Showing 30001 words to 33000 words out of 82249 words

Chapter 11 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf

ne da ba
ya son raini da ace yanada sausaucin ra'ayi zai
iya kula ummi da sunan soyayya tunda da
sha'awa mai zafi amma a bisa la'akari da yadda
yanayinsa yake bazai iya baiwa ummi fuskar
soyyaya ba dan gudun kada tarai na shi tunda
yana ganin ta ne a karamar kanwarsa, malamin
daya fara shaida musu wannan batu ya tabbatar
musu da cewa wannan shi ne hakikanin ra'ayin
dr. khalifa wanda yake tafiya akai, hajiya hauwa
tace,"to malam ba za a iya tankwasa zuciyarsa
yasota ba ko ya ki ko ya so, malam mahaifin
yaron nan dan uwanmu ne matarsa ta asirce shi
bai jin maganar kowa sai tata duk wannan uwar
dukiyar daya tara idan bbu shi ita da khalifa za
su mallaketa.
Malam yayi murmushi yace "akwai hanyar hakan
amma ba zai yiwu ba har sai ya dawo kasar nan
dazama sbda za muyi amfani da kasar daya taka
ne muyi masa aikin da mukewa lakani da bita zai
zai, zaita bin ummi sai yadda tayi dashi, anan ne

suka dan yi murmushi hnkalinsu yafara kwanciya.
"Yace suyi hakuri nasara sai a hankali da hakuri
ake samunta ba da gaggawa ba,.
****
Fatima da jiddah daga can london din ke damun
ummi akan tadinga neman khalifa a waya da
sunan za ta gaida shi bai dace tabar damuwa a
cikin ranta haka ba, suna ba ta wannan shawarar
ne saboda ganin yadda hnkalinta ke tashi
musanman fatima da ke kusa da ita tana ganin
yadda ummi ke kuka akan rashin khalifa tun tana
boye wa har kukanta ya bayyana ita kanta mama
ta fara gane damuwar da ummi take ciki, dukda
cewa ba a san abinda ke damunta ba idan ta
tambayeta sai tace bakomi, mama ba ta son
takurawa ummi sbda tanajin dadin zama da ita.
Rannan dai da fatima ta matsa mata akan sai ta
kira khalifa a waya tayi murmushi tace "fati idan
yabamu amsar da za ta daga mana hankali fa?
da muguwar rawa ai gwamma kin tashi, fatima
tagirgiza kai tace "wannan hujjar ta ki ba za tasa
mi ta zama ckin damuwa ba, idan kin ce da
muguwar rawa gwamma kin tashi ai kuma kar ki
manta ance a rashin kira karen bebe ya bata
kuma a rashin tayi akan bar arha, ummi tajawo
wayarta ba tare da ta ce komi ba ganemo
nomban khalifa takira ckin sa'a tashiga.
Bata jima ba tana ringing yadaga cikin
kasaitacciyar muryarsa yai sallama gaban ummi
na faduwa tasa hands free dan fatima taji da
kunnanta.
Ta gayar dashi ya amsa tace "ka gane me
magana yayana?
Yace "na gane mana ba ummi bace.
Tace "ni ce kira nayi dan mu gaisa na ga tun
tfyarka kana tmbayar kowa a gdan nan amma
ban da ni, bansan laifin da nai maka ba, .
Yayi dan jim kamar ba zai amsa ba, daga bisani
yace "ina cewa kowa lafiya? idan nace kowa
lafiya kina ciki.
Ta ce "shi knan nagode yaya karatu.?
Ya amsa "karatu Alhamdulillahi.
Za takara magana taji dif ya kashe wayar tayi

murmushin takaici tace "kin ji ko?
Wadannan abubuwan ne suka sa ba na son
bugawa khalifa waya, ba wai dan ba na jmson jin
muryarsa ba kullum farin cikina ko da a waya ne
in dinga hira da khalifa ina jin muryarsa amma ba
zan samu wannan hadin kan daga gareshi ba,
sbda ba ya bukatar soyayya dani.
Hawayen dasuka zubo mata yahana. ta cigaba da
magana, hankalin fatima ya kartashi taji tsanar
khalifa ya kara kamata, wai wani irin mara imani
ne wannan tasa dankwalin ta tana sharewa ummi
hawaye, tace "ki yi hakuri insha Allahu khalifa zai
zamo mallakinki.
Ta ina?
Akwai wanda zai yiwa khalifa auren dole? idan
har kuwa ba auren dole za a yi masa ba to ba
zan same shi ba don baya sona, rokon dazan miki
daya neduk yadda mama za tayi miki akan ki
gaya mata abinda yake damuna kada kisake
tasan cewa khalifa nake so.
Fatima tayi mata wani irin kallo tace "matsalarki
knan ummi banga ta inda za a samu mafita ba
ana wannan boye boyen.
A DAREN FARKO
16
.Sai da dare yayi sosai khalifa khalifa yadawo
gdan tare da shu baby yau ta yi masa nacin da
dole ya amincewa kwananta. agdansa, ahi kansa
bai san dalilin dayake gudun kawo mace gdansa
ba sbda anisa, tun daga nau'in kayan jkin shu
baby za kasan lalacewar ya yi yawa, a ranta tace
"tabbas yau sai na ga abunda khalifa yake tsoro,
tabi bayansa zuwa ciki, anisa na kwance a bisa
kujera a fali tana kallon wani film a wayarta, duk
zamanta a gdan bata taba ganin khalifa ya zo da
mace ba duk da ta san yana tare dasu sai fa yau,
suka dubi kowa ita da shu baby kowacce tashaki
wani masifaffan kishi a zuciyarta, anisa ta maida
kanta tana kallonsu suka wuce dakinsa, bby tace
"sbda wannan figigiyar yarinyar dama kake kin
kawo ni gdanka?
Yamata wani irin kallo yace "kiyi abinda ke
gabanki shuu wannan kanwata ce ba na son....

Bai cigaba da maganar ba yashige toilet yayi
wanka yayi alwala, bayan ya idar da sallar dake
kansa yaleka falon yace "anisa wannan da kika
gani abokiyar karatuna ce ki kawo mana abinci
daki kuma ina so ki gaisheta.
Yawan kukanta yana ba shi haushi ganin ta fara
share kwalla yasa ya koma cikin daki, tunanin da
anisan tayi shi ne wai ita wacece ne a gun dr.
khalifa da har zai gujewa bacin ranta, tunda
takawo kanta zama a gdansa dole tahakura da
duk abinda za taji ko tagani, a sanyaye tamike
tashirya abinci a tray tashiga dakin da sallama
tatsuguna ta gaisar da baby tafita, kallon daya
bita dashi yakara baiwa baby haushi taja tsaki
tabude abincin taxuba a plate tafara ci, dandanon
abincin ya burgeta ga takaici da kishin wadda
tadafa, shima yazuba na sa yana ci yana fadin
"kai aniaa ta iya girki mijin ta ya mori mace.
Sun kwana suna morar junansu ta hanyoyi daban
daban wadanda suka kware a kansu ko
wannenau ba baya bane a wannan harkar, sun
gamsu iya gamsuwa hakan yasa kowanne
zuciyarsa wasai ba damuwa, khalifa na son yayi
bacci sosai amma yunwa ta hana shi baccin dole
yafito falo sai dai tebur wayam yaleka kicin ba
abinci bbu anisa yadawo dakinta ya iske doguwar
takarda mike bisa gado tun kafin yakaranta ya
san abinda ta kunsa yace"shikenan shukura ta ja
min asarar mai dafa min abinci da kula da gdana.
Salam.
Abbakar ina maka ban kwana tare da fatan allah
yasa kagama karatunka lafiya ka koma gda lfya,
xamana a gdanka ya kare ba tare da na gaji da
ganinka ba sai dai yin haka shi yafi mana ni da
kai, na gode kwarai dagaske da masuakin daka
ba ni a gdanka duk da cewa hakkana bai cimma
ruwa ba na samun masauki a zuciyarka wanda
shi ne makasudin zuwa na wannan kasar, amma
dai na godewa Allah daya ba ni ikon aikata
abinda natabbatar zai wahala ka manta dani har
ka koma ga mahallincinka, ina rokaonka a duk
sanda katuna dani kai min addu'ar alheri. khalifa
na zo wannan kasa ne dan neman soyayyarka da

take ta cin zuciyata tun daga ranar da idanuna
suka fara ganinka na yi suk kokarin da zan iya na
ganin na ja raayinka banyi nasara ba, tun daga
gda nigeria har izuwa yanzu dana tabbatar ba
zan same ka ba, daga karshe ina maka fatan
dukkan alherin duniya dana lahira.
Ni na san bbu namijin dazanso bayan kai,
Anisa....
Iya abinda takardar takunsa knan, har gumi yaji
yana keto masa sbda tsabar tausayin anisa,
yadinga jin wani iri a ransa yana tunanin rayuwar
dasukeyi wadda ba ta da wani amfani a garesu,
idan suna gaban iyayansu sai su dinga nunawa
su na kirki ne amma a bayan idon iyayan na su
suna aikata abinda suka ga dama.
Shin tsakanin iyaye da Allah wa ya fi dacewa aji
tsoro, in har suna boyewa iyayansu halin dasuke
cki ne don suna tsoronsu, Allah daya halicci
mutum shi yafi dacewa a ji tsoro, kuma Allah
yana kallon mutum a ko wani hali yake.
Wannan nasiha da khalifa yaiwa kansa yasa yaji
nan take komi ya fice mai daga rai ya tsani yan
matan dayake tare dasu na holewa, yana bukatar
yazamo natsatsen mutum wanda yake biyayya ga
Allah da manzonsa, takaicin abubuwa da dama
suka kamashi har yaji kyamar kansa da kansa
yakeji, yamike jikinsa ba kwari yafito daga dakin
yadawo dakinsa, ya isje shu bby har yanzu
baccinta take cike da nishadi da kwanciyar
hankali, yasa hannu yagirgizata dakarfi tabude
ido tana fadin "bacci ke damuna,yace " ba na iya
juriyar yunwa.
Tace "ina yar aikin gdan nan?
Yace "ba ta nan.
Ba abinda shukra tatsana irin girki amma da yake
khalifa ne haka tadaure tadafa ruwan tea da
dankali da plantain, ba wani kwarewa tayi da
girkin ba yunwa ce tasa kawai yaci.
*****
A DAREN FARKO
17
Tun daga wannan lokaci rayuwar khalifa ta sauya
gaba daya yadaina sauraror kowacce mace har

da ita kanta shuu babyn, hatta fAisal ya watsar
dashi sbda ya yi ya yi yaja hankalinsa don shima
yadawo hanya tagari faisal ya yi masa wani irin
kallo shekeke yace "kai kiwa meya sameka da za
kace mudaina rayuwarmu, tajin dadi mu takura
kanmu, ko mafarki kayi ka mutu an sa ka a
wuta?
Khalifa yace "ko kusa banyi wani mafarki ba na
dai yi wa kaina fada ne dan na fuskanci gaskiya,
na ga yakamata inja hankalinka kaima damu
daina wannan rayuwar kafin ranar nadama tazo
mana.
ko wata amsar kirkifaisal bai ka ra bashi ba
yamike yavarshi a gurin,hakan yasa khalifa ya
janye jikinsa yakoma rayuwarsa shi kadai, yanemi
masu dafa masa abinci da gyaran gida bai zuwa
ko ina sai makaranta inya dawo yakan kulle
kansa a dakinsa yayi ta nazarin abinda yake
karantawa ko karatun alkur'ani mai girma wanda
a baya ko bude shi ba ya yi sbda shagalta da
rayuwa da ya ya mata dayayi, sai yake jin dadin
rayuwarsa a haka hatta hotunan sa da
nambobinsa ya goge, yayi ta karfafar zuciyarsa
tare da neman gafarar Allah yana rokon Allah
yataimake shi yaraba shi da wannan rayuwa.
A haka a haka har Allah yataimake shi
yakammala karatunsa yakawo shi inda ya fito da
kyakyawan sakamako zuwa babban likitan mata a
lkacin ya dada kasaita irin mazan nan ne da dole
idan aka kallesu a kara sbda cikar zatinsu,
kwarjini da ilimi, 'yammata sun yi sunyi suja
ra'ayinsa kowacce tana fatan yasota amma ya ki
bada kai, matar aurance har yanzu baiga wadda
yagamsu yaji ta yi masa zai zauna da ita a
matsayin matar aure ba, amma dai mace ta
holewa ya yi alkawarin insha Allahu ya daina.
Kafin ranar dawowarsa gida nigeria ya yi ta
neman yadda za ayi yaga anisa ya rasata haka a
kano bai san a ina zai ganta ba, yana yawan jin
tausayin ta tare da yimata addu'a duk sanda
yatuna ta.
Tunda ya daura damarar tahowa gida damuwarsa
itace yarinyar nan ummi ya san ta yi girma yanzu

sosai ta kara wayo a baya ma ta iya budar baki
tace tana son shi ballantana yanzu, bayan shi ba
wani sakar mata fuska yakeyi ba ballantana ace
shi kwata kwata ba ya da ra'ayin auran zumunci
kuma ko yana dashi ma ummi bata cikin
lissafinsa, cikin hikima yatambayi mamansa a
waya ko an yiwa ummi aure, tace ai bata fidda da
mijin ba ma ba ta sauraron kowa tun da tayi
candy abban k7ma ya ce ya dace ta fidda mijin
aure tunda mutane dayawa suna nunawa suna
sonta in ya so taci gabada karatun a gdanta sai
tace wai wanda takeso din ya yi doguwar tafiya
idan yadawo za ta gabatar dashi.
Wannan yafadarwa dr. khalifa gaba ya tabbatar
yarinyar nan in baiyi da gaske ba zata zame
masa matsala, har ranar dawowar tasa tunanin
da yake fama dashi a xuciyarsa knan, yarinyar
tashiga ran mamansa za a iya cewa sai ya
aureta ko da yake bai da matsala da abbansa,
maganar mamansa kuma da karfi a kansa baya
son bata mata rai.
*****
Karfe sha biyun rana fatima tagama shiryawa
cikin wata blue din batik mai haske riga da zani
ne amma kai kace siket ne sbda yadda kayan
suka zauna a jikinta suka yi mata kyau abin har
ba a magana, ita da kanta ta yi sha'awar kanta
sbda kayan sun mata kyau, telan dayayi dinkin ya
gwanance a fagen tsarawa mata dinki, ta jima
tana gyara gashinta ya dau kyalli ta tsara daurin
dankwalin sosai yadda yadace da adonta tazuba
fashion da mayafin da suka dace da kayan, ummi
ce ta bukaci taraka ta gdansu yau wato gdan
iyayanta, fati bata fiye son xuwa gdansu ummi ba
sbda jininsu bai haduwa da hajiyarsu ummin ba
tare da ta san abinda tayiwa hajiyar ba, tana cin
darajar diyarta ummi ne kawai sbda a halin yanzu
ummi tanad\ matsayi lamba daya a zuciyar
fatima ba ta da na biyu kowacce irin alfarma
fatima za ta iya yi akan ummi.
Innar tana zaune a kofar dakinta tace "inna sai
mun dawo.
Tace "adawo lafiya a gaida su.

Tayi sallama a kofar dakin malam musbahu
yadago yadubeta sai yayi saurin bude idonsa
gaba daya yace "kai fatima wacce irin kwalliya ce
wannan? kin ga yadda kikayi kyau kuwa?
Ta lumshe kyawawan idanuwanta tana murmushi
tace "ka manta na gaya maka za muje gdansu
ummi.
Yace "fatima gskiya in banda ummi na da
matsayi mai girma a gareni ba zan iya barinki fita
cikin wannan kwalliyar ba ban taba ganin ranar
dakikayi kyau a ido irin wannan rana ba, fatima
ina fatan Allah ya mallaka min ke.
Tace "malam ai ya mallaka ma saura kadan
yarage komi lokaci ne.
Ganin zai tsaida ita da maganganu na santin
kyaun datayi yasa tawayance tafice tabarshi yana
hadiyar yawu kamar yabi ta yayi ta kallonta yau
kyaun datayi masa daban ne.
Bayan sun gaisa da mama tawuce dakin ummi ta
iske ta tana shiryawa tace "mutuniyar kin hadu
kayan nan sun yi miki kyau bana wasa ba.
Fatima tace "kai wai ke ba kya gajiya da yaba
kyau na ne? kullum sai kin cena yi kyau.
Tayi dariya tace "to ai yabon gwani ya zama dole
kinyi kyaun ne ba na gajiya da kallonki fatima,
don Allah idan kinyi aure kada kidaina kwalliya
kina matukar yin kyau da kwalliya dukda cewa
idan ma bakiyi kwalliyar ba kyau kike yi ke kam
Allah ya yi miki baiwa da yawa fatima.
Tace "don Allah kiyi sauri mutafi kadda yamma
tayi ba kya gajiya da surutu.
A cikin mota suna tafiya ummi tana tuki fatima
tana gefenta suna hira, tace "duk inda muka wuce
fa sai an kalleki fatima ina kallon wani dazun da
danja ta tsayar damu sajra kadan yabuga wa
wani sbda kallonki, kidinga sa nikab kidaina
daukar hankalin mutane.
Ta dubeta tace "su sukaga za su iya ni bance
wani yakalleni ba duk wanda wani abu yasame
shi a dalilin kallona to shi yadauki alhakin kansa,
muyi wata hirar.
Tace "yawwa ai kuwa yau zan miki gagurumin
albishir.

Fatima tace "Allah sarki ai kuwa ni bani da wani
labari da nake son ji mai faranta rai daya wuce in
ga khalifa ya dawo ya amince da batun auranki
da shi, wlh a wannan rana bansan farin ckin
dazanyi ba, bansan yadda zan fassara wannan
rana ba, gskiya anty ummi ina kaunar khalifa ne
sbda son da kike mishi., duk da cewa na tsane shi
tawani fannin sbda ba ya da tausayi.
Ummi tayi dariya tace"ummi misali idan ke ce
wani namijin yazo yana miki irin son danake wa
khalifa za ki tausaya mai kiyarda da auran ko da
ba kya sonsa ?
Fatima tace "ummi ni mutum ce da ba na son
ganin musulmi dan uwana a cikin damuwa in dai
har na san yana zubda hawaye akan ciwon so na
irin yadda kike zubda hawaye akan son khalifa
zan tausaya mishi.
Ummi ta girgiza kai "to albishirinki soyayya ba
haka take ba.
Tayi saurin katseta da fadin "ko ma yaya take
ummi, khalifa ba shi da kirki, ba shi da tausayi,
ya kamata mutum yaso mai sonsa, ya kamata
mutum yakasance mai tausayi, nikam ba zan taba
yiwa khalifa uzuri ba, duk da haka don Allah ina
rokon idan khalifa yadawo kasar nan...... "
Ummi tayi fakin a kofar gdansu tace "ki kwantar
da hankalinki idan Allah ya kaimu gobe khalifa zai
dawo kasar nan.
Tadafe kirji tare da fiddo ido tace "don Allah
dagaske kike ?
Tace "kada kiyi shakkar hakan kizuba ido gobe za
kiga dr. khalifa.
Ita kantaa ummi bataji dadin samun hajiya saude
a gdan ba sbda a fili suke nuna ba sa son fatima,
yayin da ita kuwa ta tsani mutum ya nuna mata
ba ya son fatima, tana matukar kaunar fatima a
ranta.
Fatima tatsuguna har kasa tagayar dasu su ka
amsa kowacce fuska ba fara'a suka ja baki suka
tsuke, wayar fatima tafara ringing tamike tayi
sauri tafita ganin sunan malam musbahu, nan da
nan hajiya saude tazubawa ummi harara tace
"wai me kike nufi da yawo da wannan kodaddiyar

yarinyar, duk inda za ki sai da ita za ki, sai da ita
za kizo gdan nan ma kin dauko ta kina nufin duk
abinda xa mu tattauna akai sai dai muyi a
gabanta knan ba mu da wani sirri sai ta ji ?
Hajiya hauwa tayi tsaki tace "ba ma wannan ne
abin haushin ba saude sai yadda ummi take bata
rai idan munce muna son magana da ita wai lallai
sai duk abinda za a fada a fada a gaban fatima.
Bayan ita fatimar idan sun tashi na su sirrin da ta
ta uwar tafiya take gdansu suyi maganarsu ba a
gaban ummin ba.
Hajiya saude tace "ai ummi ba ta da wayo na
rasa wacce irin soyayya takewa fatima kamar
wadda ta asirceta, ga ta dai a haka kamar wata
mai wayo nan kuwa ba komi a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login