Showing 9001 words to 12000 words out of 82249 words
Chapter 4 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf
har zuwa shima
lokacin da Allah (SWT) ya kar'bi ransa sai d'ansa malam musa
yagajeshi a lokacin ma bai dade da auran fari ba inda matarsa
zainab tafito itama daga zuri'ar tsohon malamin marigYi
malam Yakubu, an ce na ji dad'i shi ne gari ba na saba ba.
Malam musa yayi kyakyawan gadon hali na hakuri datsananin
juriya irin na mahaifinsa, mutum ne mai matukar saukin kaida
sanin yakamata, hka itama matarsa zainabu bbu abinda
yadameta da zafafawa kanta game da rayuwar duniya.
Suna zaman su lfya a dan karamin gidan da yake haya kusa da
makarantarsu basu dogara da kowa ba sai Allah mutane ne
dako kadan va su da kwadayi, mutanan unguwar sunajin dadin
zama dasu sosai ana zaune lfya.
Aliyu shi ne d'a na farko da goggo Abu tafara haifawa malam
sai mai sunan malam Yakub suna cewa dashi malam, sai
rukayya sai fati sai mai sunan malam Haruna suna cemasa
baban gida sai muhammadu nazifi sai nuraddeen ba su da
wadata da dukiya rayuwa ce tarufin asiri amma akwai wadatar
zuci da son juna, rayuwarsu tana yawan ba wa mutane sha'awa
yadda suke kamun kak da tarbiyya da girmama jama'a da
'ya'yan gidan masha Allahu hka suke amma ba kamar fatima,
itace tafi fad'a kowa d'auko halayyar mahaifinsu kamar yadda
tafi kowa kama sak da mahaifinsu don hkane tafi kowa kyau a
gidan.
kaf zuri'ar marigayi malam haruna kyawawan gaske ne har
kwatance ake dashi a garin sbda kyaunsu ga uwa uba farin jini
dukda cewa ba masu kud'i bane ba su da komi sai rufin asirin
Allah.
Tun fati tana 'yar mitsitsiyarta ake mata shaidar hkuri dasau'kin
kai duk inda fatima tashiga sai an yaba halayyarta, balletana
biyayya ga iyaye wad'anda takeji kamar tayi musu numfashi
don tsananin so da 'kauna ko kuma takwanta sudinga bi ta kan
ruwan cikinta don biyayya.
Hka a makaranta malamanta ke ji da ita bayan maida hankali
akan karatu da gudun fitina ga biyayya da tsafta.
Fatima kyakyawar gaske ce daga ganinta ka ga bafulatana sak
zai wahala mutum yagaji da kallonta sbda Allah ya yi mata
baiwar kyau mai tsayawa a zuci.
Bayan auran yayarta rukayya da shekara biyu wata rana da
daddare malam musa yana zaune kan tabarmarsa goggo Abu
tana gefe itama kan tata tabarmar yayin da fatima ke zaune
kusa da su tana yi masa firfita.
Yace "zainabu yaya batun d'an gidan rukayya ya warware ko?
Ta ce "Alhamdulillah jiki kam dasau'ki yau danaje na iske shi
yanata wasa da yara.
Yace "Masha Allah, sannan yagyara zama yadubi fatima yace
"fati yaya batun haddarki ta jiya kin haddace"
Tace "na haddace har d'azun na ba da a gaban malam
musbahu ya dad'a min wani.
Yayi murmushi yace "Alhamdulillah yana daga cikin ni'imar da
Allah yake yiwa mutane shi ne yabasu 'ya'ya na gari salihai
wad'anda zasu zamo farin ciki a gareka, fatima ina matu'kar
alfahari dake sbda kinada hankali da biyayya ban ta'ba shakku
akan biyayyar da kike mana ba wannan shi ne dalilin dayasa
kai tsaye ko shawara banyi dake ba na daukeki nabawa malam
musbahu auranki sbda na fahimci halayyarku ta zo d'aya.
Shi ma mutum ne da Allah yahore masa ha'kuri dasanin
yakamata tunda nake dashi bai taba aikata min wani abu na
assha ba, sai dai ajizanci irin na d'an adam wanda yake kai
mutum ga kuskure.
Amma dukda hka ina neman yardarki, idan kin yarda ba wani
abune mai girma agareni ba don ina da ya'kini da kwanciyar
hnkali akan hakan, idan kuma kin ce baki yarda ba ma'ana ba
kya son shi ina mai yimiki rantsuwa da girman Allah ba zan
damu ba na san Allah ne bai 'kaddara musbahu mijinki bane
shi yasa kika'ki amincewa dashi.
Fatima kanta na 'kasa ta shiga shararar 'kwalla batace komi
ba, malam yace "fatima kada wannan magana tad'aga miki
hnkali balletana tajefa zuciyarki cikin damuwa.
Cikin shashe'kar kuka fati tace "dole indamu baba ban ta'ba
tunanin akwai watarana dazakayi tunanin zan bijirewa
umarninka ba, har inada abinda zanyi wanda zaisa inyi gaban
kaina ba tare da umarninka ba.
Wlh idan har akwai watarana wadda za tazo in bijirewa
umarninku ba na fata tarismeni ina numfashi a duniyar nan
gara in mutu da in ganta sbda haka baba ba na bukatar ka kara
neman yardata a bisa wani bu wanda kake nufin zartarwa a
kaina.
Na amsa malam musbahu hannu biyu biyu kuma zan yi masa
biyayya bakin iyawa ta.
Malam musa yagirgiza kai yace "Allah yayi miki albarka fatima,
Ubangiji Allah yasa kigama da duniya lfya, biyayyar dakikayi
mana Allah yasa 'ya'yan dazaki haifa suyi miki wadda tafita,
dukda haka ina mai tabbatar miki dacewa hakkinki ne in nemi
amincewarki akan auranki da malam musbahu kamar yadda
nayi miki bayani a baya ba wai dan ina shakkun amincewarki a
gareni ba sai dan in ba ki hakknki a matsayina na mahaifinki.
Yadda nake miki wannan magana haka na zaunar da musbahu
nace dashi musbahu yau fiye da shekarar ka goma a hannuna
tun lkcin dakazo da sassafe kana kuka kana ce min in
taimakeka inje in ba wa kawunka hakuri matarsa ta yi maka
sharri zai dake ka natambayeka abinda kayi mata kace min
cewa tyi dashi na yi mata sata, malam musa yace "fatima a
lokacin ne nasa musbahu a gaba har gidan kawunsa wanda
yake bayan wannan layin na mu, kasancewarsa maraya,
mahaifiyarsa ta rasu tun yana yayayye, yayin da mahaifinsa
yarasu bayan shekara d'aya tsakani wannan shi ne dalilin
dayasa kanin mahaifinsa yadaukeshi yabawa matarsa wadda
ita kuma tadauki tsanar duniya ta dora masa, take wahalar da
rayuwarsa.
Abunda yasa musbahu yazo guna shi ne "lokaci lokaci kawun
na sa yana zuwa dashi nan don daukar karatu da magriba
kuma ya san akwai fahimtar juna tsakani na da kawunsa.
Lokacin damukaje gdan nayi sallama da kawun yafito yana
ganina tare da musbahu ya hau fada ko gaisawa bai bari munyi
ba inda yake shiga ba nan yake fita ba, dakyar nasa yayi shiru
nace "Alhaji Habibu ba haka ake lamarin duniya ba, idan mace
tagaya maka magana saika bincika kafin ka dauki mataki,
sha'anin mata idan akace ba su suka haifi d'a ba sai a hnkali
ballantana d'an dayake maraya.
Albaji habibu yace "duk abinda yagaya maka karya ne don ya ji
Kawai ana cewa maraya ne duk abinda aka ajiye a gidan nan
saiya sace yasiyar sannan idan nayi masa magana sai ytafi
yana hadani da muatane ana cewa muna cutar dashi alhali shi
maraya ne don ba mu muka haife shi ba.
Ina dalilin wannan, haka kawai an ba ni ajiyar kudade masu
yawa yabi dare ya bi rana har dakina ya sace, to ba zan iya ba
yan sanda zansa sukama shi su kulle in huta ko kuma in kai shi
gidan kangararrun yara ka ga na huta.
Na dubeshi tsam sai da yagama fadace fadacensa nace"to ni
kam ba zan bari kakai musbahu gidan kangararrun yara ba
tunda shi ba kangararre bane, idan kai ba za ka iya rikon shi ba
dan kawai ba kai kahaife shi ba ni zan iya, sai dai ina son
kadinga Tunawa wannan yaron maraya ne kuma maraya ne a
gareka, idan kaci amanarshi Allah ya tambayeka kamar yadda
yazo acikin hadisin ma'aiki(SAW) ,sai ya tambayi kowa akan
abinda yaba shi kiwo, maigida mai kiwo ne Allah sai ya
tambaye shi akan iyalansa ya yatafiyar dasu..........
Ya katseni cikin hushi yace "Ni bance kayi min wa'azi ba tunda
nan ba makaranta bace, ka ce za ka iya rike musbahu, ka ga
gashinan kuje kukarata idan yagwada maka mugun halin sa za
ka koreshi ne, da kai ka kama da sannu zan ganku a rana. "
Nace "Insha Allahu ba za kaganmu a rana ba, kai ne dai za kayi
nadamar abinda kayi masa, da sannu za kaga sakayyar da
Allah zaiyi masa kuma da sannu za kagani watarana zai zama
abin taimako gareka da iyalin na ka ma wadanda kuka hada
kai dasu kuka walakantashi.
A lokacin kawun musbahu yashiga dakin da musbahu yake
kwana a zaure yadinga watso masa kayansa yana masifa a
haka nataya shi mu*a kwaso kayan, wannan shi ne dalilin
zaman muśbahu a gidan nan lokaci lokaci dangin iyayansa na
uwa dana uba sukanzo guna suna yi mini godiya shi ma yana
ziyartarsu.
malam musa yaci gaba dacewa fatima lkcn dana gama
tunasar da musbahu wannan lbri kansa na kasa nakara da
fadin "musbahu lkci ya yi dazakayi aure shekararka ashirin da
bakwai a duniya, kana bukatar ajiye iyali tunda kke baka taba
cemin ga wata mace dakakeso ba sbda kunya dakake da ita
da kawaici.
Musbahu ka rayu kana hidima gareni vakin iyawarka, allah
kadai yasan kaunar danake maka, wannan shiyasa nadauki
diyata mafi soyuwa a zuciyata nabaka ita dan tazamo matarka
uwar yayanka.
Yayi saurin fadin fTima yana me dafe kirji da fiddo idb
stories
A DAREN FARKO
7
A babban falon alhaji aka sauki iyalan malam,
falon da ba kamarsa a gdan duk wani
kasaitaccan bakon da zai gana dashi a gidan nan
yake sauke shi, aka kawo musu abubuwan ci
dana sha na alfarma.
Alhaji da hajiya maijidda suka fito aka gaisa,
malam yagabatar dasu ga iyalansa aka shiga yi
musu godiya mai yawa, alhaji hace "malam
kwarai dagaske na ji dadi matuka da zuwanku
gidan nan, sbda dama wannan gda ne na mutane
ba mu da 'ya'ya in banda d'a guda d'aya da
Allah yabamu amma idan kashigo koyaushe za ka
iske mutane da yawa a gdan ko da yaushe muna
godewa Allah kalar jama'a kam ba wadda ba ma
gani a wannan gida sai dai a gefe guda banji
dadin wannan zuwa na ku ba da sunan godiya
don banga abinda nayi ba, wlh da ace malam za
ka baiwa 'dana khalifa auran 'yarka da na yi
murna duk dan kusan d'aya muke da kuwannan
dukiyar da Allah yabani ba ta gabana ballantana
har in ga wai na fi wani.
Malam yayi shiru yana tunanin maganganun
Alhaji muhammadu, shi kam vai taba burin kai
diyarsa irin gida na aljahi muhammadu ba hakan
yasa hnkalinsa yatashi sosai jikinsa yayi sanyi.
Bayan sun dawo gida suna zaune a tsakar gida
da da daddare zainabu tace "malam ai kuwa a
dazu rukayya take ce min tunda alhaji yanemi
aure a gdan nan mai zai hana abashi fatima.
Sai ya bata rai yace "shi yasa hnkali na yatashi
lokacin da alhaji yafurta wannan magana a
gabanku, sbda ku mata ne karamin tunani gareku,
tunanin ku ba ya wuce karan hancinku, ko da
yaushe kyale kyale na duniya kan dauki
hankalinku ku aikata abinda zuciyoyin ku suka
raya muku sai daga baya azo ana nadama sbda
haka ba na son wannan magana daga yau, shi
yasa ko amsa ban ba wa alhaji ba lokacin da ya
fada, ba na ra'ayin diyata tayi auran dukiya, idan
alhaji ya kasance mutumin kirki mai taimakon
talakawa sai akace muku shi dan na sa da
sauran danginsu haka suke? da zaran mun dauki
fatima mun ba su shikenan kowa ma cewa zaiyi
kwadayi yakaimu ba za ace su suka nemi auran
ba cewa za ayi ni ne nanemi khalifa ya auri
fatima duk gorin da akanmu da duk walakancin
da akayi mata mu muka jawo.
Goggo Abu tace "kuma hakane fa malam bbu
wanda yayi wannan tunanin acikinmu kowa kirkin
Alhajin yake kallo.
************
Tun daga wannan lokacin aminci mai karfi da
zumunci yashiga tsakanin mutanan da iyalansa
da alhaji da hajiya maijidda a lokacin nan shi
khalifa yana kasar germany inda yake karatunsa
na likita.
Alhaji bai da abokin shawara sai malam haka
hajiya maijidda ta dauki goggo Abu kamar yar
uwarta tajini, dukda cewa alhaji muhammadu bai
ka ra nuna wa malam yana son yabawa dansa
khalifa auran 'yarsa fatima ba tun daga wannan
lomacin hankalin malam bai kwanta ba ba wai
don yana kin alhajin ba, malam yana matukar
kaunar alhaji har cikin zuciyarsa kamar yadda shi
ma alhajin yake nuna masa kauna ta tsakani da
Allah, auran fati ne kawai ba ya son yabawa
khalifa sbda abinda zai je yazo.
Bayan shi kansa alhajin akwai mutane wadanda
suke da kima a idon malam suna nuna
sha'awarsu akan malam yaba 'ya'yansu auran
fatima sbda kamun kai na yarinyar da uwa uba
kyawun halittarta bai taba furtawa wani ya ba shi
ba, sai dai yayi dariya kawai yace aure nufi ne na
Ubangiji.
A ranar da alhaji yazo wurin malam da daddare
bayan sun gama karatu da addu"o i yace dashi
"malam idan Allah ya nuna mana rana itayau
khalifa zai dawo daga kasar germany.
Gaban malam yafadi amma bai bari alhaji ya
fahimci fargabar da zuciyarsa ke ciki ba, ya
fadada fara'arsa yace "masha Allah ya kammala
karatun knan.
Alhaji yace "kwarai kuwa karatu ya kammala lfya
don ya samu cikakkiyar takardarsa ta shaida ya
kammala karatun sa a matsayin cikakken likitan
mata.
Malam yace "mun godewa Allah, Allah yasa anyi
a sa'a kuma Allah yadawo dashi lfya. "
*****************
Shi kansa malam baisan dalilin dayasa
hankalinsa yatashi sosai da maganar dawowar
Dr. khalifa ba, tun da alhaji yashaida masa
zancen dawowar yashiga damuwa sosai ko
goggo Abu bai gayawa ba, shi kadai yake tunani
a ransa karshen tunaninsa shi ne ba abinda
yadace yayi wanda yawuce yaba auran fatima
kafin dawowar Dr. khalifa ko da alhaji ya tada
maganar idan yagaya mai ya bada ita shikenan
an huta.
Wannan ahi ne dalilin dayasa yadauki fati yaba
amintaccan almajirinsa kuma d'ansa wanda
yayarda dashi fiye dakowa,a 'ko'karinsa na ganin
iyalansa sun zauna lfya a gidajan mazajansu, tun
ranar daya shiga gdan alhaji yatabbatar wannan
rayuwar ta fi 'karfin fatima ba za ta iya ba me
zaisa yada'u d'iyarsa yakaita inda za tashiga
wani hali rayuwar da mutum ya sabayi ita yake
iyawa,idan yaje inda aka fi 'karfinsa wahala zai
sha.
***************'Karfe bakwai daidai na yammacin
litinin jirgin IRS yasauka dasu Dr. Abubakar
Assadiq wanda aka fi sani da Dr. khalifa a filin
jirgin saman Malam Aminu kano dake nan kano
wanda yad'aukesu daga filin jirgin saman murtala
muhammadu dake birnin ikko jihar lagos, bayan
da jirgin da jirgin daya d'akkosu daga jamus ya
ajiye su da asubahin wannan rana.
Dr. khalifa dogon matashi ne kyakyawan gaske
irin mazan nan da ko wace mace ke burin
mallaka ba wai don shi da mahaifan sa sun
mallaki abun duniya ba sai dan haduwarsa na
gwarzon namiji wanda ya isa a kalleshi a san
cewa shi d'a namiji ne abin kwatance acikin
mazaje.
Yana da madaidaiciyar 'kiba wacce tadace da
tsawonsa ma'ana 'kibar da tsawon basuyi masa
yawan dazasu sa shi muni ba.
Babu inda yabar mahaifinsa alhaji muhammadu a
kyau kamanninsu d'aya har tafiyarshi dai
bambamcin halayyar abbansa mutum ne mai
matukar kirki da sau'ki kai da son mutane yayin
da Dr. khalifa yakasance miskili tun yana yaro bai
da son magana sai dai 'kar'karfar mutum ne
kuma gwarzo wanda ba shi da tsoro ko kad'an.
Dr. khalifa ya taso cikin gata da kulawar iyaye bai
san wani abu wai shi babu ba duk abinda yakeso
shi akeyi masa, hakan ne yasa yagirma cikin izza
da isa da raina mutane, sai dai yana raina wanda
yashiga harkarsa ne, idan baka kalli inda yake ba
ba ruwansa dakai, kuma bai ta'ba damuwa da
yawan alherin dayake yi wa mutane ba idan ma
Allah yayi mutum yana da rabo idan kazo neman
abu gun abbansa sai yabaka abinda yafi wanda
abban zai ba ka ma'ana dai shi kyautar sa
taganin dama ce kuma sa'a ce.
Bayan ya kammala karatun sa na secondary
yafara karatu anan jami'ar bayero dake kano.
Inda Allah yataimake shi shine dukda gatan da
yakeda shi na iyayansa bai wasa da karatu kamar
yadda sauran 'ya'yan gatan ke shagwaba suyin
karatu sbda iyayansu suna da dukiya. Dr. khalifa
tun yana nursery yake da kaifin basira wannan
yasa yake da farin jini a gun malamansa har
izuwa jami'a inda anan ne yazamo kamar jinjiri
wata sha kallo sbda farin jinin dayake dashi,
bayan dai tsabar kyau da iya dressing da Allah
yahore masa.
Kaifin basirarsa yana burge kowa sannan ga
'barnar dukiya dayake wa abokai maza da
mata,shi yasa duk inda Dr. khalifa yake sai ka ga
mutane ana wata irin shafta mai dad'i.
A cikin Bayero 'yan matan dasuka shiga
mawuyacin hali akan son Dr. khalifa Allah kadai
yasan yawansu yayin dashi bai san suna yi ba,
wasu suna ganin sbda dukiyar ubansa ne suke
sinsa, kasancewarsa dan gata ahi kad'ai suka
mallaka duk wannan tarin dukiyar da Allah yaba
mahaifinsa shi ne mai mallakarta to kuma shi
akwai 'ya'yan manyan masu kudi suna matkar
sonsa, su ba abinda suke nema dashi sai shi
kansa, shi mutum ne mai saurin d'aukar hankalin
d'iya mace sbda Allah ya ba shi surar da mata
keso wadda take burge su.
Sai dai kash babu soyayya acikin ra'ayin Dr.
khalifa, babi wata d'iya mace daya taba kallo
yace yana ao da bakinsa wadanda suke nuna
masa soyayyarsu ma share su yake kamar bai
gane ba, a lokuta da dama har tambayar kansa
yakanyi wai meye so?
Ta yaya kake ganewa ka kamu da son wance?
Shekarar sa hudu da kammala digiri dinsa
nafarko a Bayero mahaifinsa alhaji muhammadu
yace "yayi shirin tafiya germany inda yakeson
yayi karatun zama cikakken likitan mata.
Lokacin dayake gaya masa wannan magana suna
zaune ne a falon abban na cikin gida dasafe suna
breakfast tare da mamansu hajiya Maijidda.
Dr. khalifa ya ajiye cup din shayi yana kallon
abbansa yace "abba na ji koda yaushe fa kana
gaya min bbu abinda kafi bukata wanda yawuce
inzauna kusa dakai in kula maka da harkokin
kasuwancinka.
Abba yayi murmushi yace "ina sane da wannan
khalifa sai dai hakan ba zai hana in yi abinda
ydace ba, ina burin kazamo likita don in gina
maka babban asibiti anan kano wanda zan
sadaukar dashi sbda Allah a dinga taimakawa
bayin Allah wadanda ba su dashi.
Yace "abba toh kasuwancin na ka fa? ba ka son
in taimaka maka akansa?
Yace "kada kadamu da wannan saddik ina
bukatarka a kusa dani a ko da yaushe sbda
abubuwa suna mini