Showing 3001 words to 6000 words out of 82249 words
Chapter 2 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf
ciyuwa, muna cikin matsananciyar damuwa ,bansan dawani
ido zan kalli iyayan khalifa ba, bansan da wanne ido zan
cigaba da kallon 'yan uwansa ba damutanan unguwa, ba wani
abu ne ma ba fatima shirun dakikayi har yau baka fad'i Wata
magana wadda za a kama ba akan maganar nan kin mana
adalci, dukkan 'yan uwansa da masoyanki kowa yana cikin
damuwa. "
"Ni na kashe shi baba. "
Akayi tsit kowa yazuba mata ido, maijidda kallonta kawai take
ta yi tagumi d'ansu da suke mutuwar so khalifa ta sake
rushewa da kuka,
Goggo Abu tace "shikenan tunda kince ke kika kashe shi to
lallai ne kidaina wahalar da mutane idan anje kotu kifad'i dalilin
dayasa kika kashe shi, kin san ba wai kice ke kika kashe shi
kiyi shiru ba dole ne kifad'i abinda yasa kika kashe shi.
Ummi tari'ke hannun goggo tazaunar da ita tace "goggo me
mye amfaninki yi hushi da fati alhalin kowa anan ya san takura
matan da akayi da maganar nan yasa tace Ita takashe shin to
haka idan ma akaje kotun aka takura Mata abin da za tace
knan 'karshe idan tace ita takashe shin dole tayi shiru tunda ba
ta da dalilin dazata fad'a wanda yasa takashe shi. "
Goggo tace "shikenan ummi haka za muyi tazama cikin
damuwa tunda ba ita takashe shi ba idan anje kotu ta fad'i Iya
abinda tasani mana. "
Fatima tana kuka tace "kiyi ha'kuri goggi ba'kin cikin damuwar
danasa ku ya fi damuna fiye dakowa sai dai ba yadda zanyi,
goggo ba zan iya cewa ba ni nakashe Dr. khalifa ba sbda gaba
d'aya bayanan sun tabbatar dacewa ni nakashe shi."
Kuyi ha'kuri shirun danayi a kotu wannan shi ne abin da yafi
damuwa na, idan nace zanyi magana bansan abinda zan fad'a
ba 'karshe dai na san duk abinda shirun na wa zai haifar bai
wuce a yanke min hukuncin wanda yayi kisan kai bane a kashe
ni.
To dama abinda nake jira knan, ni kam rayuwa ta 'kare a guna
sai dai sai dai jiran lokaci ko ba'a kasheni ba ba'kin cikin
halinda iyayena kuka shiga a sanadiya ta da ba'kin cikin rashin
mijina shi zaisa zuciyata tabuga in mutu ba zan iya cigaba da
rayuwa ba shi yasa ba na bu'katar taimako tako wani fuskar
lauya don ku'butarwa idan akwai abinda nafi bu'kata bai wuce
addu'a ba, wannan ba sai na ro'keku ba na san kuna yi min.
Dan Allah kuyi ha'kuri kuyafe min babu abinda zan iya cewa a
kotu.
Aliyu yayan fati yayi mgana a karon farko tun zamansu a
d"akin yace "fatima bamu amince kici gaba dayin shiru a kotu
ba dole kiyi magana. "
Tace "shi knan yaya zanyi magana.
Alhaji muhammadu dakowa yafi sani da, abba yace "kar kice ke
kika kashe shi fati".
Tace "Abba idan nace ba ni nakashe shi ba waye? idan kuma
akayi bincike aka gane ni d'in ce abinda ake gudu shi zai faru,
kuna fad'in hakane don fa kusamar min mafita wadda za ta ba
ni damar ci gaba da rayuwa a duniya, yayin da ni kuma ba na
son rayuwar ta fita daga raina so nake na mutu na bar duniya
yadda mijina yabarta. "
Aliyu yace "Anya fati baki samu ta'bin hankali ba? "
Tace "lafiya 'kalau nake yaya ".kowa yarasa abin fad'i a kayi
shiru.
*********************************************
*********
Da sassafiyar ranar daxa a koma kotu hajiya maijiddah da
akafi sani da mama tana kwance kan faffad'an gadonta na
alfarma tunani da ba'kin cikin duniya ya isheta tarasa abin dake
mata dad'i, tana mutuwar son D'anta an kashe mata shi wata
'kanwarta dake tayata zama wato anty sadiya tashigo d'auke
da abincin karin kumallo tazauna kusa da ita suka gaisa tace
"kidaure ki sha ko da ruwan sanyi ne zama da yunwa ya fi
komi illa duk abinda yafaru rubuttaccen alamari ne babu
wanda ya isa yago ge shi. "
Tami'ke zaune tazubawa anty sadiya ido tace "anty sadiya kina
ganin haka yadace mu zubawa lamarn nan ido kullum Alhaji
yana cewa fatima ba za ta kashe khalifa ba toh ni so nake
agaya min wa yakashe min d'ana?
Anty sadkya tace "tabbas kam fatima ba za ta iya aikata
wannan mugun aiki ba abinda yake da sar'ka'kiya shi ne daga
shi sai ita a d'akin to waye yashiga yakashe shi?
Mama tace "ke sadiya idan ma ba ita takashe shi da hannunta
ba to da had'in bakinta aka kashe shi sbda ana ganin ubansa
yana da dukiya d'ansa d'aya ne ko don a mallake dukiyar
ubansa za ta iya yimasa haka.
Anti sadiya tace "kigafarce ni amma ban tari numfashinki ba to
amma idan haka ne da had'in bakin fatima ya ya za ayi ita data
kasheshi ko ta had'a baki aka kasheshi bata gudu ba har akazo
aka kamata? Allah (SWT) dasu kuma mahukuntan tunda Allah
yabasu basiran gano gaskiyar wannan alamari cikin hikima da
izinin Allah za su gano mana wanda yakashe mana d'a jininsa
ba zai tafi a banza ba.
A bisa hanyarsu tazuwa kotunne cikin mota mitar da mama ke
tayi wa abba kenan yayi tsit yana jinta ko tari vaiyi ba ya yi
tagumi yana jan charbi.
Suna shiga su malam da goggo suka shigo suka gaisa, Abba
yace"malam bana jin dad'i Yadda kake kaucewa had'uwa dani
tunda wannan abu yafaru. "
malam yarufe fuskarsa da babbar riga dan kar abba yaga
fuskarsa yace "haba alhaji me, zan ce dakai? menake dashi
wanda zan gaya maka dahar zaisa intsaya in kalleka, kaico.
Ina ba'kin ckin faruwar wannan alamari har ina cewa ina ma
ace banzo duniya ba da dai ace 'yar cikina ta kashe d'an
mutumin kirki kamar kai d'in nan Alhaji muhammadu.
Abba yaja hannunsa suka wuce cikin kotu ba tare dayace komi
ba, wuri d'aya suka zauna mutane suna mamaki sosai yadda
suke ganin iyayan wanda aka kashe da iyayan wacce ake
zargin ta yi kisan. wannan abu yana matu'kar baiwa mutane
mamaki haka zakaga jama'a na kallonsu, yai d'in ne ma dai
hajiya maijidda tasauya fuska sama sama suka gaisa ba wani
magana dasukayi fuska tamau ko da aka shigo da fatima ma
ko kallon inda take batayi ba.
ummi kamar ta fi su kansu fati shiga tashin hankali ta rame ta
lalace
.
Fati na shigowa kotu da ummi suka fara ido sannan tadubi
iyayanta dasauri tad'auke idonta xuwa 'kasa tashin hnkali
datake ganin iyayanta a ciki ko wannan ma ya ishi mutum
tashin hnkli da ba'kin ciki ina amfanin rayuwarta.
Yau kam duk abinda zai faru sai dai yafaru lallai sai ta kawo
'karshen wannan zaman kotu.
Bayan da akayi abubuwan daya dace ayi aka zauna mai
karanta 'kara yakaranto, tuhumar da akewa fati na ta kashe
mijinta a ranar da aka d'aura musu aure a daren farko.
Mai shari'a Usman Muhammad Bamaina yace "fatima musa
kinji tuhumar da ake miki a karo na biyu? "
Ta gyad'a kai tace na ji ya mai shari'a, yau kowa na jin
muryarta sosai, kuma kowa ya ji dad'in yadda tayi mgana har
alamun natsuwa a fuskar iyayanta da 'yan uwanta musamman
ummi wadda har tsima jikinta yake a ranta tana fad'in yawea
fati gara ki yiwa kanki adalci da iyayanki damu masoyanki.Mai
shari'a yace "fatima musa me za ki iya Fad'awa kotu akan
haka? ma'ana kin amince ke kika kashe mijinki Dr. khalifa.?
Kai tsaye fati taware muryarta tace "Eh ni na kashe shi ya mai
shari'a.
[5:07PM, 7/13/2017] +234 706 196 7803: A DAREN FARKO
3
Gabad'aya kotu tarud'e da sallalami kowa na fad'in albarkacin
bakinsa ,iyayan fati dasu kansu surukan suka rud'e, ummi kuwa
hannu tad'ora aka tana fad'in "wayyo Allah na wayyo fati
meyasa kikace ke kika kashe Dr. khalifa bayan ba ke kika kashe
shi ba.
Mai shari'a yayi tsawa akayi tsit sai dai kukan 'yan uwan fati da
ba ya 'karewa, ita kuwa fatin yau tana tsaye 'kyam ko gezau
gadukkan alamu zuciyarta ta fara soyewa, idanuwan amma ba
kuka take ba zafin zuciya ne, ba ta son takalli iyayanta taga
mummunan tashin hnkalin dasu ke ciki, dama chan ita mutum
ce mai tsananin tausayin mutane balletana iyayenta.
Mai shari'a yace "fatima kotu tanason kiyi mata bayanin dalilin
dayasa kika kashe mijinki a daren tarewarku.
Fati tace "ban san dalilindayasa kika kashe mijinki a daran
tarewarku".
Fati tace "bansa n dalilin dayasa nakashe shi ba, ba abinda
nao na zai iya furtawa a kan haka ya mai shari'a ina ro'kon
wannan kotu mai alfarma Data taimaka min tayanke min
hukuncin kisa a yau in bar duniyar nan inhuta, ba na son
bugawar da zuciyata keyi yazamo sanadin mutuwata na fi son
a yanke min hukunci dai dai da laifi na.
Tanumfasa tana kallon al'kalin daga bisani tad'auke idanunta
daga kansa zuwa kan jama'ar dake kotun, gaba d'ayansu su
ma ita suke kallo kowanne da abinda zuciyarsa ke sa'kamasa
game da ita.
Tayi shashe'kar ajiyar zuciya tace "iyayena da 'yan uwana da
dukkan masoya na ina ro'konku don girman Allah kuyafe min
wannan yanayi dana sa ku nadamuwa sannan kuyi min addu'a
rayuwa ta fita daga raina minti d'aya ba na son in 'ka ra yi a
duniya na fi son inbi mijina. "
Tayi shiru kamar yadda kotun ma tayi tsit kai ka ce ba kowa a
kotun, al'kali yana 'yan rubuce rubucensa, haka a 'bangaran
lauyoyi wasu suna rubutu wasu shiru kawai sukayi suna kallon
fatima.
Taci gaba da fad'in "ya mai shari'a a karo na biyu ina ro'on a
taimaka a yanke min hukunci daidai da laifina na amsa laifina
ni ce nakashe mijina".
Wani daga cikin lauyoyi yami'ke yanemi izinin magana daga
gun mai shari'a yace kanada daman magana.
Yayi godiya yadubi fatima yace "sunana barrister Abbas
Mukhtar inason kare wadda ake 'kara sbda na fahimci ba ita tai
kisan ba ina nufin fatima musa ba ita takashe mijinta Dr.
khalifa ba ina ro'on wannan kotu
mai adalci data ba ni damar yin cikakken bincike a kan
wannan al'amari, kuma inason a ba ni damar dazan yiwa
fatima tambayoyi akan abinda ake tuhumarta dashi. "
Mai shari'a yace "kanada damar yin haka.
Yayi dariya yana d'an murmushi ya'kara maida fuskarsa ga
fatima wadda itama shi take kallo fuskarta a tsuke, yace
"malama fatima musa 'karfe nawa aka kaiki gidan mijin kuma
a wace rana ce. "
Fatima tayi shiru kamar ba da ita ake magana ba, Barrister
Abbas ya'kara maimaita tambayar tare da ro'kon kotu data
tursasa fati tayi magana".
Mai shari'a yayi hakan amma Fatima cewa tayi "nagode da
kake burin taimakona a bisa halin danake ciki, sai dai inason
kayi ha'kuri gaskiyar magana ba zan iya ba ka amsa ko d'aya
ba a bisa tambayar dakake min sbda ba so nake in ku'buta
daga halin danake ciki ba, wanda yake bu'katar lauya shi
yakeson yatsira nagaya muku ba na bu'katar rayuwa dan Allah
kuyafe ni.
Mai shari'a Usman muhammad Bamaina yadubi wani dogon
d'an sanda dake tsaye gefe yace "Za a gwada 'kwa'kwalwar
fatima don mu tabbatar da mai hankali muke shari'a, idan
munyi zama na gaba za mu ji sakamakon sannan mud'ora a
inda muka tsaya.
Daganan aka d'aga 'karar zuwa mako biyu idan Allah yanuna
mana,amma kotun ta ba wa 'bangaran lauyoyi guda biyu damar
suyi duk binciken su akan yadda al'amarin yakasance don ba
da kariya dawadda ake zargi.
Yau ma kamar wancan karon kotun ta tashi da hayaniya kowa
na fad'in albarkacin bakinsa akan kafiyar da fati tayi a shari'ar
mamakin da take bawa yawancin mutane shi ne tayaya za ayi
mutum yace shi ya fidda rai kwata kwata da rayuwa mutuwa
yake muradi, wasu suna ganin wannan ya isa kowa ma ya
amince ba ita tayi kisan ba, yayin dawasu ke ganin dan ace ba
ita bace shi yasa tasallama tami'ka wuya, idan ba ita bace
waye? Gida su biyu kachal ba kowa d'aki a kulle su biyu in har
ance ba fati takashe Dr. khalifa ba to sai dai ace shi yakashe
kansa, hatta hajiya Maijidda mahaifiyar marigayin dayawa
daga 'yan uwansu abinda suke gani knan wannan kukan da
take abinda suka d'auke shi kukan munafinci ne kawai.
A harabar kotun kafin sutafi gaida malam musa ya tsaida
barrister Abbas yana masa godiya a bisa 'ko'karinsa nakare
'yarsa, barrister yayi murmushi yace, "Ba komai kada kadamu
baba na yi wannan ne domin Allah da tsananin tausayin da
fatima ke ba ni tun randa aka fara tsaida ita a gaban shari'a na
tabbatar ba Ita tayi wannan kisan ba, duk wanda yakashe Dr.
khalifa na gida ne wanda yasan sirrin gidan insha Allahu da
izinin Allah zamu gano ko waye,sai dai inason kataimaka min
fatima tadinga ba da amsa a kotu sannan xanje inganta
kutaima ka min tayimin cikakken bayani duka tambayoyin da
zan mata dan insan yadda zan 'bullowa al'amarin.
Malam yace "To ni na rasa me yasa fati take tsuke bakinta
komi sai tace ba za ta iya fad'a ba sbda rayuwar ta fita Daga
ranta.
Barrister yayi murmushi yace "bako mi tsananin damuwa ne
yasa take fad'in haka, matsayinku na iyayenta ku yadace
kulalla'bata tafad'i yadda akayi.
Malam yayi masa godiya mai yawa bayan tafiyarsu malam d'in
barrister na xaune a motarsa shi kad'ai yana nazarin alamuran
fatima tausayin ta har ya yi masa yawa a zuci.,daurewa kawai
yau yayi ya zo kotun tun a wancan zaman da akayi hankalinsa
yatashi sosai gameda al'amarin yarinyar, tun lkcn abinda yake
d'aga masa hnkali matsalar d'aya matsalar kowama ita ce
shirun da fati tayi tana neman mutuwa ido rufe ta 'ki ba da
had'in kai ballantana a samu mafita.
*********************************************
A hankali ummi tafito daga motar tabi bayan mama zuwa cikin
gida, kowanne zuciya ba dad'i , a falo suka zauna gaba d'aya
yayin da ita ta dawo dabaya zuwa ainihin d'akin Dr. khalifa na
gidan har yanzu mukullan d'akin yana hannunta ita kad'ai take
bud'ewa tashiga tunda ga lokacin daya mutu zuwa yanzu,
komi na nan yadda yake wani irin 'kamshi mai dad'in gaske
yana tashi a d'akin, gaba d'aya kayansa nasawa suna jere a
cikin wardrobe gwanin ban sha'awa manyan hotunansa da
akayi enlargement d'insu guda biyu na gefe da gefe na gadon
ya yi kyau ba na wasa ba.
Tazauna a gefen gadon tanasa hannu tad'auki hoton
tarungume kam kam idanunta a rufe hawaye wasu na bin wasu
zuwa chan ta ajiye tashiga bud'e durowowin jikin madubin
hotunan bikinsa da fatima ne birjik musamman ma gun
lunching da dinner dayawa yarungume fatin ne 'kam 'kam a
'kirjinsa wasu kuma tare da abokanansa maza da mata.
Kan cinyar ummi yaji'ke dahawaye kamar ruwa aka zuba mta a
cinya tun ranar da aka kashe Dr. khalifa take kuka amma bata
ta'ba kuka irin na wannan rana ba, har sai dataji numfashinta
kamar zai d'auke.
Ba za ta ta'ba mantawa da abinda yagya mata ba a yammacin
lahadin daza akai fatima gdansa wanda kuma a wannan rana
ce aka kashe shi bai sake kwana a gidan duniya ba.
Yana tsaye a harabar gdansu tare da manyan abokansa biyu
wad'ana baida aminai kamar su.
Manyan likitoci Dr. Hafiz Bala Muhammad da Dr. Mustapha
Abubakar kura, yana tsakiyarsu suna hira, sai ita ummi tafito
daga cikin gida tana ganinsu tahau yimusu hoto a wayarta, Dr
khalifa yaharareta yace "wai meyasa kike daraina mutane ne
ummi ni kikewa hoto?
Sai Dr. Mustapha yace "kaima kanada saurin hushi khalifa ko
wacce rana idan an maka abu za ka 'bata rai banda wannan
rana wadda tazamo ta auranka da matar dataza mo allura
cikin ruwa kaine kaxamo mai rabon daka zu'kota. "
Dr. khalifa yarausayar dakai yana murmushi tare da lumshe ido
yace "ka fad'i gskiya Dr. Mustapha tabbas ni ne na cafko
wannan allurar data zamo tamai rabo ce, a daidai lokacin dana
fidda rai da ita sai najita kawai a hannuna ,tabbas wannan rana
ta dace tazamo ta farin cikina, ranar dazan sadaukar da komi
na wa sbda Fatima. "
Ummi tay murmushi tace "shiyasa nima nake maka hoto
domin ka yi min kyawun daban ta'ba ganin ka yi shi ba a
duniya dukda cewa kai d'in me kyau ne kullum kyau kake da
ado. "
Dr. Hafiz Bala yace "har bayan hoto yanada kyau ma yayi miki
kyauta ta musamman ummi."
Dr. khalifa yayi murmushi yace "ko shakka babu a wannan rana
ina cikin farin cikin daban ta'ba samun kaina a cikin shi ba, sai
dai kasan tun safiya gabana ke fad'uwa bansan dalili ba
wannan yayi sanadin dayasa tun ruwan shayi danasha rabin
cup d'azun bayan d'aurin aure ban iyacin komi a bakina ba.
Ummi tayi wal da ido tace "fad'uwar gaba kuma Dr. a irin
wannan rana? ni dai na san ko kusa bakayi kama da wanda
mace za ta ba wa tsoro ba ballantana ince firgita kayi sbda
fatima.
Dr. Mustapha ya bugi kafad'arsa yace "wa wannan? ni tunda
ake ma gwargwadon bud'ewar idanuna ban ta'ba ganin
namijinda yayiwaa mata farin sani irinsa ba, farin ciki ne yayi
masa yawa sbda soyayyarshi yasa ma gabansa yake
fad'uwa....... "
Tunanin ummi yakatse a nan lokacin da mama taturo 'kofar
d'akin tatsaya tana kallon ummi kukan datake yabata tsoro
ta'karaso dasauri ta kamata takwashe hotunan dasuka ji'ke da
hawaye ta mayar, takamo hannunta tafito da ita tarufo d'akin
takar'be makullin tace "daga yau ko 'kofar d'akin nan ba na so
kisake zuwa, haka kada ki 'kara zuwa kotu ba xa muyi biyu
babu ba, mun rasa Dr.khalifa muna cikin ba'kin ciki mai tsanani
kema damuwa na neman xama ajalinki to B xai yiwu ba.
Cikin kuka ummi tace "Don Allah mama kada kiharamta mini
shiga d'akin likita, yin hakan ne kad'ai zaisa zuciyata ta
sassauta daga damuwar danake ciki, na rasa d'an uwana ga
aminiyata na cikin matsancin zargi na bi duk hanyoyin daya
kamata inbi don ganin fatima ta ba lauyoyi had'in kai ta 'ki
burinta akasheta meyasa ba zanyi kuka ba mama?
mama tayi tsaki tace "ina mamakin yadda ke Da Alhaji kuka
d'auki damuwar duniya kuka d'orawa kanku akan fatima shin
dakuke cewa batace komi ba me za tace, fatima ba ta da abin
cewal shiyasa tai shiru, ko a hankalce