Showing 72001 words to 75000 words out of 82249 words

Chapter 25 - A DAREN FARKO COMPLETE Book by Rabi'atu Nasidi Abubakar .pdf


gaskiya ba da ace zan vi hanyar gskiya wannan
hanyr da kika nuna mini ba zan kauce mata ba

tunda hanya ce ta hakikanin gskiya.
Na marairaice murya "ummi bakin ki ne ke furta
wannan kalma na ta'addanci ki ji tsoron Allah
kidaina fada ni har kin sa tsoro ya kamani.
Tabushe da dariya tace "kidaina damuwa jiddah
babu wanda nataba fadawa wannan maganar sai
ke, kuma na gaya miki ne sbda ke din sirrina ce
babu maganar da ba zan iya gaya miki ba duk
nauyinta kuwa.
Nace "meye amfanin gaya min din tunda na ba k8
shawara kin ki dauka, har da bakinki kince abinda
nafada gaskiya ne kiyi wa Allah ummi kiyi hakuri
da dr. khalifa kada soyayyarsa tasa ki haukace,
don ni na fara zargin kin samu tabin kwakwalwa
ne, lfya kalau kike ba za kidinga furta wannan
mummunan lafazin ba.
Tace "Lafiya ce ta sani furta wa kuwa jidda zan
kuma aikata.
Na ce "to meye laifin khalifa don bai so ki ba, ana
soyayya dole ? ke yanzu za a tursasa ki son
wanda ba kya ra'ayinsa ?
Tace "Nima bance miki dr. khalifa ya aikata min
wani laifi ba, zan kashe shi ne don kowa yarasa
shi sbda sun nuna min rashin tausayi shi da
iyayansa sun san ina son khalifa amma lokacin
daya dawo daga germany ya rikice akan cewa
fatima yake so sai suka watsar da komi ba sa
kallon kowa sai dansu suka fifita bukatar sa akan
ta kowa aka bashi fatima sbda gata ana bukatar
farin ckinsa, idan har khalifa zai kasance ckin fari
ciki to basu damu da kowa ba da komi ba
wannan ne dalilin dayasa zan kashe shi kowa
yarasa.
Nace "kai lallai ummi kin cika mara hankali, to na
ji za ki kashe shi ba kya tsoron kema kar a kashe
kin ? kinsan fa hukuncin wanda yai kisa kashe shi
akeyi ko bakisan da haka ba.
Dariya sosai tayi tace "na sani mana jidda ai ni
mutuwa hutu ce gareni da akan rashin khalifa, ke
bari in gaya miki wani abu matukar ina cikin
duniyar nan ba zan bar khalifa yarayu da wata
diya mace ba ne ko zan yi hakuri da auran khalifa
ba dai fatima ba don fatima ta ci amanata ta

yaudareni na gama gaya mata sirrin zuciyata da
niyyar ta taimake ni tasama mini fada a zuciyar
khalifa amma ina maimakon tayi min hakan ganin
son da khalifa yake mata sai tayi amfani da
wannan dama tabi hanyar data mallake zuciyarsa
har yadinga nunawa tamkar zai mutu ne idan
yarasat., duk fa fatima da khalifa sun san halin
danake ciki basu tausaya min ba, jidda ko ke din
nan bakisan sirrin zuciyata cikin abinda yashafi
khalifa ba yadda fatima tasani, ta san ydda nake
kwana ba na barci, ta san yadda nake kwana
idona na zubar da hawaye, ta san yadda nake
yini ba ci ba sha, duk sbda na rasa khalifa, amma
fatima tashare tashiga fafutuka akanta, har sai
data mallakeshi, ita kadai yake kallo, itace a
gabansa, wannan shine dalilin dayasa nace yadda
narasa shi itama tarasa shi.
Nace "Don Allah ummi me zan gaya miki ki
fuskanci cewa wannan kuskure ne babba za ki
tafka ? duk wannan abubuwan da kike fada ba
hujja bane wanda za tasa ki raba fati da khalifa
ta wata hanyar m bllantana ta wannan
mummunar hanyar, don Allah ummi kiyi hakuri.
Tace "Jiddah karki bta bakinki da ace, zan iya yin
hakuri da tuni na ba wa kaina hakuri.
Nace 'na ji ki bi duk hanyar da za ki bi don ganin
kin rabasu amma ba wannan ba.
Tace "jidda kudimmu dayawa sun salwanta akan
in raba fati da khalifa in ja hankalinsa sai
yakasance ma kamar soyayyarta ake kara masa,
babu wata hanya da za tayi tasirin rabasu sai
wannan hanyar da zan bi, dole in bita kiyi hakuri
kawai
Nace "To naji tawace hanya xa kibi ki kashe
shin ? ashe ke yar ta'addace ban bansani ba ?
Tabushe da dariya tace "duk lokacin dakika samu
labarin an kashe dr. khalifa, ni ummi ni na kashe
shi, idan kin dawo kya ji bayanin hanyar da zan
bi....
To nan ne takashe wayarta.
Tun daga wannan rana ban sake samunta a waya
ba, hankalina ya tashi sosai idan nayi yunkurin
kiran wani sai in ji a jikina kamar ba da gaske

ummi take ba ko kusa ban yarda za ta iya aikata
kisan kai ba, to kada yakasance nafada ita kuma
ba gaske take ba dana rasa yadda zanyi sai nayi
shiru naci gaba da addu'a. Ba a dade dayin haka
ba wata rana da safe wani matashi yazo gdan
danake zaune a london yace sako ke tafe dashi
yana son magana dani, nace "daga ina ?
Yace "Daga kano, na zo miki da wani muhimmin
abu amma na roki yazamo sirri a gareki.
. ****
Jiddah zaria,,, to ko wani sirri ne kuma
wannan ???
A DAREN FARKO
37
Duk da cewa zuciyata bata kwanta da mutumin
ba amma na daure nace ba kmai shigo muka
zauna a falo yana duba na yamiko min wani
memory card, nace "Na meye.
Yace "karbi xan miki bayani.
Na jima ina kallonsa sannan nace "kana tunanin
zan karbi abinda ba ni da masaniya akan sa.
Yayi murmushi yace "don Allah kar ki damu
wannan abin ba zai taba zama abin cutarwa
gareki ba face yazamo abin amfani na tabbatar
ba za ki taba mantawa da zuwana ba yayin da
kika fahimci muhimmancin wannan abin a gunki
idan bukatar sa ta taso.
Nace "to ai ni bansan daga ina kake ba, ban san
meye a cikin sa ba ballantana in san dalilin daya
sa ka ban shi, ka fada min mana idan kana son
in karba.
Yace "jidda kiyi hakuri dai ki karba wannan
memorin ba wani ya shafa ba illa aminiyarki
ummi.
Yajefo min kan cinyata yamike tsaye yana cigaba
da kallona yace "na daina lallabaki akan ki karba
idan kin ga dama ki jefar dashi nidai ai na kawo
miki, ina son kisani lokacin da ummi tayi miki
wayatace za ta kashe dr. khalifa ina zaune duk
wani bu da kuka fada yana ckin wannan memory
daga bisani za kiga wasu muhimman abubuwa
da xai miki amfani a ciki, in kuma har yanzu baki
gamsu ba za ki iya jefar dashi.

Yana gama fadar haka ya kama hanya zai fice,
na dauki memodin jikina na rawa nabishi ina
rokon yadawo yagaya min sunansa kuma yayi
min karin bayani don ba karamin rikitani yayi ba.
Yace "Babu wani bayani dazan kara miki, jin
sunana kuma ba ya da amfani gareki a yanxu
tunda dai kikaji nafadi haka kin san wannan
memorin yanada amfani gareki, kiyi hattara ki
kiyaye kada ki bude shi sai bukatar hakan ta
taso.
Iya abinda yafada min knan yafice yabarni tsaye
da memory card a hannuna jikina na rawa.
Jidda tayi shiru.
Kowa ma a kotun shiru yayi ana kallonta, masu
rubutu na yi masu nazari na yi. fatima na tsaye
kyam inda aka tsaida ta ko motsi ba ta yi ba,
kallon dakowa yake wa jidda itama shi take
mata.
Ummi kuwa da kai tsaye ita abin yake shafa tana
zaune tadaura kanta bisa cinyarta itama dai bata
motsa ba, mutanan da basu sn ita abin yashafa
ba basu kalleta ba iyayan marigayi dr. khalifa da
iyayan fatima fatima da wadanda suka san itace
umin da ake nufi sun dawo da kallonsu kanta, ina
zaton shi ne dalilin daya sa ta sunkuyar da kanta
bata dago ba, to ama dayake hankalin mutane na
kan jidda da mahukunta suna son jin yadda
al'amarin ya kaya sai basu motsa da wani abu ba
suka fuskanci jiddah don jin yadda za ta kasance
cikin wannan al'amari mai ban mamaki, aka ba
ma jidda umarnin taci gaba bayyana labarin
datake bayyanawa, tadora da fadin.
Bayan tfiyar wannan mutumin nazauna shiru ina
tunanin al'amarin nayi shawarar in bude wnnan
memory a wautata in ga meye a cikinsa, haka
kawai sai naji tsoro ya kamani, kamar wadda
akayi wa dabaibayi nakasa budewa kuma nakasa
bayyanawa kowa al'amarin, nayi masa ajiya mai
kyau har zuwa lokacin danaji gabaki daya na
kasa samun natsuwa idan nakwanta bacci sai
bacci ya gagareni, in kuwa nasamu barcin zan yi
ta fama ne da mafarkai masu ban tsoro, dole
tasa nabaro london ina ckin karatu na nadawo, a

ranar dana dawo din nasamu lbrin an kashe dr.
khalifa lamarin daya tayar mini da hankali sosai,
nana da nan natuno hirar da mukayi da ummi a
waya wanda tun daga wannan rana ban sake
samun ummi a waya ba sannan itama bata sake
kirana ba, a wannan lokacin ne nadakko wannan
menoryn nabude naga abinda ya kunsa.
Jidda takara tausasa lafuzanta cike da ladabi
tace "ya mai shari'a wannan memorin shi ne
shaidata dukka abinda nafada yana ciki.
Mai shari'a yabada umarnin akawo na'urorin
dazasu haskawa dukkan jama'ar da ke gun abin
da ke cikin memorin, nan da nan aka kawo
jama'a suka baza idanuwa cike da mamaki, har
lokacin ummi bata daga kanta ba kuma babu
wanda yayi mata magana.
Abinda allon talabijn din yafara nunawa shine
ummi ce tsaye a wani guri ita kadai, ta sha ado
tayi kyau dayawa ,wani matashi yabullo ta
bayanta yace "ummi gani na zo.
Ta waiwayo tadubeshi tana murmushi tace
"sannu dazuwa yaya.
Yayi murmushin shima yace "yauwa ummi ya
akai naga fuskar ki ckin damuwa ?
Daga gani wani abu yana damun zuciyarki, gaya
mim ko meye zan taimake ki in dai zan iya.
Tayi murmushi tace "na san za ka taimakeni yaya
shi yasa na fiddo maka damuwata, duk da cewa
magana ce nazo maka da ita mai tsananin nauyi.
Yabushe da dariya yace "kada nauyinta yadameki
maganar dakika iya dauka nikuma sai ta
gagreni ? Dubeni da kyau fa ummi.
Ta jinjina kai.
Yaci gaba da fadin "ummi tun lokacin dana ganki
zuciyata take bala'in son ki, kina ta shareni kin ki
ba ni hadin kai, kin sha walakantani a gaban
yarana ina kyaleki, kowa na mamakin yadda naki
tsayawa in dauki kwakwaran mataki akan ki, na
san ke da kankikin san kina yaudarar kanki ne
kina ganin kamar kinfi karfi na ne shiyasa ban
dauki mataki akan ki ba, ba haka bane ummi da
ace na yi niyyar rabaki da rayuwarki gaba daya
da yanzu na gama dake, da ace na yi niyyar

dauke ki in boye da yanzu na yi, amma dayake
duk ba wannan manufar ce a zuciyata ba na sa
miki ido duk dacewa kullum kwanar duniya
azabtuwa nake da soyayyarki, Allah ne yasa min
sonki a zuciyata ba tare da manufar komi ba face
in aure ki, ban taba sha'awar auran diya mace ba
sai ke, tun daga ran da na ganki sai naji kawai
ina sha'awar ace na gina gda na ajiye matar aure
nima ta haifa mini 'ya'ya yadda maza keyi sai
gashi ban samu hadin kanki ba.
Aka hasko fuskar ummi tayi murmushi tace "ba
komi ka kwantar da hankalin ka yaya lokaci ya yi
da za kasamu hadin kaina yadda kake bukata.
Yace "Za ki aureni ummi ?
Ta amsa "zan aureka in dai kai min wani aiki shi
ne sharadin aurena da kai.
Yace "wani irin aiki ne wanann ummi gaya min
shi komi wahalar shi zanyi in dai zai sa ki aureni,
aurenki shi ne cikar burin rayuwata a duniya, ba
ni da bukatar komi domin na mallaki dukiya, mace
sai wadda na zaba in yi amfani da ita, ke kadai ki
ka tsaya mina zuciyata ba na son bata miki rai
na fi son in aureki in zauna dake a matsayin mata
ta, yanayi ne daban taba fuskanta ba a rayuwa
ta.
Unmi tace "wannan damuwa ta ka ta zo karshe in
dai kayi min abinda nakeso zan mallaka ma kaina
a matsayin matar aure.
Yace "To fada min meye wannan aikin ko zan
rasa raina zan miki.
Tayi murmushi tace "Akwai wani mutum mai
suna Abakar ana cemasa dr. khalifa.
Shi nake so kawai ka kashe mini in dai khalifa
yabar duniya kazo a daura mana aure.
Yavushe da dariya mai karfi yace "shi knan ko da
wanda za akashe bayan shi ?
Ta Girgiza kai "shi kadai ne ba na son gani a
duniya.
Yace "an gama yaushe kike son a kashe shi ?
Tace "A DARANSU NA FARKO da amaryarsa kuma
ina so a kashe shi ne ta sigar da za ayi zaton ita
amaryar ta sa ce takashe shi, in dai kayi min
haka ka biya dukiyar auran ummi.

Yasake bushewa da dariya yace "in dai kisan
kaine ko ta wacce hanya mun iya ta sai dai in
bamu sa kammu ba.
To daga wannan shafin sai aka hasko dakin da
aka kai fatima, fuskar ummi ce ta bayyana yaya
na binta a baya tabude mai murfin kwaba
yashiga.
Sai kuma aka hasko ummi t shiga daya murfin
kwabar ta rufe.
A wani shafin kuma an hasko fuskar dr. khalifa
ne ya bude kofar kwaban da yaya ke ciki, sai ga
yayan ya fito tsulum ya tsaya gaban dr. khalifa
cikin zafin nama yadamke masa baki ya hantsila
shi kan gado yasa filo yadanne bakinsa.
Sai aka hasko fuskar ummi ta fito ta maida
murfin kwaba ta rufe ta hau kan gadon da
karamar wuka a hannunta ta nunawa dr. khalifa
daf da kunnansa takai bakinta tace "Ni ce ajalin
ka.
An hasko fuskar khalifa yanata wutsil wutsil
bashi da damar magana.
Sai kuma aka hasko yaya ya amshi wukar
hannun ummi ya chakawa dr. khalifa sau biyu,
sai suka fice daga dakin suka rufe kofar shi da
ummi.
Bayan wannan,
Sai akaga fuskar yaya a zaune kan kujera unmi
na gefensa yace "Aiki dai ya kammala kuma ya yi
kyau ummi ya batun aurammu ?
Ummi ta harareshi tace "wai kai meyasa ba ka da
hankali.
Yaya yazaro ido "Ni ne ba ni da hankali ummi ?
Tace "To ina kaga hankali.
Yayi murmushi yace "Ni kuwa nake da hankali.
Ta girgiza kai tace "babu rashin hankalin daya
wuce kace kai dinnan kanada hankali kai daman
ka yarda zan aureka ?
Ya kura mata ido yace "ummi ni kikawa haka ?
kin san waye ni kuwa ? ki guje shiga cikin hadari.
Tamike tsaye tace "shi yasa nace ba ka da
hankali kamar ni in rasa wa zan aura sai dan
ta'adda, ko ka manta kai dan ta'adda ne, ka
gaggauta fiddani daga zuciyarka domin bazaka

taba samuna ba.
Yayan yamike tsaye yanuna ta da yatsa yace "kin
yi babban kuskure ummi sai kinyi da na sani da
kika mini domin baki yaudareni ba illa kanki.
Ta kyalkyale da dariya tace "yaya ba zan yi da na
sani ba har abada domin ka mini aikina dr.
khalifa dai ya mutu kuma ba zai dawo ba buri na
knan yadda na rasa shi kowa ma yarasa ka ga
zancan nadama ma gareni bai taso ba, in kuma
za ka kashe shi ne to bismilla.
Yace "Ba zan kashe ki ba sbda na yi alkawarin ba
zan kashe ki ba ummi amma xan ba ki mamaki
daman jikina ya ba ni za ki yi min wannan
butulcin shi yasa na shiryawa hakan, kin z hannu
ummi.
Daga wannan ranar ba za ki kara yaudarar wani
a duniya ba, idan ma kin ci gaba da rayuwa ni
daman nawa ta kare.
Iya abinda memorin ya kunsa knan TV tayi dif
kamar yadda kotun tayi shiru kamar ba kowa duk
da yadda tacika makil da mutane, abin mamaki
har yanzu kan ummi na kasa bata dago ba.
Bayan wani dan lokaci mai shari'a yadago kansa
bayan ya ajiye biron da yake rubutu yace.
"Kotu ta gamsu da bayanan da jidda tazo dashi
tare da hujjojin dakowa yagani a zahiri, don haka
ba tareda bata lokaci ba nan take wannan kotu ta
sallami fatima kuma ta bada umarnin a kawo
ummi da wanda yakashe khalifa, shari'a ta dawo
kansu wannan yakawo karshen zargin da akewa
fatima na kisan mjinta Dr. Abubakar Saddiku a
bisa kwararan hujjoji na shari'a.
A DAREN FARKO
38
Karfe takwas na dare agogo ya nuna, malam
musa mahaifin su fatima na zaune kan tabarma
da rediyo gefensa yana jin shirin iya ruwa fidda
kai da akeyi gdan rediyon kano.
Inna tafito daga dakinta tazauna dab da shi tce
"malam ni fa lamarin nan na fatima ya dameni.
Yarage sautin rediyon idanunsa na kanta yana
mata kallon rashin fahimta yace "me kuma
yafru ?

Tace "ka ga yau satin ta biyu da fitowa daga
kurkukun nan amma har yanzu ta ki daina kuka
idan an tmbayeta sai tace wai babu komi, ni abin
nata har ya fara ba ni tsoro.
Malam yace "kira min ita.
Ta kwalawa fatima kira tafito a sanyaye ta
tsuguna a gefe yace "Haba fatima wannan kukan
da kike yana nuna cewa tamkar ba ki ki yarda da
kaddara bane shi duk abinda Allah ya hukuntawa
bawansa va makawa sai ya faru, godiya ya
kamata muyi wa Allah daya takaita mana
al'amarin ya tsaya a haka, addu'ar da muke yi ce
tayi tasiri da karshen al'amarin yazo, ko meye na
tsananta damuwa, tunda kika fito daga kurkuku
kike kuka kin ki cin abinci isashe, kin ki magana
kin daina barci isashe to yaya kike son mi miki ?
Fatima tayi ta yi tahadiyi kukan dake makale a
idanunta ta kasa ta dora kanta a guiwarta
hawaye suka dinga ambaliya a fuskarta, tace
"kuyi hakuri baba wallahi ina jin ciwon
damuwarku sakamakon damuwar da nake ciki
wadda tayi sanadin damuwarku ban san yadda
zanyi indaina kuka ba tabbas da na daina amma
ba yadda zanyi nima ban san lokacin da nake
kukan ba, zuciyata ce ba za ta iya jurewa
abubuwan dasuka faru ba, ina cikin bakin ciki da
damuwar abinda ummi tayi min nakasa sabawa
da damuwar rashin khalifa, ummi bata yi min
adalci ba da tasa aka kashe khalifa na san tana
sonsa amma ita tanuna min ta hakura dashi ta
gaya min cewa idan bai aureta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login