Showing 39001 words to 42000 words out of 82249 words

Chapter 14 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

cewa asibiti za su
yace zai aaiko musu da kudin dama sun saba
dahaka duk abinda suka bukata zai musu iya
ikonsa amma ba sa gani, su dai matarsa da
dansa ne ba sa so dashi kansa sai dai dukiyarsa
A DAREN FARKO
20
Fitar ummi yakara dagawa fatima hankali sosai
takifa kanta a cinyarta tana sharar kwalla,
meyasa dr.khalifa zai mata haka, ya ya za ayi
yarasa wadda zai fadawa cewa ma yana sonta
sai ummi wannan ba karamin cin fuska bane da
walakanci, duk abinda zai sa ummi tayi hushi da
ita abin ya yi yawa ko da yake ta san dole ne
ummi tayi fushi da ita akan dr. khalifa, ba wanda
ummi ba za ta iya juyawa ba sbda son datake
masa ba kadan bane, ta gaji da kukan bakin ciki
da takaici tatashi a sanyaye. zata tafi gda taci
karo da mama a harabar gida tana magana da
ado me musu wanki da guga, yanayin ta da
mama tagani yasa tayi saurin matsowa daf da ita
tace " 'yammata lafiya ? kukan me kikayi haka ?
Ba kuka nayi ba wani abu ne yafada min ido.
Tace "ina ummi ?
Tace "ta fita ban san ina taje ba.
Tace "ke ina za ki yanzun ?
Tace "gida za ni yanzun xan dawo.
Kamar zata hanata tafiya sai tayi tunanin bai
dace ba batasan abin da za tayi ba don haka ta
kyaleta tatafi tadawo falo tazauna.
Dr. khalifa yashigo cikin shirin fita yazauna suka
gaisa tace "ba za kaci abincin bane naga ka yi
shirin fita ?
Ya girgiza kai"ba zan iya cin komi ba xuciyata
tana ckin damuwa bansan mafita ba a cikin halin

danake ciki.
Mama tayi murmushi tace "khalifa Allah (SWT)
daya halicce mu cewa yayi "ban halicci mutum da
aljan ba sai don su bauta min, to ni dai a ganina
ba wani abinda zai dagawa mutum hankali akai
in dai ba bautar Allahn nan ba, to ita kanta
bautar Allah ba zafafa mana akai ba, Allah ba ya
daurawa wata rai sai abinda za ta iya, in kuwa
haka ne bbu abinda zai zamo mai tsanani a cikin
wannan rayuwa ko meye shi kuwa, musanman
ida mutum yana la'akari da rayuwar duniya,
wadda fararriya ce kuma kararriya, duk wani abu
dakasani dayake a cikin duniyar nan a dayan biyu
yake, ko dai ka kare kabar shi ko shi yakare
yabarka, to meye dalilin damuwa.
Khalifa yayi ajiyar zuciya yace "mama na san za
ki yi min shaidar hakuri da kau da kai a cikin
al'amarin rayuwa idan yataso min, mama a
wannan karon na samu kaina a yanayin dana
kasa mallakar kaina, don na sa hakurar da
zuciyata tayi hakuri da abinda take nema.
Wallahi ji nake k ; ar zan mutu sbda ciwo fmda
radadin da nakeji a zuciya ta.
Mama tayk mai zumu da ido tana kallon fuskarsa,
tabbas yanayin fuskarsa ta nuna tabbatar da
abinda yake fada haka ne, tausayin sa yakamata
amma tjure don kada ta dada karayar mai da
zuciya tace "khalifa daman akwai abinda ba za a
iya hakura dashi ba a duniyar nan ? a matsayin
mu na musulmi munyi imani da cewa dukkan
abinda yasa me mu haka Allah ya kaddara mana
kuma ba mu da ikon kaucewa abinda Allah
yakaddara mana ,kadaure kayi hakan mana.
Yace "mama ba zan iya hakuri da fatima ba, don
Allah ki taimake ni duk yadda za kiso alheri a
gdan wanda za a ba auran fatima ba kamar a
gdan nan ba.
Mama ta jima kanta a kasa tarasa abinda za
tace, Dr. khalifa yaci gaba da fadin "wlh mama
babu abinda zan iya aiwatar wa a rayuwa ta in
dai ina cikin wannan yanayin ni dai kisha min kan
yarinyar nan da iyayanta ina matukar kaunarta.
Tace "khalifa wace irin son zuciya kake son mu

aiwatar ne ? don Allah kayi hakuri.
Ya tareta dasauri yace "don Allah kada ki ba ni
umurnin yin hakuri ina son fatima dayawa zan iya
kowani irin hali idan ban mallaketa ba, ke za kiyi
hakuri ki taimakeni ba wai ni zanyi hakuri ba
waye zai iya hakuri da abinda yake so mama"
Tace "ahi ke nan kabani kwana biyu zanyi tunani.
Nan take mama tgano dalilin kukan da fatima ke
yi knan, to kuma meye dalilin fitar ummi da safen
nan ba tare da ta sanar dakowa inda za ta ba, ta
kira wayar ummin a kashe takira hajiya hauwa ita
kuma tana ringing ba a daga ba, ta aje wayar a
gefe tayi tagumi tunani ya sha mata kai, shin
yaya za ta yi da wannan al'amari, tana bukatar
shawara, ko dayake duk wata shawara ba ta
wuce ta lallashi khalifa yayi hakuri ba domin
wannan son zuciyar ba yiwuwa zaiyi ba.
Takira sadiya kanwarta dake tayata zama a gdan
a dalilin mutuwar auranta tashaida mata abinda
ke faruwa.
Sadiya tace "tabdijam wannan ai babbar magana
ce.
Tace "to sadiya nima haka nagani, na rasa ta ina
zan gano mafita.
Sadiya tayi murmushi tace "to amm fa mama so
so ne sonkai ya fi, tun kafin khalifa ydawo kasar
nan idan nakalli fatima nakanji sha'awar ina ma
itace khalifan zai aura, hakan yasa ba na so ma
in ji ana hirar auranta me zai hana tunda dai
khalifa ya nuna wannan damuwa ta sa mu san
yadda za muyi ya aureta dama ance matar
mutum kabarinsa wani bai auran matar wani.
mama tagirgiza kai tace "kai anty sadiya anya
wannan maganar ta yi daidai kuwa ?
Sadiya tace "ta yi dai dai mana mama abinda
yasa nace dake haka, idan khalifa bai samu auran
fatima ba ba zai maida kansa kan aure ba
sannan tunda ita yakeso in ya aureta hankalinsa
zai kwanta sosai, yarinya ce mai hankali da
natsuwa, gskiya mama kada muyi wannan
sakacin daga karshe mu zo muna nadama.
Mama takwantar da kanta bisa kujera idonta na
kallon silin, sadiya ma ta zo da maganar daya

cancanta a duba, abin ne da nauyi dole kam tsan
abin yi in banda wannan matsalar ta fi kowa son
khalifa ya auri fatima sbda fatima mace ce tagari
to ya ya za tayi tadubi fati tace tafasa auren
musbahu ta auri khalifa ???
******
Tunda fatima tashiga gdansu bayan gaisuwa
datayi da iyayanta bata kara cewa kowa kmi ba
tashiga dakin innarta takwanta tana ci gaba da
hawaye.
Inna ta tambayeta damuwarta tagaya mata komi
tace "tabdijam abin da malam ke gudu ne yafaru
kin san shi Alhaji baban khalifan ya taba cewa
yana son malam yaba dansa auranki yace ya riga
ya ba da ke.
Fatima tace "to ai inna ko da ba a bayar dani ba
bazan taba amincewa khalifa ba, sbda aduniya
dai banga da namijin da ummi ke so irin sa ba,
ummi ba ta da burin daya wuce mallakarsa, ta
kwallafa rai a kansa tana matukar so da
kaunarsa.
Matsayin ummi gareni ya wuce in yi mata haka,
don Allah inna kada ki saurari maganar khalifa ba
shi da tausayi bai da adalci.
Tace "to ina ma za ayi haka ? dole yahakura.
Fatima tadinga nacin kiran ummi a waya wayar a
kashe take, dole taje ta lallashi ummi, ummi ta fi
komi a gareta.
Bayan sallar azahar tashaidawa inna za ta
gdansu ummi tace sai ta dawo, ko ganin gdansu
dr. khalifa ba ta son yi ,sbda takaicin ya cuceta
ya hadata da babbar aminiyarta abokiyar
shawararta.
Tana tsaye bakin titin kan layinsu tana neman
adaidaita sahu kawai sai ganin mota tayi ta yi
fakin a gabanta, bakaken gilashin da aka zuge
yabata damar ganin wanda ke ckin motar. dr.
khalifa ne gabanta yafadi tsmatsa dasauri tana
masa wani irin kallo, yace "ina za ki ne fatima. "
Tayi shiru kamar ba da ita yake ba, yace "don
Allah kigaya min inda za ki in kaiki.
Anan ne ta hasala tace "ina ruwanka da inda za
ni, ni ba neman taimakon mota nake ba.

Yakashe motar yafito yana kare mata kallo daga
sama har kasa, yana murmushi a wannan lokacin
ne yadada tabbatarwa kansa yana son fatima
kuma ba zai iya sakacin dazai rsata ba insha
Allahu wannan yarinyar matarsa ce ta sunnah.
Kwatsam adaidaita sahu ta tsaya a gabansu,
ummi ce tafito idanunta fes akansu bata ce komi
ba tabiya dan adaidaita kudinsa tawuce za ta
tafi, fatima tabita tana fadin "ummi ai gdanku za
ni Allah ne yataimaka bamuyi sabani ba.
Ummi tajuyo suka hada ido ,kallon datake mata
yana dagawa fatima hankali, tawuce dasauri
tabar gun, ta tsaya sororo tabi ummin da kallo.
Dr. khalifa ya iso gabanta yace "fatima don Allah
ki tsaya ki saurareni, zuciyata tana matukar so da
kaunar ki don Allah ki tausaya min.
A fusace tace "ai kai ba abin tausayi bane, babu
wani dalilin dazaisa a tausaya maka, tunda kaima
ba ka tausayin mai sonka, tun yaushe ummi take
fama da ciwon sonka a zuciyarta amma ka ki
kadubeta kake walakanta ta sbda kawai tana
sonka ?
Yazuba mata ido yana murmushi wai shi yarinya
kamar fatima ke wa tsiwa haka, son da yake
mata ya yi tasiri da isarsa ta namiji ba zai yi
komi a kanta ba, a iya rayuwarsa bai taba samun
kansa a yanayi irin wannan ba.
Tayi tafiyarta tabarshi a gun yana binta da kallo,
gumi yana yanko masa har ta bace sannan
yashiga motarsa yaja zuwa gdansu.
Baiyi tunanin nan gdan na su fati za tazo ba sai
yaganta za tashiga yayi murmushi kawai ,tafizge
kanta tashiga ckin gda tayi sa'a mama ta fita
anguwa sai 'yan aikin gdan suna hidimomin su,
ta iske ummi a daki tana hada kayanta .
Ta amsa sallamar fatin ba tare da ta kalleta ba,
fatima tazauna a bakin gado muryarta a kasa
kasa takira sunan ta, ta waiwayo tace,"na'am
fati.
Tace "ummi meye laifina akan wannan al'amarin
lokaci daya za kijuya min baya ki tsane ni ? shin
ni na budi baki nace ina son khalifa ? ko zuwa
nayi sashensa naja ra'ayinsa don yasoni ?

Ummi tayi mata wani lalataccen kallo tace "ke ki
kama kanki, kin san dai ban tare ki dawata
magana ba akan khalifa, don haka ba na bukatar
kiyi ta nemana dawasu maganganu.
Fatima tadaga murya tace "wlh ummi ko kusa
bakiyi min adalci ba, na yi zaton a gun ki zan fara
samu shaidar wani da namiji va zai taba samun
masauki a zuciyata ba, ko ina son khalifa ko babu
maganar musbahu a kaina ba zan taba ba, dr.
khalifa fuska ba sbda na san waye shi a gunki,
ballantana kwanaki suka rage a daura min aure,
hakanan ba na son shi ba na ra'ayin shi to meye
na damuwa, don Allah ummi kada kidauki alhaki
na kada ki watsa mana zumunci ki kwantar da
hankalinki insha Allahu ta hanya ta za ki iya
mallakar dr. khalifa in dai Allah ya kaddara mijinki
ne zan yi amfani da damar dana samu a kansa in
ja ra'ayinsa gareki amma fa sai in na samu hadin
kanki.
Ummi tayi dif tan juya maganganun fatima
wadanda sukan saurin fisgar hankalinta tadawo
natsuwarta, idanunta da zafin kishi yasa suka
rufe suka bude domin ta fara jiyo kamshin nasara
a maganganun fatima.
Ta taso tadawo kusa da fatin tazauna muryarta a
hankali tace "kiyi hakuri fatima a cikin gaba daya
al'amura na ba na wasa da dr. khalifa sbda
soyayyar danake mishi, ban taba jin za a wayi
gari watarana inji ba na san na budi ido in ganki
ba sai ranar da dr. khalifa yabudi baki yace min
"ke ce mace daya dayake so ya aura a duk fadin
duniyar nan, a wannan lokacin ji nayi na tsaneki
fatima duk da na san ba laifinki bane ba ke kika
sa yasoki ba amma wannan baiyi tasirin daya
Hana inga laifinki ba.
Fatima tayi murmushi tace "ke ma ba ki da laifi
ummi domin ba laifi bane don mutum ya yi kishin
abinda yake so, ballantana soyayya irin ta ki ga
dr. khalifa, hnkalina ya tashi don sabon danayi
dake ta ina zuciyata xa tasake kin juya min baya,
ummi inason ganin kin mallaki dr. khalifa don
haka zn daure shi da jijiyoyin jikinsa tunda ya ce
yana sona to ya kawo kansa garemu, kiyi hakuri

da duk abinda za kiga yana nuna mini na so,
kafin mu cimma burimmu, kuma kibashi hadin kai
a duk maganar dazai miki a kaina ki nuna mai kin
goyi bayansa, xai kasance yana son magana dake
sbda hirata da kuke.
Nan take ummi taji zuciyarta ta yi mata wasai,
kaunar fatima takaru a zuciyarta, tafasa hada
kayanta tabar gdan kamar yadda tayi nufin yi,
bayan tafiyar fatima gda takira wayar hajiyarta
tashaida mata yadda sukayi da fatima, hajiya
tace "anya kuwa dagaske take ummi ? kada fa
tayaudare ki, sai wahala ake awai wata manufa a
zuciyarta.
Hajiya tace "to ki dai yi taka tsan tsan kuma
kisan yadda kikayi kika kawo mana abubuwan da
malam yace a kawo wadanda suka shafi khalifan.
******
Cikin dacin rai fatima tadawo gida tana takaicin
son zuciyar dr. khalifa duk da ta san ba zaiyi
nasara a kanta ba amma abin yana ba ta haushi
sosai, ga mamakinta sai ta iske mama da anty
sadiya a gdan na su suna hira da inna ga zogala
a gabansu suna ci.
Ta fadada fara'arta tace "lah mama dama nan
kika shigo.
Tace "eh amma mun biya kasuwa kafin mushigo
nan din.
Inna tatashi tace "bari in tuka tuwon nan in hada
miya in dawo.
Mama ta ji dadin fitar inna tace " 'yammata na
zo ki zauna anan kiji wata magana.
Daf da ita fati tazauna tace "wannan zuwan na ki
ne don gunki muka zo.
Tace "ni mama.
Tace "kwarai kuwa fatima ko baki kai matsayin
daza muzo gunki ba.
Tayi kasa da kanta tana girgiza kai, mama tace
"fatima munzo da kanmu ne nan dan kidauki
abinda mukazo miki dashi da mahimmanci, a
wani lokacin idan za kagawa mutum abu mai
muhimmanci to kadubi yanayin dazaka fada masa
dan yafi kama batun da daraja. fatima na san
matsayin uwa nake a gunki ckin gdan nan na san

bbu abunda xan nema in rasa shi sai fa in ba ku
dashi.
ko da yake maganar danazo miki da ita mai nauyi
ne amma duk da haka nauyinta ba zai hana in
gaya miki ba, sbda na san wacece ni a gunki, ba
kuma ina nufin yin amfani da wannan damar bane
in tursasa ki ba a'a alfarma ce nake fatan kiyi
min.
Fatima dan uwanki khalifa ne ke neman alfarmar
ki amince mai ya aureki sbda ke kadai ce
zuciyarsa ke so, kuma ta aminta ya aura.
Tunda mama tafara magana fatima tasan inda
tadosa, dataji ta yi shiru tace "mama duk abinda
kika fda haka yake, kuma alfarma kowace iri zan
yiwa kowa a gdanku amma a wannan karon sai
dai in ba ki hakuri mama abu guda daya ne zai
hana in amsa wa yaya khalifa soyayyarsa itace
ummi.
Ummi kuma fatima ?
Me ya kawo ummi ckin wannan maganar ?
Fatima tagyara zama tace "mama ummi itace za
tayiwa yaya khalifa shamaki dani domin kuwa ta
fi karfin in auri wanda maitar so da farautar
nema, ummi tana tsananin so da burin auran dr.
khalifa ,da wani ido xan dubeta in na aureshi,in
banda haka da a yau dinnan xan tabbatar miki da
matsayinku a gareni mama ta hanyar amsar
bukatar dr. khalifa, kiyi hakuri mama ki taimaki
rayuwar ummi ki ceto zuciyarta daga halin datake
ciki ta hanyar sa khalifa ya aureta, mama kin zo
gdan nan ne nasan sbda ttausayn sa di kikeji da
gudun fadawarsa wani hali idan bai samu yadda
yake so ba, mama to kisani ummi ta fidr. khalifa
kuncin zuciya don shi a cikin kwanaki kalilan yake
fama da ta shi damuwar yayin da ita tadade tana
fama da damuwa, akwai daran datake kwana
kuka akwai ranakun da ko abinci ba ta iya ci,
,kullum ciwon rai ke damunta akan dr. khalifa, in
dai akwai abin tausayi ta fannin soyayya to ummi
ce, kiyi hakuri mama kituno hadisin manzon
rahama (SAW) da yace imanin dayanku ba ya
cika har sai ya kasance yana sowa dan uwansa
abinda yake sowa kansa.

A DAREN FARKO
21
A cikin uwar dakin mama ita da anty sadiya ne ke
zaune suna fama da magana daya dai dataki
karewa, khalifa yashigo fuskarsa ba walwala
yazauna kan stool yana fuskantar mama yace
"gani"
Tace "khalifa don Allah kayi hakuri da batun
fatima ba za ta amince da batun auranka batunda
dai har nataka kafata har ckin gdansu na roki
alfarmarta bata amince ba, karshe ma tashiga
kawo min wa'azi wai yadda naji tausayinka a
matsayinka na da na har nake fafutukar ganin ka
samu abun da kake bukata to itama ummi in
tausaya mata in taimaketa ta aureka.
Khalifa yaja dogon numfashi yace "wlh mama ni
ma bansan abunda ke damuna ba, na kasa hakuri
da yarinyar nan wani irin abu nake ji a cikin
zuciyata kamar idan ban samu auranta ba
mutuwa zanyi, ina jinjina wannan yanayi danake
cki mama, a ni kaina ba na ra'ayin auran zumunci
ba zan auri ummi ba, fatima kuma yanzu nafara
sonta ki ci gaba da kokarin taimakona da addu'a
da duk abinda za ki iya mama.
Wayarsatafara ringing yatashi yafita, mama taja
tsaki tadubi sadiya tace "to yanzu me za muyi,
nikam ban san abinda za a zarge ni da son
zuciya, ba na son in ja wa kaina zagi.
Sadiya tace "kidaina damuwa mama in fa fati
matar khalifa ce sai ya aureta, dole muci gaba da
jan ra'ayin fatima tunda ita yakeso itace farin
ckinsa.
Bayan dr. khalifa yagama wayar da aka kira shi
dakin ummi yanufa tana zaune tana duba wani
littafi, ta amsa mai sallama cikin fara'a, yazauna
gefen kujerar dake gaban madubi ya amsa
gaisuwar tayi masa yace "ina fatima?
Tana gdansu.
Ya gyada kai "ummi"
Ta amsa "na'am yaya khalifa.
"Ba ki da wata hanya daza ki iya ja min ra'ayin
fatima, ina sonta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login