Showing 39001 words to 42000 words out of 44977 words
Chapter 14 - MATAR UNCLE BOOK COMPLETE BY MISS HAJO.docx
ya sameta har ta fad’i”ummi ta fad’a Cike da rud’u.
”ummi don Allah yanzu duk ba wannan ba kizo karta mutu a nan na shiga ukku”
Cike da rud’u ummi ta fice ba tare da ta saurari yan uwanta da ke tambayarta lafiya ba Kai tsaye d’akin Adnan ta nufa tare da fara knocking da sauri domin ko neman waya ba ta tsaya saurara ba ya bude cikin sauri ta ce.
“fito don Allah muje ka kaini gidan yaya Bukar dauko makullin motar da sauri wai Ayda ke kofar gidan ba lfy”bai tambaya ummi komai ba shima sai sauri yayi wajen dauko makullin tare da d’aukar ummin a mota ya tada motar a matuk’ar guje.,
noor ta cigaba da jijjiga Ayda ba ayi minti sha biyar ba motar Adnan ta faka daga shi sai ummi cikin rudu ummi ta fito ta na Kama Ayda kafin ta kalli noor ta ce kamomun ita taimaka muje asibiti bar kukan “
suna kakkame kaman d’aukarta suka ji Adnan ya d’auketa kamar tamkar jaririya ya na nufar bayan motar da ita…….✍️
*CAPACITY CAPACITY CAPACITY NA CE INA MATA MASU CAPACITYN SUKE NA CE INA CAPACITY A WAJEN MACEN DA BA TA K’AMSHI*?📢 NA K’ARA DA CEWA INA AMARE DA UWAYEN GIDAN DA SUKA AMSA SUNANSU SHALELEN MAI HOUSE KAI HAR MA DA Y’AN MATAN DA SUKE KAN CIN LOKACINSU UWA UBA AMARE MASU NIYYAR SHIGA DAGA CIKI TOH GA BABBAN ALBISHIR GAREKU MANYAN MATA NESA TA ZO KUSA DOMIN HAD’ADDIYAR MAI KAYAN K’AMSHIN NAN WATAU *AREEJBYABEER* TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA TURARRUKA KO WANI IRIN LAUNI TUNDAGA KAN *TURAREN WUTA,NA KABBASA,HUMRA,OIL,HALUT OUD,KAJIJI,HUMRA’S GUMELIAN DA SAURANSU* KUNSAN KIMAR MACE DA DARAJARTA BA TA TAB’A CIKA SAI DA K’AMSHI,TURAREN @byabeer YA NA DA MATUK’AR SIRRIKA DA TASIRI GARE KU MASOYA MUSAMMAN WANNAN DA YA KASANCE NA MUSAMMAN DAGA WAJEN Y’AR MUTAN LARABAWA NA TABBATAR KIKA FARA AMFANI DA KAYAN K’AMSHIN arej by Abeer SAU D’AYA TO FA GASKIYA KIN GAMA NEMAN KO WANI IRIN TURARE DON MAI HOUSE DA KANSA ZAI DINGA MAGIYAR A NEMO WANI TA NA NAN A CIKIN GARIN KADUNA *Areej by abeer*
SANANNA CE A HARKAR K’AMSHI TA NA TURA KAYANTA KO WANI STATE CIKIN AMINCI UWA UBA HAR MA DA KASASHEN K’ETARE MUSAMMAN Y’AN UWA MUTANEN NIGER GA KAYANTA DA SAUK’IN KUD’i GA KUMA BIYAR BUK’ATA DA ZUCIYAR MASOYI KU TUNTUB’ETA A KAN NUMBER WAYARTA +234 816 492 1522 KO KUMA A SHAFIKANTA NA SADA ZUMUNTA DOMIN GANI DA IDO TIKTOK @areejbyabeer INSTAGRAM @byabeer SAYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA*
*KWALISA!!!!!KWALISA!!!!!KWALISA*
*INA MATA Y’AN KWALISA MASU JI DA GAYU HAFSAT COLLECTION TA MUSAMMAN CE WAJEN ZAKULO MABANBANTA HADAD’D’UN KAYA NA GAYU TUNDAGA KAN NA SAKAWA,KITCHEN, K’AWATA D’AKI DA SAURANSU ADO DA KWALLIYA SHINE CIKAR MACEN DA TASAN KANTA BA TA WASA DA KAYAN GAYU MUSAMMAN DA SUKA KASANCE NA DABAN DAGA FITACCIYAR Y’AR KASUWAR DA TA YI FICE A WANNAN FANNIN UWA UBA GA SAUKIN FARASHI BABU INDA BA TA AIKA KAYAN TA KUMA CIKIN YARDA DA AMINCI KAR KI BARI A BAKI LABARI Y’AR UWA DOMIN DUK MACEN DA TASAN KANTA BA TA WUCE HAFSAT COLLECTION BA TA NA SAYAR DA,
ATAMFA
LACE
CAMPY GWON
BAGS
SHOES
KITCHEN VTENSILS AND MORE
KAI TSAYE ZA KU SAMETA A ADDRESS D’INTA KAMAR HAKA
*KANO STATE KURNA LAYIN KUNYA STORE*
KO KUMA NUMBER WAYARTA KAMAR HAKA
*08131850861*
*_Miss hajo ce*_🤙🏿
♠️♣️ *MATAR UNCLE* ♣️♠️
```MALLAKAR```
*HAJARA L SADEQ*
Miss Hajo✍🏾
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*Marubuciyar*
👇🏾
Auren wata Tara
Ni da yaya arman
Khadijatul sabren
Ribar so
Najmat abiy
Mata tace
Komai mukaddari ne
And now
MATAR UNCLE
*Page d’aya ya rage mu kammala free page na littafin MATAR UNCLE a page 20 zamu tsaya zaku yi payment 300 kachal garab’asa kafin 26/July ya koma price dinsa na 500 ku tura Kai tsaye ta asusun Bankin nan 7026166536 opay Hajara Abubakar Lawal tare da shaidar biya ta 07026166536*
🅿️……………………….*19*
tare da bude bayan motar ya sakata tare da zagayawa ya shiga mazaunar driver noor ta shiga gaba ummi na baya.,
a matukar guje yabar anguwar *M & A CLINIC & MATERNITY LIMITED* na ga an rubuta a hadadd’en jikin madaidaicin private hospital d’in da motar Adnan ta kutsa ciki,.
Koda isarsu Kai tsaye d’aukarta ya yi ya na nufar Cikin ainahin Asibitin da ita bai jira daga su ummin ba’
emergency aka amshe ta ummi na biye da su taimakon gaugawa aka shiga bata Adnan ya ki barin wajen tamkar shima likitan ne ga wani respect na musamman da ma’aikatan ke basa har k’asa su ke dukursawa don gaishesa amma Sam hankalinsa ba ya kansu.,
baka tab’a fahimtar yanayin da yake ciki amma fuskarsa ta bayyana damuwa k’arara a cikinta.,
sunkai minti talatin kafin su samu daidatuwar dawowar numfashinta da saituwar bugawar zuciyar na ta bayan sun tabbatar wa da su ummi Insha Allah lafiya qlau za ta tashi ta had’u ne ko ta ga ko kuma ta saurari wani Abu da kwalwarta ta kasa d’auka hakan na faruwa kafin a basu gado bayan sunyi mata allurar bacci.
ummi da noor suna zaune gadon da ke kallon na Ayda a yayinda Adnan ke kan gadon da take Kai idanunsa a kanta ba ko kiftawa.
”wai dr din sun fada maka abunda ke damunta”?
ummi ta fada damuwa karara a fuskarta “har lokacin hankalinsa na kan Ayda ya ce.
” sun ce firgici ne da tashin hankali suka haddasa suman nata akwai abunda ya daki zuciyarta “
“Ikon Allah to ke noor kema kinyi zaune sai kuka kike kin kasa fadamun me ke faruwa tukwana ma me ya kaiku gidansu faruq da Daren nan Ina aka tab’ayi”
noor kasa bawa ummi amsa ta yi sai cigaba da kuka da tayi don ita kanta Cike ta ke da fargabar maganganun umman idan hakan ya kasance gaskiya ya Ayda zataji ita kanta gabanta da zuciyarta bugawa suke ina ga wacce abun ya faru da ita“”
shikenan ai tunda bazaki fad’a ba saikiyi ta kukan”
ummi ta fada hankalinta duk tashe idanunta itama Akan na Ayda,
sai karfe sha biyu da rabi na dare ta tashi dakyal ta iya bud’e manyan idanuwanta da takejin sunyi mata matuk’ar nauyi ga kanta da take Jin tamkar an daura mata gammo da kaya.,
cikin tsananin furgici da tashin hankalin da ya dira cikin zuciyarta ta na shirin mikewa ya rike hannunta gam fusgewa take Shirin yi da karfi ya Kara mayar da ita tamkar mai rad’a ya ce.
”kina son jima kanki ciwo”wani irin kuka ta fashe dashi bata San lokacin ta ta fad’a jikin uncle ba Tana cigaba da fashewa da kuka ta kasa furta kalma koda guda shafa bayanta ya ke a hankali ya na Jin saukar numfashinta ya na sama saboda kuka cikin kuka da tashin hankali ta ce.
“Uncle don Allah ka fad’amun Waye mahaifina nasan kai bazakayimun karya ba da gaske ni shegiya ce kamar yanda umma ta fad’a uncle karka boyemun don Allah ka fadamun gaskiya da gaske bani da uba”
“Innalillahi wa inna ilaihirajiun hasbunallahu wani’imal wakim Kai amma Allah ya tsinewa habiba tayi asara “
cewar ummi da ta Kai bangon b’acin rai jin abunda bata zato da tsammanin zai fito daga bakin Ayda ba.,
Kafin ta mik’e hankali tashe ta isa ga Ayda ta na taso da ita daga jikin Adnan da ya kasa kwakwaran motsi ta na zama gefenta tare da dafa kafad’arta ta ce”
“Habibar ce da kanta ta fad’a maki wad’annan maganganun takwara”?
Cikin kuka ta ce”Ummi so nake ku gaskatamun Ina son sanin asali na don Allah ummi karku boyemun da gaske ba ni da uba”?
“Ya subhanallah”ummi ta fada ta na dafe kanta da ya wani irin Sara mata”kafin Adnan ya ce.
”waya fad’a maki wannan banzar maganar”
Cikin kuka ta ce”umman Faruq ce”Wani irin zafi da radad’i zuciyar Adnan yake ji abunda ya ke guda shekara da shekaru
Kafin ya kalli ummi ya ce”Yanzu idan na yi k’aran Matar sai ace na yi rashin kirki ko?”
“baza a duba ita halin da ta sanya zuciyar yarinya k’arama ba haka za a danne laifin ta a ga na Wanda ke Shirin kwatar mata y’anci za a ce dangantaka alhalin ita ba ta duba wannan ba”
Jiki sanyaye ummi ta girgiza masa Kai tasan tun ta na yarinya ba a tab’a Ayda a ci bulus zai iya hakura idan shi akayiwa laifi amma ba ya hakuri Akan Ayda ta ce”babu shari’a tsakaninmu komai mutum ya yi don kansa akwai Allah ai ya na madakata ka yi hakuri Insha Allah za ta girbi abunda ta shuka “
Girgiza Kai kawai Yayi tare da maida kallonsa ga Ayda da ta had’e kanta da gwuiwa ta na kuka ya ce.
“kina son na fad’a maki gaskiya ko”?
Ya fada don son kwantar mata da hankali “da sauri ta d’ago fuskarta da tayi jab’e jab’e da Hawaye ta ce”
“Eh uncle don Allah karka b’oyemun”ya ciro handkerchief daga aljihunsa tare da kama goshinta Ayda Jin tafin hannun nasa ta ke tamkar audiga yayinda hannunsa guda da ke rike da handkerchief din ya shiga goge mata hawayen kafin ya ce ta ja numfashinta ta sauke a hankali ta yi kamar yanda ya ce.
”mikewa ya yi da kansa ya nufi fridge ya na fito da robar ruwa tare da komawa ya zauna Ayda ta zama kamar mutummutumi sai binsa da ido ta ke kafin ya bude da kansa tare da mika mata ya umarceta da ta sha Kad’an ta sha kafin ta sauke wata nauyayyar ajiyar zuciya ukku a jere har lokacin hawaye zirara suke a saman kumcinta “
“Uncle ka fad’amun wacece ni”ya ce”Ina son ki nutsu ki bani aron hankalinki sannan ki yarda da ni kinsan ai bazan maki karya ba ko?
ya fad’a da alamar tambaya “gyad’a masa Kai ta yi ta ce”na sani uncle “ya ce”Toh duk Wanda ya fad’a maki maganar nan k’arya ya ke wallahi ke halastacciyar y’a ce da aure aka haifeki kamar ko wace Y’ar sunna”
Wata nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta na Jin ragowar zafin da zuciyarta ke mata kafin ta zuba masa idanu ta ce”
“Toh uncle Waye mahaifina”?ya ce”wannan bayanin zanmiki daga baya amma yanzu Ina son ki kwantar da hankalinki kuma bana son ki fadawa kowa maganar nan kinji”
Kai ta gyadawa uncle sai a sannan ta kalli ummi da tayi nisa a cikin tunanin da ta lula ta ce”ummi don Allah ki taimakamun a fasa Auren nan wlh bana so Allah da gaske na ke“
zuba mata idanu ummi tayi kafin ta sauke numfashi ta ce”ai inaga bakin alkalami ya Riga ya bushe Aida ta ya jibi d’aurin aure a ce an fasa ai bazaiyu ba sai kija ayi ta maganganu karshema sharri ya shiga kinsan mutane “
wani irin kuka ta sanya tare da hade Kai da gwuiwa ta na cigaba da kuka ta ce”wlh ummi bana son Auren nan ki taimakawa rayuwata kar a d’aura na shiga ukku ni maryam “
“k’aran kofa sukaji alamun fitar adnan nan noor ta samu damar dawowa gadon ta na Kama hannun Ayda ta ce.
“wlh Nima Ina bayanki ba Kya aurensa ummi karkiji irin wulakancin da mamansa ta mana kuma ma kila da saninsa akayi ummi don Allah kar a D’aura Auren nan a fasa”
”maganar fasa aure ba zata tab’a yiwa ba noor Bakin alk’alami ya Riga ya bushe wannan na daga manyan manyan abubuwan da muka dinga guje mata a baya ta nace ta ce sai shi babu Wanda ya mata dole don haka bazata sa mu zama kananun mutane ba sai da biki ya rage kwana d’aya ta ce ta fasa ba ta isa ba wlh”
kafin ta fita ta bin bayan Adnan Wanda lokacin har ya amso musu sallama ummi ta Kama Ayda har mota da har lokacin kuka ta ke.,
magunguna aka basu suka dauko hanyar gida lokacin k’arfe d’aya ta gota ba k’aramin tashi hankalin su aunty Laila ya yi ba da jin batun nan kasa daurewa aunty Laila ta yi a daren ta dannawa faruq Kira ka na jin muryarsa kasan ya na cikin tashin hankali ya ce.
”wlh aunty ba da masaniyata umma ta wulakanta Ayda ba ni kaina da nayi tunanin irin maganganun da zata fad’a mata wlh da ban kaita ba sai da na fito take fadamun da kanta irin maganganun da ta fada mata yanzu Ina aydar fatan wani Abu bai sameta ba“
Aunty Laila rai b’ace ta ce” faruq idan akwai matsala a Auren nan tun kafin a d’aura a hakura dashi wannan wari irin cin mutunci ne a Kira yarinya har gida ayi mata wannan ai wulakancine sannan duk ubanda bai fasa cewa Ayda shegiya ba uwarshi a rariya ta haifesa shegiyarce sai ta nemi Y’ar halak ta aura maka Autan maza ka zo ka d’auki Kayan Aurenka ba ayin Auren”
ya na Shirin magana aunty Laila ta ja tsaki iya b’acin rai ranta ya b’aci ba ka tab’a cewa ta na da wannan fushin kafin ta mai da kallonta ga Ayda da ke jikin Mamy har lokacin Hawaye ta ke.
ta ce”banza sakarya duk ke kika ja mana masifa inbanda alakar Auren ta isa ta miki wannan cin mutuncin tun bakije ba kin fara cin karo da matsaloli wlh ummi idan za aji tawa a hakura da Auren nan”
ummi ta ce”koma meye ita ta ja ai Ana fasa Auren maganganun da zasu biyo baya sai sunfi gwara a d’aura Auren anga daman ace ma k’anjamau gareta saida akayi awo ynzu aka gano komai mutane na iya fad’a kinsan hatsarin fasa Aure kuwa a irin lokacin nan Laila inba Abun ya kai tura ba “mu bisu da addua kawai”
Wani irin zafi da radad’i zuciyar Ayda ta ke ta ya zata musalta wannan al’amarin a cikin zuciyarta wlh bata son Auren nan har cikin zuciyarta takejin bazata iya zaman Aure da faruq ba“
Daren ranar ba Wanda ya rumtsa bacci saidai barawo tunda safe faruq ya zo bada hakuri ya samu ya shayo kan iyayen dakyal kuma sun fahimci bashi da laifi,
lokacin idanun Ayda da ka kallesu kasan ta sha kuka ta gode Allah ,
duk yanda ya so ta fito kin fita tayi tamkar ba amarya ba ranar haka ta yini Cike da k’unci sai bayan la’asr ganin ta k’iya a shiryata ga shi fir ta ki cin abinci dakyal aka samu ta sha hollandia shima kad’an saida ta ga ran ummi ya b’aci Akan sai mutane sun fahimci akwai matsala tukwana ta samu aka shiryata amma har lokacin kallo d’aya zakayi mata kasan ta na cikin damuwa”.
Kamu sukayi wanda tun fara bikin sai lokacin faruq ya halarta a wajen kowa saida ya so ya fahimci akwai damuwa tattare da amarya sai akayi tunanin ko kewar rabuwa da gida ce haka dai aka gama kamu komai Yayi kyau gwanin burgewa saidai rashin walwala daga amarya.
Bayan gama kamu kowa ya watse ya rage daga Ayda sai kawayenta sai mufeda su noor ma sun tafi kallonta jawahid ta yi ta ce”
“Meyasa wai naga yau duk Baki da walwala gashi faruq ya aiko motoci a maidamu kin kiya kince ba me shiga ko fad’an da aka Saba akayi Ana bikin ma”?
ta ce”bakomai fa ummi ta aiko driver ya taho ai zai maidamu”
Khairat da ke karasowa wajen minti kusan talatin da fitarta waje ta zo tare da Kama hannun Ayda suka matsa cikin sauri ta ce.,
“don girman Allah Ayda kiyi mun wata alfarma d’aya Waziri ne ya zo ya fi sati biyu ya na mun magiyar na hadashi da ke kuyi bankwana akwai maganganun da yake son fada maki don Allah karki musa kije minti biyar ya yi yawa”
Ayda na zaro idanu ta ce”meyasa zaki mun haka khairat wlh na ma manta da shi gaskiya bazanje ba kawai wani ya ganni ayimun wata fasaarar daban”
“wlh ba kowa kofar saida na tabbatar ba kowa shysa ko su jawahid ba su sani ba Allah ya bani tausayi ganinki kawai ya ke so wai gudummawa yake son baki frame yayi miki kuma akwai maganar da yake so kuyi daga bankwana meye Ayda kinsan bawan Allahnan ya soki ko darajar wannan ya ci mana”?
Ta ce “to me zaisa bazai Baki ba dole sai ni zai ba gaskiya bazanje ba”
ta Kai minti goma ta na yiwa Ayda magiya kafin ta yarda ta bi bayanta ba ason ranta ba “
ja ayda ta yi ta tsaya alamun ya fito suyi maganar bayan isarsu wajen da ya yi parking motar tasa.
”khairat ta ce”ki shiga kuyi maganar a mota kinga kar bisa tsautsayi wani ya ganki cikin zaifi sirri nake ga“
dalilin wannan ya sanya Ayda yin yanda khairat ta ce “Wani irin kallo ya ke bin Ayda da shi Wanda ya sanyata k’asa da kanta cikin sanyin murya ta ce.”,
”Ina yini “wani ajiyar zuciya ya sauke bayan ganin khairat ta bacewa ganinsa kafin yayiwa duka ilahirin motar lock ya ja ta a guje kamar zai tashi sama.
a matukar firgice Ayda ta fara kokarin budewa taji a rufe ta juya cike da tashin hankali ta bud’e baki da niyyar magana ya hura mata wani farin abu Wanda a take ta fice daga hayyacinta tare da sulalewa jikin kujerar gaban motar sumammiya…….✍️
*wasa farin girki littafin Matar uncle ba a fara komai ba tukun wannan duka sharen fage ne daga Page 21 zamu tsunduma asalin labarin Kudai kawai ku hanzarta antayawa paid grp Masoyan asali ba a fara komai ba tukun duk wacce ta San in ta saya zata fitar mun da littafi don girman Allah karma ki saya mu rikewa juna amana*🙏
*CAPACITY CAPACITY CAPACITY NA CE INA MATA MASU CAPACITYN SUKE