Showing 63001 words to 66000 words out of 82249 words

Chapter 22 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

mai tambayar tana
harararsa tace "to bace min da gani kaje kace
ummi tadafa maka.
Zaiyi magana tace "Allah idan kana matsa mata
xan hanaka ganinta.
Yafice zuwa falo abinda yasawa ransa shi ne ba
zai iya barci ba sai ya rungumi fatima a jikinsa
ko ta halin kaka.
Anty sadiya tafito daga dakin dasu fatin suke za
tashiga dakin mama ganin shi a tsaya yasa tace
"yaya akayi boy?
Ya tsareta da ido fuskarsa ba walwala yace "ina
fatima?
Tace "wanka take.
Bai ce komai ba yasa kai dakin ummin, ta bishi
da kallo tana jinjina kai tashige dakin maman
tazauna kusa da ita tace "in kin gama ki ban in
ba ta tasha ba za tasaki jiki tasha a gabanki ba.
Mama tamika mata a sanyayae tace "kazar "yar
sokoto ta kawo ma yana kitchen idan za ta iya ci
ki hada ki bata wannan fitinannan yaron za a sha
matsala dashi dole sai an gyara fatima, sai dai ni
kam jikina ya yi sanyi wannan soyayyar da khalifa
ke nunawa fatima ta yi yawa, kada fa idan sun je
aun zauna tayi amfani da wannan damar tadinga
juya shi kamar waina.
Anty sadiya tace "don Allah mama kada ki sawa
ranki irin wannan damuwar kowa da lokacinsa
kuma a yanayin fatima ba za tayi haka ba
yarinyar ta samu tarbiyya me kyau.
Mama tace "uhm sadiya mutum ba a shaidarsa
mace tana da wani irin hali yayin da da namiji
yadaga hankali a kanta yana sonta dayawa shike
nan tasamu damar yi mai yadda taga dama
maimakon tayi amfani da wannan damar gun
rikeshi da kyau sai tadinga murza kambunta
yadda taso.
Sadiya tace "mama ki yarda da Allah ki yarda shi
ne me komi, addu'ar da kikewa khalifa ke da
abbansa ba zai taba faduwa a kasa ba, insha
Allahu bbu abunda zai faru da aurensu sai alheri,

kidauki fatima kamar "yar dakika haifa sai Allah
yakalli kyakyawan niyyarki yatsare khalifa daga
dukkan wanda zai masa abin da zai gusar da
hankalinsa, idan kaji tsrom Allah ka kyautatawa
'ya'yan wasu Alkah zai dubi na ka zuri'ar ko ba
ka da rai.
mama tace "Hakane anty sadiya ina kaunar
fatima dayawa nima yanayin soyayyar da khalifa
ke nuna mata ne yayi yawa ni na rasa me yakeji
a zuciyarsa game Da ita, in dai akan fatima ne to
fa zuciyarsa ba ta da sukuni, zai iya hakuri akn
komi banda ita.
Duk su mama na wannan tattaunawar ne dai dai
lokacin da fatima tagama wanka tafito daga toilet
daga ita sai dauri kirji sai ko dan tawul din data
yafa a kafadarta bata san khalifa na dakin ba,
ganin shi kawai tayi tsaye jikin madubi ya kuma
zuba mata wadannan fitinannun idon na sa masu
tsananin kyau da laushi, tatsaya sororo tana
kallonsa kamshin dayaji yana tashi a jikinta yaji
kamar ana fizgarsa zuwa jiki? ta, lamarin dayayi
sanadiyar daya kasa rike kansa sai da ya isa
gabanta yaja hannayenta biyu yahadata gam da
jikinsa yasa harshensa yana lasar lebbenta, gaba
daya jikin su yadauki rawa ita tsoro takeyi kada
wani yashigo ya iskesu a haka yayin da shikuma
jikinsa na rawa ne sbda wata fitinanniyar shawa
data jefa shi a cikin yanayin da bai taba shiga ba
a rayuwarsa, yakama kunnuwanta yana gaya
mata kalaman dashi kansa bai san yana fada ba,
har sai da fati taji tsigar jikinta na tashi tasa
hannu tarufe mai baki.
Kwatsam ummi taturo kofar dakin tashigo, khalifa
yasaki fati yajuyo yayi wa ummin wani irin kallo
yafice, ta ajiye abin cin data zubo musu kamar ba
abinda tagani tashiga jan fatin da hira nan kuwa
zuciyarta kamar za ta tarwatse sbda wani
azababben kishi da taji ya tokare mata kirji, sama
sama fatima ke iya magana, hira ta ki yiwuwa
domin hankalin fatiman ba ya tare da ummin, Dr.
Khalifa angonta ne kawai a gabanta shi take
muradin kasancewa tarea dashi.
*****

Tunda sassafe wasu yayyan innarsu fatima suka
iso gdan duk da ba yau ne za a kai amaryar ba
sai sati ya zagayo amma za su dafa abinci sbda
'yan'uwa maza daza su zo domin auran.
Yaya kubura tace "Ina amaryar ne?
Inna tace "Tana gdansu angon amma yanzu za
tazo.
Gaba daya suka rike baki sukece "wani irin tsarin
banza da wofi ne haka?
Yaya kubura ce tafi sauran fusata tace "Ni na
taba jin irin wannan? yaya za ayi ace amarya na
gdansu ango?
Ke ba kya tsoron ace kwadayi ne yasa ta tattare
a gdansu angon?
Yaya rabi tace "ke kike wannan xancan kubra tun
yaushe ake cewa kwadayi ne yasa ciki sati daya
aka fasa bawa musbahu aure aka bawa khalifa
don kawai babanaa yanada farcan susa, to
ballantana yanzu ace tan gdan wai acan ma
takwana, in barda zuvarwa kai daraja meye
wannan?
Inna tace "Ai ba wani abu yasa taje ba sbda
kunshi ne da gyaran gashi.
Yaya kubra tace "duk wani gyara ita batasan inda
za taje ayi mata ba sai ta tafi yawon tallan kanta
a gdan surukan, To Allah dai ya sawwake amma
gskiya kidinga lura kuna jan mutuncin ku irin
wannan abu ne ke sawa a dinga wa mutum gori
daganan mutumci yazuve. "
Inna dai tana jinsu bata sake cewa komi ba,
itama kanta ba a son ranta fati takwana gdan su
Khalifa ba mutumcin mama ne yasa ba ta iya
musu da ita, sun nuna suna son fati daywa,
hakanan fatima tasauya ra'ayin ta gaba daya
akan Khalifa.
Wuraren karfe takwas da rabi su fati suka shigo
tare da ummi, tun kafin matar da aka dauka
musamman dan tayi mata kwalliya tazo fati har
ta fara daukar ido abin gwanin ban sha'awa,
kowa yakalleta sai ya kara, fuskarta dai ce ta dan
kumbura sakamakon rashin barcin da bata samu
ta yi sosai ba a daren jiya, tsabar tunanin khalifa
da kaunarsa da asuba ne bayan sun idar da salla

tazauna jugum tayi tagumi.
Ummi tajanye hannun na ta tace "haba matar
yayana tunanin yayan ke damunki?
Tayi mata wani irin kallo tadauke kai bata ce
komi ba, ummi tayi murmushi tace "Ba kiyi laifi
ba dan kin kasa sukuni akan dr. khalifa, ni na san
tabaki yake yana dandana miki zuma a baki,
shiyasa hnklinki ke tashi dayawa, fatima ba ki da
laifi don kin damu da yaya Khalifa, bai dandana
wa mace irin wannan zumar ba ta rikice akansa
ballantana ke da yake nuna miki so irin haka har
yana hada jikinsa da naki'.
*****
Karfe goma sha dayan safiyar lahadi daruruwar
alummar musulmi suka shaidi daurin auran Dr.
Abubakar Saddiki Muhammad da Fatima Musa,
daurin auran daya samu halartar manya manyan
mutane tun daga kan manyan yan kasuwa da
sunan su yayi fice a fadin kasar nan zuwa
manyan yan siyasa da kusoshin gwamnati da jiga
jigan malaman da ake ji dasu a jihar mu ta kano,
hatta bangaran sarauta sun halarci daurin auran
ballantana likitoci da abin yazama nasu maganin
a kwabe su, maroka suka rinka yayata sunan
ango da amarya da iyayansu yayin da gdajan
rediyoyi ke ta bayyana yadda abubuwan ke
gudana, sai shiga ake ana fita da nau'ikan
abubuwan ci da na sha na alfarma daga gidansu
dr. khalifa da gdansu inna.
Angon ya sha ado ya yi kyau daya wuce misali,
abin sai wanda yagani shadda ce mai tsadar
gaske fara kal riga da wando da babbar riga sai
akayi aikin babbar riga da blue din zare, hula
kansa ma ya kasance fara da blue takalminsa
blue, a ckin gda amarya fatima irin shigar ango
aka mata fari da blue, ba a iya tantance wa yafi
kyau tsakanin angon da amaryar kowanne ba
baya bane ko ina masu hoto ne da bidiyo ke
daukar ango da abokanansa sannan suka shigo
gda tare don gaida iyayan amarya..
Gdansu fatima ma cike yake da mata anata
rangada guda d sanya albarka, fatima ta zamo
matar dr. khalifa rana ba ta karya sai dai uwar

diya taji kunya, farar tukunya mai fidda farin
tuwo, kirari iri iri maroka suke tayi musamman a
gdansu khalifa inda anan ne ake facaka da kudi
kamar ba nemansu ake ba.
Abba yadinga kyautar muhimman abubuwa yana
fadin "ai wannan rana ce ta farin ciki garesu ranar
auran dansu daya.
To fa.
Ina su hajiya hauwa da hajiya saude kannan
abba iyayan ummi? wadanda duk wani burinsu a
wannan rana bai wuce ace da diyarsu ummi aka
daura auran ba, amma hakan bai yiwu ba, khalifa
da iyayansa basu damu da damuwar kowa ba sai
ta su.
Da farko basuyi niyyar zuwa gdan ba a yau daga
bisani saude tace gara suje karshe a zo anayi
damu ai idan baka iya kama barawo ba kai sai ya
kamaka.
Ba za ka iya shaida bacin ran dake tare dasu ba
amma zuciyarsu fal bakin cki da takaici, da
isowarsu a safiyar abba yaraba musu sabbin kudi
rafa rafa yace suyi liki, duk da haka ransu ba dadi
tunanin su shi ne da da ummi aka daura auran
nan ai sun more irin wannan dukiya haka.
Bayan gama daurin auren suka kebe a ckin wani
daki, saude tadubi hauwa tace "ke wadannan
mutanen ba na wasa bane sun fi mu shiri.
Hauwa tace "Yo ba kiji abin da malam yace jiya
ba? yace ai uban fatima ne yahada wani
gagarumin asiri ya dabaibaye zuciyar khalifa
yadda b ya son kowacce mce si yarsa fatima
shiyasa muke tayin aiki aikin ya ki kama khalifa,
yace. a wani lokacin yana so ya so ummi sai
asirin yayi tasiri a zuciyarsa yakasa katabus yaji
kamar ba ya da iko a kansa sai son fatima.
Hajiya saude tace "Haba ko da naji ni nasan arina
wai an saci zanin mahaukaciya, wannan aikin da
malam keyi ba zai tashi a banza ba da mugun
abinda da sukayi, duk mu mun manta uban fati
malami ne sai da yayiwa khalifa asiri duk iyayan
ya gama dasu anma ba komi jiya da dare na je
na kaiwa malam kudin bajimin sa dayace a kawo
za a zubar da jini yace musa ido za muyi kallo

dakansu sai sun gane kurensu kowa yaci tuwo
damu miya yasha.
A DAREN FARKO
33
Mama tana iya kokarin ta akan bawa su hajiya
hauwa 'yanci a gdan dan dai kada ayi korafin
amma bata tsira ba duk inda tayi binta suke da
harara suna kwafa.
Karfe hudun yamma angwaye da wasu daga ckin
mutane aka fara daukan mutane zuwa inda akayi
gagarumar walima maza zalla, ana kiran slar
magriba aka tashi kowa yana farin ciki da sanya
alheri.
Karfe tara da rabi na daren dr. khalifa ya fito
daga wanka a dakinsa abokansa biyun nan Dr.
Bashir da Dr. Hafiz su biyu suka rage bayan kowa
ya watse,yafada bisa gado yana mai da numfashi
da kyar.
Dr. Bashir yadubeahi yana dariya yace "Ango na
amarya, amaryar ka ta yi kyau yau abin har ba a
magana sai dai kwalelen ango, ko ganinta yanzu
ba damar yi.
Dr.khalifa yace "Ba komi ai komi lokaci gareshi
rana ita yau iyanzu babu wanda zai mini shamaki
tsakanina da ita zamu kwana a daki daya sai
yadda naga dama da ita.
Kafiz yace "Oho dai ba haka aka so ba wai kanin
miji ya fi miji kyau, ko in je in dauko maka ita?
Dr. khalifa yace 'Rufa mini asiri dazun nan mama
takirani dakinta tana gaya mini idan taji na je
gdansu fatima sai ta batan rai don Allah kaji wani
danyan hukunci mutum da matarsa.
Dr. Baahir yace "Ai ta yi ma haka ne don ta san
halinka, a gdan iyayan na ta ma sai kabita ka
matseta kai ba kunyar mutane kake ji ba.
Yace "kai ba a irin gdansu fati ake wannan ba ka
san akwai inda ake barin halak don kunya.
Dr. Hafiz yace "To kai ka san kunya ne Abbakar?
ko dayake yanzu ka sauya kamar ba kai ba, son
fatima ya sauya ka dayawa kamar bakaji tashan
'yN mata ba, tunda kadaura idonka akan fatima
kadaina tunanin 'yammatan ka, tun wasunsu na
damuwa suna damun mu har sun hakura.

Yace "Kai ni ai babu sauran wata diya mace a
zuciyata tunda na mallaki gimbiyar mata fatima
ta rufe kofa gaba daya.
****
Da gari ya waye mama tazo da kanta taroki inna
da malam akan a bata fatima akwai shirin da za
ayi mata, a zuciyoyinsu basu ji dadin haka ba har
ita kanta fatiman sbda ta san dr. khalifa
matsamata zai yi a gidan amma mama tafi karfin
komi garesu, iyayan khalifa suna da kimar da za
su iya yi musu komi surutun mutane ne yake
damun su fassarar nan ta kwadayi ita take damin
inna komi akayi idanuwan mutane na kai kuma
sai sun yi magana.
Bayan tafiyar mama abinda inna da malam ke
tattaunawa knan, Fatima na dakinsu na yara a
kwance tana fama da barcin gajiya ita kanta ta
san a yanzu ta canja, ta baza kunnuwa tana
addu'ar Allah yasa kada malam ya amince da
komawarta sai dai kash sai ji tayi malam din na
cewa ta tafin kawai.
Amma dai kija mata kunne tasan abinda takeyi,
kuma tasan kanta. Ya sa kai yafita.
Inna ta kwala mata kira ta fito ckin rashin kuzari
kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki tazauna
daf da ita, tace "To malam dai ya amince da zan
ki a gdansu khalifa, jan kunne da zanyi miki shi
ne ke diya macece ki san darajar kanki idan har
kina son ki samawa kanki kima a gun khalifa na
san yadda kike biyewa al'amarin khalifa sbda son
da kike masa, to kisani namiji sai ana taka tsan
tsan da al'amuransa dole mace Tayiwa mijinta
biyayya domin aljannarta. na karkashin kafarsa
amma kada ki zake karki ja wa kanki abin fadi.
Jin tayi shiru yasa fatima a sanyaye tace "Inna
don Allah kibarni anan nima ba na son zama a
gdan nasu.
Tace "to yaya za muyi kin san ko a yanzu khalifa
ya fimu iko dake in dai aure ke sa ayi iko da
mace tunda an daura kasancewar ba a kaiki
gdansa ba ba zai hana dokar Allah aiki a kanki ba
a cikin hakkokinsa da Allah ya jarabta akanki, kai
mace daki ba shi ne sharafin biyayyar aure ba

shaidu da sadaki sune aure in dai an yi su ya
zama dole mace tayiwa mijinta biyayya ko a ina
take kuwa kinga in dai haka ne dole mu amince
da zuwanki gdansu khalifa.
Fatima taji zuciyarta ta karaya bata ankara ba
kawai sai jin hawaye na xubo mata, ,ita kanta
bata san kukan metake ba batasan ma'anar
kukan na ta ba.
Inna tayi murmushi tace "To meye na kuka,
khalifa zabinki ne fatima kin manta yadda kika
dinga kuka kina rokon a bashi ke?
Duk abinda khalifa yazo dashi dole kiyi biyayya
domin aure kikayi na soyyaya na zabin ranki da
zuciyarki,ban taba zaton xan ga hawayenki ba
bayan kin zamo matar khalifa fatima, ki share
hawayenki ki mike kafafuwanki kiyi walwala kin
auri wanda kike so.
Fatima tayi jugum ta san magana ce irin ta gugaz
zana inna take gaya mata akan abinda tayi akan
musbahu ,taci gaba da kuka sosai ,taci gaba da
kuka sosai inna ta tashi tashiga hidimomin
gabanta tana fadin "Ai sai kiyi.
Fatima ta koma ckin daki ta kwanta bata san
abi? da ya daga mata hankali ba hawayanta suka
ki tsayawa, ummi ce ta yaya lavulan dakin da
sallama tayi turus tan kallonta tace "Kukan
amarci kike tun yanzu fati ko wani abu aka miki?
Babu Babu amsar da za ta iya ba ummi don ita
kanta bata san kukan da take ba.
Ummi tace "to koma dai meye kisaki kukan tashi
kiyi hakuri kiyi wanka ki shirya tafiya za muyi
ango yana jiranki za mu fara fita hada kayan
sayan baki kafin na lefe shi khalifan ma ya so
ace Dubai za aje a hado har kayan dakinki mama
ta ce babu inda zai tafi dake ba tare da an kaiki
gdanki ba.
Fatima dai ba ta son magana ta tashi tayi
wankan, ummi tagama shirya mata kayan ta,
suka yi sallama da inna suka nufi gdan mama,
dogon hijabi da nikab tasa suna shiga harabar
gdan fati tayi sauri tashige ciki don kar su hadu
da khalifa ta zauna a falo a kunyace tagaishe da
abba da mama ko kanta ba ta iya dagawa.

Sai mama ke mata dariya tace "in har wannan
kunyar za ki sawa ranki za kiyi ta wahalar da
kanki ke kawai ni dai ba suruka na dauke ki ba a
matsayin diyata kike har yanzu, tashi ki wuce
daki idan kin huta akwai girke girke na abokan
mijinki.
Da zarar an kra dr. khalifa mijinta sai taji wani iri
a jikinta, tana jinjina alamarin kamar a mafarki
,duk yadda ta so shi a ranta take tsananin son
tadinga ganinsa a ko yaushe sbda burgetan da
yake yau tsoron ganinsa take, fatanta kada
yashiga gdan suhadu, tayi sa'a kuwa har magriba
tayi bai shiga ba tuni suka gama hada abinci mai
rai da lfya suka shirya kan tebur tashige daki tayi
wanka tasa doguwar rigar shadda koriya takara
gyara gashinta tayi sallar isha'i tana shirin hawa
gado takwanta aka turo kofar cikin tattausar
muryar nan tasa yayi mata sallama.
Khalifa ne.. A figice tadago idonta taxuba masa
yana ckin wata lafiyayyar shadda brown me
haske an mata aiki da dark brown din zare irin
dinkin tazarcen nan, kamshin turaransa yadinga
ratsa mata zuciya, ya fidda gilashinsa ya
baibayeta da fitinannun idonsa ba walwala sosai
a tare dashi yace "Fatima.
Duk kokarin da tayi na tsayuwa ta kasa svda
rawar da kafafunta suka shiga yi, ta durkusa a
gun tadafa gado.
Ya kara kirn sunanta a karo na biyu a nan ne ta
amsa, yace "Tun karfe nawa kikazo gdan nan?
Muryarta na rawa tace "sha biyu.
Yace "Amma ba ki san hanyar dakina ba
ballantana ki zo ki gaisheni.
Gabanta yafadi tadago ido a tsorace tana
dubanshi abinda ta gani a cikin kwayar idonsa
yasa tayi saurin maida kanta ksa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login