ckin
ruwan sanyi sai mu gasata mu korera da kissa.
Gaba daya sukayi na'am da wannn shawara.
Karfe goma sha biyun dare usman ya iso gdan,
har zai wuce dakinsa sai dai yafasa ya murda
kofar dakin farida,. Ga mamakinsa sai yaga ta
saki fuskarta ta amsa mai sallama tare da mai
sannu daxuwa.
Usman ya saki baki galala yana kallonta cike da
mamaki da farin cki a zuciyarsa.
Da gari ya waye ne take tmbayarsa ina za akai
amaryar bataga anyi shirin komi a gdan ba.
Yace "ai abuja za mutafi da ita anjima tunda kin
ga gdan nan ya yi muku kadan. tace ai ma hakan
yayi daidai kaima za kafi jin dadin zaman abujan
amma dai zanyi rakiya ko tunda dama ban taba
zuwa ba.
Yayi dan jim bai so hakan ba amma ya daure
yace "shknan sai ki shirya mutafi.
****
Karfe go;a sha biyun ranar talata an gama shirya

amarya fatima za a tafi abuja, shi kuwa ango da
uwargda suka taho a sabuwar motarsa.
Babbar hudubar hajiya itace "kin san dai baki
taba budar ido kin ganni dakishiya a gdan nan ba,
haka yan uwanki idan kim saki baki kin zamo
wadda tarako mata duniya, xa kizo kina nadamar
da za tasaki kuka da idonki.
Farida tasaki ranta sosai kamar ba ita ba ta
gayar da dangin mijinta tare da tmbayar ina
amaryar take za taje su gaisa,jidda da tafi kowa
tsanar farida tayi tsagal tace "kin ga malama ba
ruwanki da amarya kiyi harkarki tayi ta ta.
Farida tayi murmushi tace "haba jidda meye don
na ce zanje mugaisa.
Daya daga cikin yayyan usman hajiya hadiza tace
"kin ga dakin nan shiga ni ban son hayaniya.
Tamike tashiga dakin da aka nuna mata tayi
sallama, suka amsa tace "na san baku sanni ba ni
ce farida matar usman na rakoshi taryar amarya
ne.
Daya a cikinsu tace "ai kin kyauta mun gode
sosai.
***
Farida ta kwana ne a dakin usman sbda ta
marairaice masa yan uwanta dana fatima
tsangwamarta sukeyi, har ckin ransa ya amince
da ita har yaji a ransa ba dadi, yace to tadawo
dakinsa tazauna kawai.
Tayi ta amfani da damar data samu gun jan
ra'ayinsa yana bata kulawa, da safe ma bata
barshi ya fito daga dakin da wuri ba duk da ya
san da yan baka a gdan amma sai yadinga ji da
farida bai son damuwarta, har su jidda suka
gama hidiman cin abincin su da wanka.
Farida dashi usman din suka shigo, farida tai
saurin zama kusa da ita takamo hannunta tace
"haba amarya wani irin kuka ne haka kamar
zamanin da, sbda fa in deve miki kewa nazo in
dan tayaki zama kafi? ki saba don Allah ki hakuri
ki saki ranki.
Farida ta kalallame usman tahana shi sakewa da
fatima da zarar zai shiga dakin sai tabi shi tana
fadin, "man muje muga halin da amaryarmu ke

ciki. Shi duk bai san kishi bane ya dauka dai
kyautatawa ne shiyasa yake biye mata.
Farida tabar usman a falo tashiga daki ta fada
toilet takira wayar isha take tambayarta yaya za
tayi tahana uaman kwana da fatima.
Isha tace "shiga za kiyi dakin ke kadai ki nuna
mata wuka ki cemata wallahi idan tayarda usman
yashigo lallai sai kin kasheta, idan usman
yashigo lallai tai ta ihu har sai ya fita, to da
zarar ya fito ke kuma sai ki janye ra'ayinsa kuyi
daki, gobe kuma sai mu shirya mata wani tuggun
a haka har yagaji da ita yakoreta kiyi zamanki a
abuja.
Farida ta kyalkyale da dariya tace 'kai Allah yabar
mana ke isha kin iya tsara tuggu shiyasa nake
sonki.
Tace "sai kinji ni aminiyar...
Ba karamin frgita farida tayi ba, jikinta yadauki
rawa sakamakon ganin usman tsaye a kanta yana
mata wani irin kallo.
Ya zabga mata wata muguwar harara yace
"kaiconki Farida,zuciyarki tana miki saka da
mugun zare, dama biyoni kikayi don ki rabani da
matata ko?
Allah bai baki sa'a kin kori fatima ba kanki kika
kora, don ina son ki tattara ki bar min gdana na
sake ki.
Faida takwala kara zata fara yi mai hauka yafice
yashige dakin fatima ya sama kofar key,.
Fati tatashi a tsorace tana kallonsa, nan da nan
idonta yaciko, yayi murmuahi yace "haba fatima
sai kace kinga dodo.
Tashiga mai magiya, ko kula ta baiyi ba yakashe
fitila, tun tana kokarin kwatar kanta har tagaji
tahakura.
****
Da kyar fatima tatashi tayi sallan asuba taci gaba
da barci, bata farka ba sai sha dayan safe.
Ta tsuguna tagaishe shi cke da fara'a ya amsa,
tace "ina anty farida mu gaisa?
Yayi tsaki yace "ba ta gdan.
Ina tatafi?
Bansan inda tatafi ba.

Tayi mai wani iein kallo wace irin magana ce
wannan?
Yajawota jkinsa dakarfi yahadeta da kirjinsa
takama kuka tana kici kicin kwacewa.
Yace "dama kin hakura kin hadu da cingam.
Hankalin fatima yakara tashi ganin yadda yake
neman cire mata riga, Allah yabata sa'a tafisge
kanta ta gudu ckin dakinta.
Kafin tarufe kofar ya danna kai yatsaya yana
mata dariya, yace "kin fiye tsoro fatima.
Ta durkus tana fadin "Don Allah kayi hakuri na
tuba.
Yarungumeta tsam yana shafa mata jiki, yace
"wai don Allah fatima so dadi gareshi ko wahala?
Me yasa ciwon so yakeda daci a zuciya?
Me yasa soyayya ba ta barin zuciya tazauna
lafiya.
Ba ni wannan amsar".
Alhamdulillah.
Daga taku
RABI'ATU NASIDI ABUBAKAR.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login