Showing 69001 words to 72000 words out of 82249 words
Chapter 24 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf
Bashir yace "Allah ta tashi kaine kake kara
shagwaba yarinyar nan.
Khalifa ya lallaba fatima ta tashi tafara tafiya da
kyar takai bango tadawo za ta zauna, Dr. Bashir
yace "a'a bai isa ba cigaba da tfya.
Khalifa yafusata yace "Kada Allah yasa kadubata
in dai sai ta cigaba da wahalar tfya kana gani fa
dakyar take tafiya.
Bashir yayi murmushi yace "Abbakar kaine ka
haifarwa da fatima wannan ciwon.
Yaja tsaki "To ina ruwanka kai dai kayi aikin ka
mana ni ban son sa ido.
*****
An yanke shawarar sai an kai fatima gdan wanda
yahada da yini da party guda biyu amma a ranar
da za akaita da yamma za ayi kamu hade da
walima, ta dai ji sauki sai abinda ba a rasa ba,
tun a safiyar yau lahadi tadawo gdansu, a gdan
dan hausa aka shirya za ayi kamun, ango da
abokanansa ma za su halarci gun domin za ayi
kamun ango daga karfe hudu zuwa biyar xa ayi
komi a gama, dan haka karfe uku da rabi na
yamma aka fara daukar mutane zuwa gdan dan
hausan, mawakan zamani na ta cashewa ana
wasa ango da amarya da iyayansu mama da
abba da inna ma sun halarci gun malam ne yace
va zai je ba.
Yau shigar ango da amarya ta kasnce dark da
light brown, shi shadda ita less, abin ba a
magana kyau an yi shi sai wanda yagani duk
wanda yake gun ya yabawa haduwar ango da
amarya sbda sunyi kyau na daukar ma'ana ayau
an ga abinda ake kira matching, kalandar da aka
raba a gun ta ja hankulan mutane da yawa domin
anyi hoton ne a wani irin yana yi me ban sha'awa
wanda yake tabbatar wa da jama'a tsananin so
da kaunar dake tsakanin ango da amaryarsa.
Lokacin da mawaki yanemi fitowar ango da
amarya filin rawa don su taka rudewa gun yayi
domin cewa yayi zai ga wanda zai riga wani
mikewa tsakanin ango da amarya.
Fatima tayi wuf tariga dr. khalifa mikewa, gaba
daya aka shiga tafa mata, mawaki yace "kyautar
fatima tafarko ce sannan ta dr. khalifa tunda ta
rigashi mikewa.
Lokacin dasuka iso filin rawan, iyayansu da
abokai da dangi aka dinga yi musu ruwan kudi
har ya kasance babu abunda kake gani a gun sai
sabbin kudi suna tashi sama da kasa.
Karfe biyar da rabi akayi kamun amarya karfe
shida kuma akayi kamun sngo, shida da rabi aka
rufe taro da addu"oi na musanmman daga
manyan kuma shaharrarun malamai, bakwai
saura kwata aka tashi.
Karfe takwas aka shiga wata liyafar inda malamai
mata suka yiwa ango da amarya fadakarwa ta
awa daya kachal yadda za su zauna da junan su,
karfe taran dare aka dauki amarya zuwa dakin ta
bayan iyaye da yan uwa da abokan arziki sun yi
mata nasihar zaman lfya tare da addu'ar Allah
yasanya wa aurensu alheri tare da albarka.
Duk inda amarya tagifta sai kamahi mai dadi da
sanyaya zuciya ke tashi.
*****
Wannan shi ne asalin labarin masu karatu sai
kuyi jimirin biyoni kuji yadda aka kaya, an dai
kashe Dr. khalifa a DARANSU NA FARKO da aka
kai fatima, shin waye ya kashe Dr. khalifa ? shin
ina labarin musbahu ku biyoni.
*****
Karfe shida daidai na yammacin Alhamis jirgin da
ya taso daga Lagos yadire Jidda a airport din
Malam Aminu Kano dake birnin kano, tana rataye
da jakarta ta hannu, tashiga motar gdansu da
aka zo daukar ta, tana shiga gdansu aka rude da
murnar ga jiddah ga jiddah, ta zauna a falom
mahaifiyarta suka gisa tare da tambaye tambayen
'yan'uwa da abokan arziki.
Ummansu tace "ke dai jiddah idan kika sawa
ranki abu sai kinyi shi har yaushe kikaje london
din da za kice sai kin zo hutu ?
Tace "wallahi umma nima banyi niyyar zuwan ba
haka kawai a wannan satin naji gaba daya
hankalina ya tashi da zaman london din ga
mafarkai ina tayi marasa dadi nayi nayi in jure na
kasa kwana biyun da suka wuce ko barci bana yi
sosai.
Umma tace "To Allah yasa alheri, Allah yarabamu
da muagun ji da mugun gani.
Tace "Amin, ina Abba ? "
Tace "Ya fita amma tunda yamma tayi yana
hanyar dawowa.
Tace "Bari in yi sallah in je gdan su Ummi wai
tana shigowa kuwa na san rashin kirkita.
Umma tagirgiza kai tace "Wayyo Allah ai ummi
gaba daya ba ta ckin natsuwarta hankalin kowa a
tashe yake sakamakon wani abin tausayi daya
faru.
A firgice jiddah tace "Mr ye umma ? ko shiyasa
idan namata waya ba ta shiga a kwana biyun
nan ?
Tace "ai idan kikaga ummi sai kin tausaya mata
sbda firgicin data shiga ai na yi zaton ta gaya
miki a waya ma ?
Jiddah tace "wai me yafaru ne umma ?
Umma taja dogon numfashi tace "Uhum ai jidda a
ranar aka kashe Dr. khalifa da Fatima ,yanzu
haaka zancen danake miki fatima na kulle ana
tuhumarta da laifin kashe Dr. khalifa.
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un. Jiddah ke
maimaitawa jikinta na rawa tabugi kirji tace
"Mama an kashe khalifa ?
Ta amsa cikin tausayi.
'"An kashe Khalifa jiddah kuma fatima tana cikin
mummunan zargi don ita da kanta ta amsawa
kotu cewa ita ta kashe shi.
Jiddah ta girgiza kai ta mike tsaye tace "Fatima
ba za ta kase Dr. khalifa ba, ko da ace ba ta son
shi ba ta da dalilin kashe shi akwai wadda na
sani wadda ke da dalilin kashe shi kuma shi ta
kashe shin ni ce zan fasa kwan, nasan waye
yakashe Dr. khalifa.
Alhamdulillahi.
Masu karatu a yi hakuri ayi jimirin biyoni a littafi
na hudu kuma na karshe don jin ya zata kasance,
waye yakashe Dr. Khalifa ?
A DAREN FARKO
36
NI na san wanda yakashe Dr. khalifa da dalilin
dayasa aka kashe dr. khalifa.Jiddah taci gaba da
tayar da maganar wanda yasa mahaifiyar ta ta
cikin tashin hankali, ta zaro idanuwanta gaba
daya cikin kaduwa take kallon jiddah tace "Ke
'yar nan kin san abinda ki ke fada kuwa ?
Na sani Ummah, "kin sani jiddah ?
"Eh na sani mana umma, idan babu rami babu
abunda ke kawo batun rami, wannn maganar da
idan mutum yadauketa ya san abinda yataka,
haka kawai baxai fada ba sai yana da hujjah
hujjar ma mai karfi.
Umma ta jinjina kai har yanzu fuskarta a razane
tace "Jiddah ki yiwa Allah da Annabinsa kada ki
kara furta wannan maganar ballantana wani
yajita kija bakinki ki shiru.
Jiddah tai murmushi tace "Ummah na yi zaton za
kitambayeni inda nasan wannan maganar me cike
da gagarumin sirri ba wai ki dinga rokar kada in
fada ba, yaya lallai in boye wannan maganar ko
kuma kiyi shakkar inda naji ta.
Umma ta girgiza kai tace "Jiddah tsoron hadarin
dake cikin maganar ne ya firgitani yasa narude ni
din ma dakike fadawa tsoro nakeji ballantana idan
magana tafasu kowa yaji, kin san irin wannan
maganar gagurama ce kuma ni banyi shakka don
na ce kina da masaniya akan kisan khalifa ba
sbda bazai yiwu kifadi hakan ba face lallai kin
sani, mamaki na shi ne a ina kika sani ke da ba
ki a kasar, to amma tsoron danaji yasa maganar
mamaki ta kau a zuciyata nake roko ki rufawa
kanki asiri ki rufa mana.
Da zarar kin furta wannan maganar za a shiga
tuhumar mu.
Jiddah tace "Umma yaya za ayi ina ganin gskiya
kiri kiri a rufeta, yanzu sai kisa ido a kashe
Fatima ? Alhali ba ita takashe khalifa ba dole in
bayyana wanda yakashe khalifa yau din nan,
tamike tsaye.
"Umma ki kwantar da hankalinki babu abinda zai
same mu sai alheri insha Allahu, itama umman
mikewa tsaye tayi tace "ta ina zan kwantar da
hankalina jiddah ? ai hankali ya bar kwanciya in
dai kika fasa wannan maganar ni dama na sani
ban fadi miki ba.
Tace "Ummah ko baki gaya min ba zanji ke dai ki
tamin addu'ar neman kariyar Allah ahine me
kowa da komi, tarike hannunta lokacin data yi
hanyar fita tace "jiddah kar dai kijefa kanki ckin
hadari, takatse ta umma bazaki tambaye ni
wanda yakashe dr. khalifa da dalilin kashe shi ba
sai rayuwa ta kike neman karewa to bari kiji,
"Kariya tana gun Allah ban taba tunanin zan dawo
nigeria a wannan lokaci ba haka kawai ina zaune
hankali na naji ya tashi, Allah ya dawo dani ne
don yatoni asirin wadanda sukayi wannan kisan .
Allah ya dawo dani ne don ya kubutar da Fatima
kinga kuwa ba ni da dalilin dazai sa in rufe bakina
don in kare rayuwata, jin an yi kiran sallar
magriba yasa jiddah tafita tana fadin "ina zuwa
ummah.
Hankalin ummah yatashi sosai zuciyarta tashiga
harbawa, kar fa yarinyar nan tajawo mana fitina
ya kamata in sanar da babanta halin da ake ciki,
wannan maganar me hadari wa zai sa kansa a
ciki don wauta ?
Tana cikin wannan tunanin babansu jiddah
yashigo tare da babban yayansu Alhaji Nazifi,
tace "Yawwa Alhaji gara da Allah yaka wo ka
jiddah dai ta dawo mana da fitina tana neman
jefamu ckin zargi.
Yace "me ya faru daga dawowarta ?
Ta bayyana masa duk abubuwan dasuka tattauna
da jiddah, hankalinsa shima yatashi, Nazifi har ya
fi abban na su fusata yace "kin ga yarinya mara
hankali ? wa yagaya mata ana irin wannan ?
Alhaji yce "Dakata, tanada dalilin fadin hakan, ta
gaya miki ?
Umma tace "Yo Alhaji ni da hankali na yatashi ina
na tsaya tmbayarta wanda take nufi ya yi kisan.
Yace "yanzu tana ina ?
Tace "ta fita nasan dai ba za tawuce gdansu dr.
khalifan ba ko gdansu fatima.
Yadubi Nazifi yace "maza nemo mini ita a waya,
zo muje masallaci mudawo, Alhaji Nazifi yayi
kwafa xuciyarsa cike da haushi nomban jiddah
tana dagawa yace "Ke fitinanniya munji maganar
dakika zo da ita sai ki zo kiyi mana bayani. Bai
jira jin abinda za tace ba yakashe wayar.
Suka yi alwala suka nufi masallaci. itama umma
alwalar tayi tai sallah zuciyarta cike da fargaba
sai a yanzu take son jin hujjar da jiddah ta taka
take furta cewa ta san wanda yakashe dr. khalifa.
****
A harabar gdansu ummi, jiddah ke tsaya tana
neman wata waya kiran yayanta yashigo, don
haka tafasa shiga gdan tadawo da baya zuwa
gdansu kafin baban na ta sudawo daga masallaci
itama tayi ta ta sallar.
Kannanta duka suna falon da abokiyar zaman
umanta hajiya zainab da suke cewa Anti, Abba da
Nazifi suka shigo har gara fuskar Abban tana
nunawa zai karbi maganar da fahi ; ta.
Nazifi kuwa gallawa jiddah harara yake kamar ya
shaketa yahuta, ya tsani ana zaune lafiya a tado
da ftina.
Jiddah na zaune gaban abbansu ta lankwashe
kafafu kanta na kasa tana mai bayanin daya
daurewa kowa kai, babu wanda yakatse ta sai da
tayi shiru.
Nazifi yaja tsaki yace "kai jiddah ni duk da haka
inain wannan abubuwan dakika fada bai isa ya
zamo hujja akan wannan gagarumin magana ba,.
Shari'a fa sabanin hankali ce kuma ita an yi mata
lakani da mace mai ciki ba a san abinda za ta
haifa ba, sannan hausawa sunce idan baka iya
kama barawo ba barawo sai ya kamaka, eh
abubuwan da kika fada mana ya isa a dubesu a
yi nazari amma ba zai isa gamsashiyar hujjar da
za a tunkari kotu da ita ba kai tsaye sai an yi
dogon bincike da taka tsan tsan sbda kotu ba
gun wasa bane. wannan maganar saita jefamu a
wahala.
Umma tayi farat tace "yawwa alhaji abinda nake
son ka kalla knan mutum yana ckin zaman sa
lfya bai dace yadauko ma kansa abinda zai zama
fitina gunsa ba, wannan magana ce me sarkakiya.
Jiddah tace "ki kwantar da hankalinki insha
Allahu Allah zai fitar damu ni dai addu'arku nake
nema, ina ji a jikina wani nauyi ne ya hau kaina
wanda ya zamo dole in yi magana a cikin wannan
lamarin idan nazauna inajin tsoro za ayi kwaba.
Gaba daya suka yi shiru kowanne zuciyarsa bata
gamsu da abunda jiddah ke niyyar yi ba a son
ransu abba ya hana amma ga mamakin su sai ga
abban na cewa "Allah ya taimake ki jiddah, Allah
ya tsareki.
Dama kowa ya san fatima ba ita tayi kisan nan
ba fatima ba za takashe khalifa ba.
*****
Daga wanna rana rayuwar Jiddah ta kasance a
boye babu wanda yasan tana kano sai 'yan
gdansu har zuwa ranar da kotu za tazauna don
yanke huku ? cin karshe tunda dai wadda ake
zargi ta amsawa kotu karara cewa ita tayi kisan.
A ranar fatima fuskarta ba tashin hankali sosai
idanuwan ta ba hawaye sai dai jawur dasuka yi.
Yau kotun ta cika makil, 'uyan'uwan fatiman har
wadanda basu taba halartar kotun ba yau sai da
suka zo. Ummi na zaune kusa dasu inna kamar
yadda tasaba kanta na kasa.
Fatima na tsaye kan minbarin amsa kara bayan
mai karanto kara ya karanto.
Kafin kowa yace komi sai akaji barrister abbas ya
tashi ya nemi izinin magana.
Alkalin yace "yana da damar yin hakan, yayi
godiya sannan yashaidawa kotu cewa yau ya zo
da babbar hujjar da zata gamsar da kowa cewa
ba fatima ce tayi wannan kisan ba, aka bashi
izinin yagabatar da hujjarsa.
Wata kofa ce tabude jidda ce tafito, lamarin
dayasa kallo yakoma kanta ana shirin ganin
abinda zai faru, itama fatiman kallon jidda kawai
takeyi cike da mamakin lamarin kamar yadda
fuskar kowa a kotun yanuna ckin wadanda suka
san jidda, kowa ma knan ballantana babbar
aminiyarta ummi.
Barrister abbas ya gabatar wa da kotu jidda da
kuma rokon kotu tabawa jidda daman gabatar da
bayanin datake dauke dashi, ake ce duk za a iya
yin hakan.
Bayan jiddah ta yi sallama tafara da fadin "Ina
gdan da nake zaune birnin london wani yamaci
naji wayata na ringi ? g ina dakkowa naga
nomban babbar aminiya ta ummi, hakan yasa
nadaga dasauri muka gaisa na tambayeta labarin
gida da rayuwa.
Tace "komi lfya jiddah, sai dai ni ina cikin
matsanancin tashin hankli wanda yasa rayuwat
ma gaba daya ta fita daga raina.
Nace "Subhanallahi me ke damunki kike fadin
haka ummi.
Tace "eh to jidda a iya saninki dai kin san tun
tasowa ta ma'ana lkacin da na mallaki hankalin
kaina babu abinda yake barazana da duk wani
farin ciki na rayuwata wanda yawuce dr. khalifa
ko ?
Na amsa mata "eh na sani ummi.
Tace "To dr. khalifa shi ne matsala ta ko kin san
cewa zancen auransa da fatima ya tabbata.
Nace "to kiyi hakuri mana ummi, ni dai na san
duk abinda ke faruwa Allah ne yahukunta hakan
zai faru sai dai kiyi hakuri domin kuwa lamari na
Ubangiji yadda yakaddara haka zai faru, cikar
imanin musulmi yadda da kaddara cikin abinda
yayiwa mutum dadi ko akasin haka.
Ummi taja dogon numfashi tace "Jidda kina nufin
in hakura da dr. khalifa ? duk lokacin dana bata
ina jiran dawowarsa daga grmany ya tashi a
bansa knan.
Nace "Bai tashi a banza ba idan har za kiyi aiki
da shawarar dazan ba ki, abinda nake so kigane
shi ne idan zuciyar mutum tadamu da son wani
abu kuma bai samu ba yadan gana ga Allah yayi
hakuri, yakaddara cewa Allah ne bai kaddara abin
nan da rabonsa bane to Allah zai dubi niyyarsa ya
musanya masa abin nan da wanda yafishi, don a
lokuta da dama mukan so abunda ba alheri bane
garemu, abinda nakeso inkaiki gareshi ummi shi
ne ki kaddara dr. khalifa ba rabonki bane a bisa
abinda Allah ne yakaddara ba wani ba, domin
wani ko wata bai isa ya kwace maka abinda Allah
yakaddara rabonka bane, in dai kin yarda da haka
to saikiyi hakuri na san abinda ciwo amma in kin
daure kin yi hakuri don Allah, zai miki maganin
damuwar ki, ance idan so cuta ne hakuri magani
ne.
Ummi taja dogon numfashi tace "jidda hakika
shawararki itace akan hanya anma wannan
hanyar binta ba zai yiwu ba idan nabita mutuwa
zanyi.
Nace 'Haba ummi ya ya za ace wanda yabi
hanyar gskiya yamutu.
Tace "jiddah ba zan taba iya hakuri da dr. khalifa
ba idan kuwa nace zan hakura dashi to mutuwa
zanyi.
Nace "To ni dai kuma ban san abinda zan ce miki
ba ummi ba ni da abinda zance sai dai kiyi
&akuri.
Tace "Ba zan yi hakur ba jiddah na yarda na rasa
dr. khalifa amma yadda na rasa shi sai dai
kowacce mace tarasa shi, babu macen da za ta
moreshi.
Na ce "ummi me kike nufi da fadin haka ?
Kai tsaye tace "Kashe shi zanyi.
A nan ne jidda tayi shiru.
Yayinda jama'ar kotu suka rude da hayaniya ana
fadin "Lahaula" wasu na salati, sai da aka
tsawatar sannan kowa yai shiru.
Mai shari'a ya dubi jiddah yace "kotu ta ji abinda
kikace, akwai karin bayani ko shi knan hujjar ta
ki ? sannan kuma akwai shaidar da za ki
tabbatarwa da kotu cewa kunyi wannan magana
da wadda kika kira ummi.
Ta gyda kai tace "Ina da kwakwarar hujjah ya
mai shari'a.
Cikin rudani na tambayi ummi "kashe shi za kiyi ?
Tace "Abinda kunnanki yagaya miki shi nake nufi
tare da kara tabbatar miki da hakan kar ki dauka
da wasa nake......
Na katseta nace "ummi an taba irin wannan
maganar da wasa ?
Tace "Yawwa gara da baki wahal da kanki gun
shakkar abinda nafada ba.
Nayi ajiyar zuciya nace "ummi meye dalilin da
yasa za ki furta wannan maganar mai tada
hankali ?
Tayi dariya tace "na gaya miki idan har na rasa
khalifa to sai dai kowa yarasa shi har iyayensa
da kowa nas.
Nace "amma lallai yau ummi na tabbatar ba ki da
hankali kuma ba ki da tunani.
Tace "in dai akan son dr. khalifa ne ba damuwa
duk abinda za ki kirani kinyi dai dai.
Idanuwana a makance suke babu abunda zan
hango illa abunda nasa gaba zan aiwatar wanda
shi nake ganin zai bani mafita, haka kunnuwana a
toshe suke ba zan iya sauraron kowani nasiha ko