Showing 15001 words to 18000 words out of 82249 words
Chapter 6 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf
kan tsiya wanda ko
kallo mutane basi ishe shi ba.
Hajiya sauda tace "wai waye ne ?duk kin rikitani.
Hajiya hauwa taja dogon numfashi cikin takaici
tace "waye in banda khalifa.
Hajiya sauda tace "to sai me dan ummi ta ce duk
duniya babu wanda takeso sai khalifa, kada kibani
kunya mana yaya hauwa kamar ba ke ba ko in ce
kamar ba mu ba?
Hajiya hauwa tace "uhm saude dole hankalina
yatashi kina kallo fa yadda rayuwar yaron nan
yake, ko kallo mutane basu ishe shi ba, gaisuwa
da yake mana ma dan ya zama dole ne a gareshi,
in banda haka khalifa bamu isa yagaidamu ba ni
kam ba khalifa da uwarsa na tsanesu ba zan taba
kaunarsu ba shiyasa da ummi tabudi baki tace
min ba ta da gwani wanda yawuce khalifa hankali
na yayi mugun tashi nayi gaggawar kiranki a
waya dan musan abin yi.
Hajiya sauda tayi murmushi tace "Allah sarki yaya
hauwa ni ko da kika gaya min maganar nan sai
naji zuciyata ta yi 'kal 'kal, na jima banji maganar
data faranta min rai irin wannan ba.
Hajiya hauwa tayi tsaki tace "ke da Allah ana ga
yaki ke kina ga kura me za muyi khalifa, yarinyarn
nan ummi duk dan abinda na samu a gun kayan
kwalliya suke tafiya don dai musamu gallelen
alhajin birni mu darje amma ta lalace kan khalifa,
wannan sangartaccen yaron da bai san yafita
neman na sa ba sai dai dukiyar ubansa dasuks
jiku a ciki shi da uwarsa.
Hajiya hauwa tace, "to sai me idan khalifa bai
nnemi na sa ba sai na ubansa? dama me muke
nema ne? burin mu dama aibai wuce musamu
wani ba ko d'an wani, to bamu samu wanda yake
wanin ba ai a karan kansa sai dan wani to
dawani da d'an wani in dai za mu shaki dukiya ai
mu burinmu ya cika.
Hajiya saude tayi ajiyar zuciya tace "to in banda
abinki saude taya za mu iya mallakar wannan
yaron mai masifar girman kan tsiya, zancan
danake miki fa a satin dazai kama idan Allah ya
kaimu zai tafi germany karatu sai ya yi shekaru
hudu zai dawo, na ji uban abban hajiya yana
gayawa jummai wai so yake yazama cikakken
likitan mata, don haka karatu yakeso yayi a
germany mai zurfi. wlh saude idan kinji kudin da
muhammadu yakashe akan wannan tafiyar na
khalifa sai kin rike baki sai hankalina ya kasa
karba inda zai zauna ma tsawon wannan
shekarun hudun da aka zuba akan su ya ishe irin
mu mumore mun gama arziki a duniya dai.
Wai amma jummai maimakon tai mashi fada
yarage kashe kudi haka akan khalifa sai fadi take
ya yi daidsi.
Hajiya saude tayi murmushi tace "to ko anan za
kisan lallai auran ummi da khalifa shi zaisa mu
mallake dukiyar alhaji muhammadu cikin sauki
kinsan ana cewa daka haifa gwamna gwara
kahaifi matar gwamna saita kawo maka gwamna
har gida sai ka shekara kana yawan neman ganin
gwamna ma baka ganshi ba amma idan kabi
takan matarsa lokaci guda sai kaganshi ba tare
da ka samu matsala ba sbda ita mace mace ce
daban take, yanzu idan muka bi duk hanyar data
dace gun cusa ummi a zuciyar khalifa shikenan
mun mallaki khalifa, idan muka mallaki khalifa sai
yadda mukayi dashi ko uwarsa bata isa tayi
yadda takeso ba sai mu din dai.
Da ba a so muci arzikin slhaji muhammadu kinga
munci dan bakin ciki sai dai yamutu.
Kuma anan ne za mu fanshe haushin da mukeji
na hajiya maijidda uwar khalifa, tana ji tana gani
za mu aurawa khalifa ummi za mu mallake shi
'kaf shi da dukiyar uban na sa tunda dama alhaji
muhammad ba shi da tunani sai khalifa, idan
ummi ta auri khalifa shi kuma zai kasance ba shi
da tunani sai na ummi sai yadda mukayi dashi da
dukiyar ta shi, hajiya maijidda tazama yar kallo
yadda tamaida mu yan kallo mu da dukiyar dan
uwanmu ba mu da iko akanta muna gefe sai
abinda aka sammana me zai hana muyi farin ciki
akan soyaygar da ummi ke wa khalifa, wannan
itace hanya daya tilo da burinmu zai cika kuma
za mu nunawa maijidda ita ba komi bace hancin
gauta ce bata isa komi a miya ba.
Hajiya hauwa tace "tabdijam amma fa kinyi tunani
saude shi yasa ake cewa mai shawara ba ya
aikin banza, tabbas gaskiya kika fada sai dai
abinda nake jinjinawa shi ne tayaya za mu
mallaki khalifa kidinga tuna masifar jin kansa fa.
Hajiya saude tace "kash yaya hauwa ni kunya
nakeji kamarki wannan maganar kalaman nuna
karaya da gazawa suna fitowa daga bakinki,
khalifan banza khalifan wofi har meye shi, wa
yayi ma ballantana yafi wani ko za murasa zanin
daurawa sai mun mallaki khalifa, sai mun shiga
ko ina zamu shiga dan mu tura ummi gdan
khalifa, matakin farko dazamu fara dauka shi ne
ummi za takoma gdansu khalifa dazama, hikimar
yin hakan shi ne a matsayinta tamace wadda
takai mace muka dade muna koyar da ita kissa
da kisisinar jan hankalin namiji tabi hanyar duk
data dace tafara kafa gwamnatin ta a zuciyar
khalifa kafin tafiyarsa germany a wadannan
gajerun kwanakin 'kididdigaggu, ko yaya ne mu
tabbatr khalifa ya bar kasar nan ne da tunanin
ummi ba wai soyayyarta ba.
Kafa soyayya a zuciyar wanda kwata kwata
hankalinka ba ya kansa abu ne mai wahala sai a
hankali, lamari ne da ba ayi masa gaggawa a
cikin lamari irin wannan to ko shakka babu ba zai
ci nasara ba, ana kaddara cewa mutanen dasuke
cin nasarar abubuwan dasuka sa gaba na rayuwa
su ne masu hakuri a dukkan lamarinsu.
Sbda ita nasara kafad'a da kafad'a suke tafiya da
hakuri, ballantana lamari irin wannan ba abu bane
mai wahala amma fa ga mace datasan abinda
take wadda takaranci halayyar d'a namiji, kada ki
jinjinawa ummi jin kan khalifa har jikinta yayi
sanyi, ki kashe mata guiwar taji cewa ba za ta
iya ba ,ko da tanajin cewa ita d'iya mace ce da
za ta iya jan hankalin d'a namiji ko waye shi,
idan kika jinjina al'amarin itama girmama zaiyi a
zuciyarta daga nan sai ta kasa yin komi sai
asarar tashafe mu baki d'aya.
Amma idan kika nuna mata ba kowane khalifa
face namiji kamar kowa shikenan saita ka ra
samun kwarin guiwar kokarin janyo hankalinsa
har muyi nasara.
Yadda za ayi takoma gdansu khalifa da zama
kuwa wannan sai idan Allah ya kaimu wayewar
gari gobe lfya idan nazo sai musan abin yi.
***************
Ba kowa a gidan sai fatima ita kadai, sauran
kannanta suna makaranta yayin da goggonsu Abu
tatafi barkan haihuwa da akyi musu, ta karasa
tankadan garin tuwon datake takai kitchen
tashare gidan tadora ruwan tuwon sannan
takoma kan tabarma tadauki wani littafi na
addu'a tana dubawa maisuna Du'a'ul mustajaba.
Zuwa can ta ajiye ta kwantar danta kan pillow
tana tunanin auran da za ayi mata da malam
musbahu nan da lokaci kadan har yanzu dai
malam bai yanke lokacin da za ayi bikin ba haka
zalika musbahu bai taba kiranta da sunan zancan
ba, kunyarta yakeji kamar yadda ita matake
bala'in jin kunyarsa, kafin malam yafurta cewa
zai hada su aure, malam musbahu ba wanda yafi
shiri da shi a yaran gdan sai ita, tun tana karama
musbahu ya fi kaunarta fiye da kowani d'a a
gidan nan duk abinda yasamu kafin yaba kowa
sai ya ba ta har sai da mutane suka shiga zargin
ko dai son ta yakeyi, ganin bai furta ba yasa aka
watsar haka itama take bala'in kaunarsa tun
lokacin da bata sani ma musbahu ba dan gdansu
baneballantana data mallaki hankalin kanta
tagane musbahu maraya ne yahadu da zaluncin
matar kawunsa har malam ya amshi ragamar
rigimar rikonsa, sai tausayinsa yasa take ka ra
kaunarsa suka rike shi tamkar dan gdansu, in
banda wannan lokaci da malam yake gayan mata,
da ya gayawa mutanensa cewa zai ba wa malam
musbahu auran diyarsa fatima sannan dayawa
wasu suka san ba malam bane yahaifi musbahu
ba sbda yadda malam din da ita goggo Abu din
da yayansu ke matukar ji da musbahu shi ma
haka yazamo dan halak agaresu ya sadaukar da
rayuwarsa gaba daya gun soyayya a garesu,
kyautata musu tamkar su suka haife shi, koda
yake ako da yaushe yana gayawa malam cewa
bai taba kaunarsa a matsayin iyayan riko ba
kullum a matsayin mahifa yake daukarsu wanda
ba shi da kamarsu a duk fadin duniyar nan kamr
yadda yake da tabbacin suma haka suka dauke
shi, rayuwa suke a gdan mai dadin gaske ga shi
dai ba su da abin duniya sai rufin asirin Allah,
abinda yakesa suke jin dadin rayuwa shi ne
girmama junansu da kaunar juna da ake sbda
Allah da tarbiyyar data ratsa duk d'an dayake na
gidan ne, nisan da fatima tayi cikin tunani yasa
har ruwan data d'ora bisa wuta ydinga tafsa
tamanta dashi sannan mutum na tsaye a kanta
bataji takunsa a lokacin daya shigo ba ballantana
sallamar da yayi mata saida yatsuguna gabanta
yace "fatima wani irin tunani kike haka kina
yarinya karama mai kankantar shkaru haka ina ke
ina wannan tunani?
Kafin yagama rufe baki fatima tatashi dagudu
jikinta na rawa za ta shige daki, musbahu ya
mike shima yana murmushi yatare kofar dazata
shiga yana murmushi yace "fati haka za mu
zauna koda yaushe kina guduna kamar dodo
tunda malam yace ya ba ni ke ban kara magana
dake ba ko gaida ni ba kya zuwa kiyi ina dalili.
kan fatima na kasa kamar za ta nutse a gun sbda
kunya, tarufe fuskarta da tafukan hannayenta
yace "je ki kigama tuwon kuma kada ki kona
mana tuwo amma fa lallai yau ke za ki kawo
mana tuwo ni da abokina mansur, idan har bazaki
kawo mana da kanki ba ba na cin tuwon, idan
kinyi kada ki aiko dashi zan kwana da yunwa, bai
saurari abinda za tace ba yafice yabarta tsaye
kamar an zare mata jijiyoyin jikinta tana kallon
yadda ruwa ke tafarfasa akan wuta amma ta
kasa tashi tayi talge, hankalin fati ya tashi kwarai
da gaske idanunta suka cika da kwalla har ji tayi
kirjinta ya yi mata nauyi numfashinta yana sama
sama kamar zai dauke .
Tun tasowar fatima babu wani d'a namiji daya
taba cewa yana sonta ta amsa mai ballantana
maganar soyayya ta had'a ta dashi shekarunta
goma sha shida da haihuwa ajinta hudu a
secondary, tun tana shekara sha biyar ake cewa
ana sonta kasancewar ita yarinya ce da Allah
yahorewa kyau ba na misali ba abin sai wanda
yagani sannan tana da shiga rai yadda kasan
wadda aka tsuma ta da maganin farin jini, in dai
namiji zai ga fatima sai ya yi shaawar ace
matarsa ce.
sbda bayan kyaun ga natsuwa ko magana fati
take ka san ta samu tarbiyya irin wanda duk d'a
namijin arziki yake burin mallka a matsayin matar
aure.
Shigowar goggon ta Abu yasa tatashi dagudu
tawuce 'yar rumfar kwanon dake gaba kitchen
dinsu inda suke hura wuta, goggo tarike baki
fatima yau me ya sameki sai yanzu ake talgen
tuwo? kina sane dacewa ba na son ayi tuwon
dare a gidan nan, fati bata saba karya ba don
haka tai saurin kallon idanunta kadai, goggo dai
ta san akwai abinda ke damunta yau abinka ga
babba ballantana wanda yahaifeka, ta jima tana
nazarin fuskar fatima sannan ta gyada kai tawuce
daki.
Har fati tagama tuwo a sanyaye jikinta yake ko
magana akai mata dakyar take amsawa hatta shi
kansa bakinta ya yi mata nauyi, bayan sun idar
da sallar isha tana zaune kusa da goggo sanye
da hijjabinta da charbi a hannun ta tana ja
hawaye sai neman xubo mata sukeyi tana maida
su dan kar goggon ta gane tayi mata tambayar
da za ta gagara amsawa amma ina dole tatashi
daga gun tashiga dakin dasuke kwana da
kannanta tazauna tana sharar kwalla, har goggo
tashigo tazauna kusa da ita cikin saryin murya da
tausayawa irin na d'a da mahaifi tace "fatima na
san duk abinda zai dameki bai wuce maganar
auranki da musbahu ba, fati kada kicutar da
kanki idan ba kya son musbahu kina sane malam
bazai matsamiki ba, shi ma tunda farko abinda
yasa yace ya ba shi ke kai tsaye dan ya san
dakake har musbahu babu wanda ba zai yi masa
biyayya ba.
Sannan ya yi la'akari dacewa ke da musvahu
akwai kaunar juna mai karfi a tsakaninku tun
kafinn ku mallaki hankalin kanku kusan ku waye
ku a rayuwa.
Fatima tace 'goggo inason yaya musbahu sbda
ba shi da makusa da mace za ta ki shi hasalima
banga abinda baba na zai bakata in ki yi masa
ba, inji ina kinsa a matsayinku na iyaye na,
biyayyarku a gareni wajibi ce, wannan damuwar
tawa ba ta da nasaba na kin yaya musbahu sai
dai ni kaina bansa abinda yashiga xuciyata ya
tsunduma ni a bakuntar rayuwa a yau din nan .
Goggo tayi murmushi tace "ai baki shiga bakuwar
rayuwa ba fatima sai randa kika shiga gdan aure
kika zamo matar aure lokacin ne za kishiga cikin
bakuwar rayuwa wadda baki santa ba amma da
sannu saiki zama 'yar gari har wata rana kigaya
wa wasu yadda aka gaya miki, kowacce mace sai
da tashiga irin wannan bakuwar rayuwar.
Tashi maza ki kaiwa musbahu abinci daga yau
haka za kidinga yi.
Bayan goggon ma cigaba tayi da zama ta kasa
tashi har sai da goggon taleko takara yimata
magana sannan tafita tadauki abincin tanufi dakin
musbahu dake zaure, ta yi sa'a ba kowa a dakin
ta ajiye dasauri za tafita sai ga shi yafito daga
toilet yace "to dawo kidana murna dodon na ki
yananan, har wani rawar jiki kike za kigudu ko?
Tayi murmushi tatsuguna daf da gado tarufe
fuskarta da hijabi, yazauna akan kujera yace
"fatima ki rufe fuskarki yadda kikeso sbda kina da
abin rufewar, mace kyakyawa irinki ta isa tayi irin
kowacci yanga ga kowane d'a namiji ko waye shi
ballantana almajiri kamar ni.
Fatima tun lokacin da baba yabudi baki yakira
sunana har sau uku hankalina a tashe nadinga
amsa masa sbda bansan wace magana zai
gayamin ba wadda har tasa yayi min irin wannan
kiran.
Tun kafin yagaya min na san duk abinda zai gaya
min din magana ce da muhimmancinsa ta isa.
Fatima malam yabude baki yace dani "musbahu
na ba ka auran fatima, wlh fati ban taba kwana a
zaune ba, yadda naga rana haka naga dare
hnkalina ya tashi kwarai dagaske ba dan komi ba
sai dan tunanin dame zan rike mace kamar ke
fatima.
Ina sane dacewa mutane da dama suna tunanin
inasonki ne sbda yanayin shakuwar mu tun kina
karama nima ina karami to Allah yasani fatima
ina matukar kaunar ki sbda haduwar jini da Allah
kan hada tsakanin mutum da mutum amma Allah
ya sani tun da nake ko da wasa ban taba kallonki
da wata siffa ko da wata manufa ba, bayan
kanwata ina kallonki ne a matsayin kanwata
wadda muke ciki daya.
Yana magana ne cikin yanayin tausayin kai
muryarsa kasa kasa yana mata wani irin kallo,
lamarin yajefata ckin sabon tashin hnkali da
rudani idanunta suka kama zubar da hawaye,
fatima ban taba tunanin akwai lokacin da xan iya
zama in miki maganganu makamantar wannan ba
sbda kallon ki nake kamar kanwar damuka fito
ciki daya.
Shi yasa nayi ta jinjinawa yadda zaman aure zai
kasance tsakanina dake.
To amma a safiyar yau abokina mansur yasauya
min tunani akanki ya ce dani 'tunda aure bai
haramta tsakanin ka da fatima ba ba yadda za ai
kunya tahana muku nishadantar da zuciyarku ta
hanyar soyayya, shi aure dakuke gani ba bu
abinda yake rike shi yazauna lfya sai soyayya.
Ya jawo abinci yakama ci yana cewa "fatima har
na rasa dawata kalma zanyi amfani a bakina kan
yiwa Allah godiya daya azurtani da mace kamarki,
fatima in sonki wlh don Allah ni ma ki ce kina so
na inji dad'i.
Bai aune sai kawai yaga ta tashi ta faki idonsa ta
fice daga dakin a guje ya kyslkyale da darya har
da tafa hannu yace Allahu akbar, fati manya shi
abinda yake ba shi mamaki shi ne wai an wayi
gari shi da fatima sun zamo masoya soyayya
kuma irin ta aure.
Tabbas Allah ya amshi ran mahaifinsa ya zamo
maraya sai dai shi maraya ne wanda yai rashin
mahaifa amma ba wanda yarasa iyaye ba, a
rayuwa iyaye suna da daya wa mahaifa ne kwara
d'aya kachal, shi kam Allah yai masa baiwa da
iyaye nagari yagirgiza kai yana murmushi.
****************wannan page goron jumma'a ne
gareku ba ki d'aya,,,, daga jiddan nan dai 'yar
mutan
A DAREN FARKO
9
karfe goma da minti hamsin hajiya saudat ta faka
motarta a kofar gdansu ummi, ta sha ado da
wata galleliyar shadda maroon colour, ta yi kyau
kasancewar su kam Allah ya hore musu kyau da
son gayu.
ita mijinta ba wani mai wadatar zuciya bane
sosai kusan itace mai kudin don yar kasuwa ce,
daga kasar dubai ake kawo mata kayan sa wa na
mata, koyaushe gdan ta cike yake da mata
business takeyi ko ta ina.
Ita kam Alhaji muhammad ne asalin ba ta jari
amma duk da haka ba sa gani.
Taahigo uwar dakin hajiya hauwa tana kwance
kan gado ummi na kwance gefenta zancen
khalifan dai suke, saude tace "kitashi mana tun
yanzu kifara shirya kayanki don da kaina yau zan
kaiki gdan alhaji muhammadu chan za ki zauna ni
zan xan gaya masa cewa tunda Allah yayiwa
mahaifinku rasuwa ya zama dole a tallafa yaya
hauwa a gun rikonku, na san dai idonsa da kunya
ba zaice ba za ki zauna mai a gda ba sannan ita
hajiya maijidda na san za tai farin cikin xaman ki
a gdanta, don za ta ga cewa haka zaisa tasamu
fada a gunmu ke Kuma idan kinje ba cewa akayi
kisaki jiki kina bacci ba, yakin neman zuciyar
khalifa za kiyi ko ta halin kaka sannan ki dage
dun kyautatawa uwarsa, yin haka ne zai sa in
yadawo daga germany ko