Showing 9001 words to 12000 words out of 44977 words

Chapter 4 - MATAR UNCLE BOOK COMPLETE BY MISS HAJO.docx

11 Aug 2025

1445

da zumburar Baki gaba ta gefen ido momy ke kallonta

samun Mufedah tayi tare da Iman babbar Y’ar aunty Aisha “.

“Aunty Ayda tun dazu ke muke ta jira tun fa 3 mukazo ya akai aunty Mufedah ta rigaki dawowa”sarkin tambaya kin tsaya mugaisa ko tambayoyin zaki fara”iman ta tura Baki Tana cigaba da game a wayar Mufeda ta ce”Munb’ata “kamota tayi tare da bata peck a kumatu ta ce “sorry Daughter ni na isa jeki kuyi wasa a waje”ta fad’a Tana mata wayau “ba musu ta mik’e tayi waje”mufedah ta ce”ya zaki koreta “Tana bud’e jakarta ta ce “Abu zan gwada maki ”

Ta na gama bude jakar ta fiddo dalleliyar iphone 15 sabuwa dal a kwalinta tana karkad’a wayar da murmushi a fuskarta ta ce “Haba yarinya ya zan Bari kaina ya kulle nayi sabuwar waya”

?zaro ido Mufedah tayi ta ce15pro nake gani Ayda waya saya maki”Dariya ta sa ta ce”wa fa zai sayamun kike tunani?ta ce “kaina ya kulle waya saya maki”

Ta ce”Wallahi saurayi nayi yau da haduwarmu da sayan wayar awa biyu ba ayi ba anjima ma yace zai zo ga gidan duk na ga a Cike”

”ta fada ta na yatsine fuska”da tsoro a fuskar Mufedah ta ce”Kaii gsky Ayda Bakiji wlh ko tsoro ma bakyayi to idan su ummi suka gani kice musu me”ba mai gani saidai idan ke kika fada musu lokacin da yaya Faruq zai kawomun tawa nikuma saina sayar da wannan na sha shagalina da kudin”Mufedah dai duk ta tsorata ta ce “saidai ki sayar da waccen tunda 14pro ce daman kina korafin level dinki ya wuce ta”ta na daura towel da nufar toilet ta ce “wlh ko 15pro dinma zan lallaba ne amma sai nayi 16pro hankalina zai kwanta “koda ta fito daga wanka shiri tayi sosai tayi kyau cikin blue din Egypt abaya don tafi sakasu bata fiya son Dubai sosai ba kwalli kawai ta kurta sai lipstick da ta sanya a lebenta tayi rooling gyalen kamar ka sace ta ka ruga flat shue tasa kasancewarta doguwa batason saka dogon takalmi ya subhanallah sak ta fito tamkar horul ayn da aka siffanta mana su gaskiya ba namiji ba ko mace ta kalli Ayda saita burgeta balantana namiji irinsune halittan da duk hassadar mai hassada Toh fa bai isa ya kusheta babu makusa a tattare da ita.

turarruka masu dadin kamshi ta fesa tanajin kiransa na shigowa wayarta ko kula wayar batai ba saida ta gama shirinta tsaf kira na biyar tukwana ta amsa cikin zazzakar muryarta mai matukar sanyaya zuciyar mai sauraro ta furta”Okay Ina zuwa ba jimawa”

Kallon kanta tayi a madubi tare da yin murmushi ita kanta ta san tayi kyau mayar da wayarta tayi jaka tare da fitowa cikin takun nan nata na kasaita mai matukar Jan hankali juya idanu tayi tare da tura Baki gaba kafin ta sauko palourn ganin duka kowa yana palourn sai hira ake yayinda Noor da mufedah suna gefe suna ta hira “

Masha Allah daughter wannan irin kyau haka ko duk mu akaje akayiwa kwalliyar “murmushi ta yi tare da zama kan hannun kujera ta na satar kallon momy da tayi kamar bata ganta ba ta ce”A a aunty zanyi bak’o ne dai”ah Kice faruq ne zaizo ja’iri ko a waya ba ya kiranmu muna gaisawa a haka kuma yake son mu bashi d’iya dukda shima d’in namu ne”

”Aunty Aisha ta amsa charab da cewa”Allah ubangiji ya kiyaye wlh mudai bazamu basa ba aunty donfa bakya yawan zuwa Baki San irin dibar albarkar da yake mata ba yanzu haka ba waya hannunta ya amshe idan ya daka mata tsawa kamar mala’ika tsoronsa take kamar rai da ajali wannan mai mugun halin irin na uwarsa zamuyi fatan bawa zukekiyar kanwarmu da ta fita zakka”Ummi na hada fuska ta ce”

“bana son irin maganar nan Aisha meye na siffantasa da mahaifiyarsa sa’arkice “to ai ummi gaskiya ce na fada mudai a family dinmu ba mai irin halinsa wajen mamansa ya gada wlh”Dariya aunty Laila ta sa da cewa”To ai gaskiya ta fad’a ummi halin faruq kusan duk na Habiba ne kawai dai Allah rufa asiri ya mana zabi mafi alkhairi “

ta amsa da amen tare da kallon Irin yanda Ayda Ta hade rai momy ta yi tare da dalla mata harara ta ce”kunga muyi shiru aunty Laila kar ta kullacemu kinsan aka tab’a faruq da uwarsa kamar ranta”Kara shakuwa sosai Ayda tayi da maganar momy tare da gunguni kasa kasa ta mike zata fita ta ce”Zagi na zakiyi ba gunguni ba dawo ba inda zaki”Nan ma bata ce Kala ba sai ummi da ta hade rai ta na kallon momy ta ce “bana son Haka Amera me yasa wai kike mata haka tsawon watanni bakuga juna ba amma kinzo kallon arziki bata isheki ba kuma yanzu kina neman ki hauta da fad’a meye haka ke Ayda wuce ki tafi karki shanya mutum a waje ”

Hawaye na zuba daga idanun momy ta ce”Wlh ummi haushinta nakeji ta rasa Wanda zata so sai faruq mutumin da bamu da makiya sama da mahaifiyarsa sannan don Allah ummi tun ba yanzu ba nake Neman alfarmarki ki daina barin Ayda zanje da faruq ba ma shi ba da kowama don Allah “

“Wannan duk ya wuce amerah bana son tada abunda ya wuce zance kuma bazan hanata ba tunda ba kwadata zamuyi mu ci ba”amma dai ummi…“daga mata hannu tayi ta ce”bana son Jin komai tarenta kuma da faruq idan akwai alkhairi a ciki Allah ya tabbatar idan kuma babu Allah lalata abun”Babu ma wani alkhairi”cewar aunty Aisha “Aunty Laila ta ce”shine kawai muci gaba dayi musu Addua amma gaskiya zuri’ar Habiba Zuri’ar mu ce amma bakayi fatan ka Kara hada zuri’a da ita don Sam halinta ba na dauka jifa yanda fir ta karfi da yaji ta rabamu da D’an uwanmu mu dashi sai nesa nesa ga ta hanasa zama da mata inma Yayi saitayi yanda tayi ta fitar masa ji fa don Allah yaran nan biyu tunda iyayensu suka tafi Dasu yaya ya bar musu su ta rabasu da shi abun gwanin ban tausayi nan suka cigaba da tattaunawarsu irin ta y’an uwa.

Ayda ko jiki a sanyaye Tana Jin zuciyarta ba dadi don sosai momy ta b’ata mata rai ta isa wajen sabon saurayinta Wanda suka sanyawa sugar dady ita da kawayenta don a kalla ya haifeta ba walwala sukayi hirar ganin bata da walwawala ya sanyasa tambayar “lafiya”Tana dafe kanta da ke Sara mata ta ce “kaina ke ciwo”Cike da kulawa irin na dattawannan ya ce”Shikenan badamuwa beauty gobe na zo Allah ya sauwake akwai gajiya tattare dake na lura kije ki huta “Cike da Jin dad’i ta ce”to nagode saida safe”sukayi bankwana koda ta koma suna nan yanda ta barsu ko kallonsu bata yi ba ta haye sama momy ta ce “kungani ko haushinmune taji mun aibantasa “Mufedah ta ce”don Allah momy ki yi hakuri ba ma fa wajen faruq taje ba “Ayman da suna wasa dazu ya ganta ya ce”Wajen wani tsoho ne ma ya zo wajenta ”Dariya mufedah da Noor sukayi Noor ta ce”kaikuma uban sa ido ko”ya tura Baki gaba ya ce”Ai gaskiya ce tsohone wlh yagirmi dadynmu “sai a sannan ummi tayi dariya ta ce”tofa samarin na Ayda hada tsaffi aka fara kulawa “Aunty Laila itama na dariya ta ce”ja ira ta gudu ai da mun zolayeta “aunty Aisha tace “ni wlh dadi na ma daya da ba shi kadai ta nacewa ba ta na kula wasu”Mufedah ta amshe da cewa”aiko Akan kula samarin suke samun matsala ba abunda baiyi mata ba Akan hakan ya daketa zagi hantara ba abunda baya mata amma wlh bata daina kulawa ni namayi mamaki da ummi take Barinta “Murmushi ummi tayi ta ce” ni nasan dalili na kyaleta duk wannan raye rayen kan da take kyaleta nayi kuma Ina da dalili shiyasa kukaga kamar wai ko bana son tsawatar mata ku ai kunsan waceceni Akan tarbiya ta fada ta na kallon su momy”dariya momy tayi ta na kasa da kanta aunty Laila ta ce”gaskiya kam ummi kin sha wahalar Mu kam saidai Allah ya biya ki da gidan aljanna musamman Amera da Aisha “momy ta ce”Kai aunty Laila wlh saidai ki cire kanki amma Ina sane ba wai na manta ba duka ummi tafi Shan wahalarki a kanki fa ummi ta fara duka “jefawa momy pillow aunty Laila tayi ta kauce noor na dariya ta ce”to momy ki bari a bamu labari mana “Hararta aunty Laila tayi ta ce”ohhh wayau so kike ki ji labari kije ki fadawa babanku ya Kara Daure muku kuyi abunda kukaga dama ni tashi ma ki bani waje “Tana dariya ta tashi tana cewa”ai sai na lallaba ummi ta fada mana wlh na je na bawa Daddy Labari ”suna barin wajen aunty laila fuska da damuwa ta kalli ummi ta ce”wlh ummi har yanzu matsalar nan bata warware ba har yanzu Abban su Fatemah bai chanza ba……..✍️

*Share fisabilallah*👍🏾

_*Miss Hajo ce*_🤙🏿

♠️♣️ *MATAR UNCLE* ♣️♠️



```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*

Miss Hajo✍🏾

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*Marubuciyar*

👇🏾

Auren wata Tara

Ni da yaya arman

Khadijatul sabren

Ribar so

Najmat abiy

Mata tace

Komai mukaddari ne

And now

MATAR UNCLE

🅿️……………………….*6*

“Har yanzu abban su Fatimah bai chanza ba kuma wlh duk na fara gajiya gaba d’aya wlh tarbiyar yaran nan a raunane take ummi yanzu haka fa Fatima ban isa inyi mata fad’a ba shisha haka suke sha da kawayensu har su rik’a posting In nayi magana ta ce Flavour ne karshe ma cewa tayi ban Waye ba har yanzu ni daman ba’a san Raina ya fitar da ita karatun nan ba Allah ummi hankalina ba a kwance yake ba zargin yarinyar nan shaye-shaye suke nake na masa magana ya ce sharri zanwa y’arsa flavor ne ba wani Abu ba haka ake nikuma gaba d’aya nasan Dabi’un da take ba na sak lafiyayyu ba ne yanzu haka last week daga Noor tayimun laifi na mareta wlh gaban idonta ya Rama mata banyi aune ba Nima sai saukar Mari naji harna had’a Kaya na zantaho kuma ya dinga lallashina Yanzu haka Haidar nema yake shima ya sangartasa fir shi daman ko Ina suna tare dalilin da ya Hana na taho da shi ma ko ina suna tare kullum suna fad’a da malaman makaranta wlh ummi Ina cikin tashin hankali basaji amma ban isa nayi musu magana ba karshe ma hademun Kai suke ya zuga su su dainamun magana rayuwa zata tafi a haka kike ga ummi Ni matsalar fatima wlh tafi damuna idonta ya bude fiye da yanda bakya tunani a american nan shigar banza ko kamar ba yar Muslma ba Ga Noor itama yana shirin turata itacema mai sauki sauki don Bata son b’acin Raina ita da sauki”

Nauyayyar ajiyar zuciya ummi ta sauke ita kanta lamarin Laila na damunta ta na kwantar da murya ta ce”kici gaba da musu addua Kawai lailah ki Hana idonki bacci ki nemawa yaranki shiriya don Allah shine kawai zai shirya Miiki su da taimakonku to tunda mahaifinsu ya Gaza ku hadu ku tarbiyantar da su sai ki barwa Allah komai tunda yaga kokarin da kike maganar Noor kuma barta a hannuna nasan yanda zan masa admission zan sama mata a makarantar su Ayda ta dawo arewa da karatu karmu yarda ya fitar da ita gaskiya tunda yanajin magana ta nasan hikimar da zan masa shi kuma Haidar Yaro ne ki jasa jiki sosai shakuwarki tafi karfi Akan na uban tunda ke fa tare kuke rayuwa a cikin gida ya kasance ya fi shakuwa dake don sauranma ke kikaja sukafi shakuwa da son uban sbd akwai yaran da idan uban ya nuna son a fili kema nuna musu soyayyar bawai yawan hantara ba to a sannan ne zaki samu ki tarbiyartar dasu Cike da hikima da wayau ita kuma fatima zan Kara kiranta muyi magana ki Kara hakuri rayuwar aure bata taba tafiya 💯 ,”kafin ta numfasa ta dora da cewa “Wlh laila ko wani aure yana da nasa jarabawar saidai na wani yafi na wani duka ne kuma ya Kara dukanki na Baki go ahead ki taho gida Nima na gaji da dukan nan girma kuke kar abun Yabi jiki har diya da jikoki dukda Ana dadewa amma ya Kara dukanki ki taho gida kawai saina dauki mummunan mataki Akan wannan ba a aure da duka ko cin mutunci”!

wata Nauyayyar ajiyar zuciya aunty laila ta sauke ta ce”Insha Allah ummi duk zanyi amfani da abubuwan da kika fadamun nagode Allah ya barmana ke ya ja da ranki don wlh ummi ke Y’ar aljannace Insha Allah ba abunda muka nema muka rasa daga iyaye kinmaye mana gurbin uwa da uba Baki Bari munyi kukan maraici ba kin rikemu tamkar y’ay’anki komai kin mana a rayuwa Allah dai ya biyaki da gidan aljanna”duka sauran suka amsa da amen ummi ta ce”bana son godiyar nan lailah ni ba iya matsayin kanne na daukeku ba Inajinku matsayi biyu tamkar y’ay’an da na Haifa nake jinku a cikin Raina Allah dai ya Kara had’a kawunanmu ya jikan iyayenmu da rahama”

Duk suka amsa da ameeeen “Momy dai shiru tayi don damuwace a ranta Aunty Laila ta kalleta kafin ta maida kallonta ga ummi ta ce”Sai maganar Amera Ummi wlh Wannan Aurenma So take ta kasosa “Kamar wacce aka zabura momy ta kalli Aunty Laila fuska had’e ta ce”Meye haka Aunty Laila don Allah karkiyi wata magana ba na ce miki na gyara ba maganar ta wuce ”Ai wlh ko me zakiyi saidai kiyi amma saina fad’awa Ummi kwata-kwata barrister ba Jin dad’in zama yake da ita ba duk hanyoyin da zata bi ta kuntata masa ya gaji ya saketa shi ta ke wlh bawan Allah nan wuya kawai take basa hakuri ya ke da ita fiye da yanda bakya tsammani ummi shi kuma wai nauyin ya fad’a maki ya ke munyi magana sosai da shi akwai matsala gaskiya “saurin barin wajen Momy tayi baki d’aya ummi ta bita da harara tare da cewa”Idan zaman gidan kikeso ai sai kidawo Gaki ga shi maganganun mutanema kad’ai sun isheki a fara miki irgen Aure da bakisan ciwon kanki ba”Aunty Laila ta ce”ni sai inga wlh amera kamar Han yanzu wancen Marar mutuncin mutumin ne a ranta idan kika Lura gaba d’aya bata son zaman aure kinga haka akayi wancen na Alh mudassir dukda laifinta kad’an ne ni wlh barrister ma nafi tausayawa saboda yanda yake mugun sonta bawan Allahn nan da wani ne tuni ya saallamota gida ko ya k’ara aure”Ummi ta ce”Anya kuwa Laila Mutumin da ko zancensa bata so a tada koda wasa kike ga take so har yanzu a a gaskiya na fi zargin kawai don ta ga ta na da kyau kuma jikinta na da kyau har yanzu ba a cewa ma tayi aure bare har ace ta haihu ta na da budurwar y’a shine yake daukarta take ga inma ta fito wanda ya fisa zata aura nidai shi na fi zargi amma zan Kira barrister idan hidima ta lafa muyi magana”Aunty Laila ta ce “ai bazai fad’a maki komai ba da wahala Nima wlh dakyal saida abun ya kaishi bango ya sameni yake faffad’amun Kamar me tsoranta wai amma don Allah karda ko da wasa na ce shi ya kawo karanta”.ummi ta ce “ai daman bana son ya fad’amun d’in zandai masa nasiha ne cikin hikima na basa hakuri”.

Lokacin su Ayda kuma suna Daki suna ta hira su ukku gaba daya yanda Ayda take bawa noor labarin rayuwar da suke a makaranta sai taji bata da inda take da sha’awa kamar itama ta shiga Makarantar tasu har doki take Cike da zakuwa ta ce”Wlh Nima nan zan dawo da karatu Ina komawa zan fadawa dadyna ya samamun addmission”Yawwa Y’ar gari” Ayda ta fada suna tafawa”Murmushi Mufedah tayi ta ce”amma wlh kika kuskura kika biyewa group din su Ayda ba karatu zakiyi ba don kingansu nan c’o dinsu daga mai biyar sai mai hudu Ayda ce mai sauki ta ke da biyu a semester daya kafin ta gaba”tab to ai ni daman ba kokari gareni ba fa ni bana son karatun daman kawai don a shakata zan shiga” Ayda na zaro ido sai kuma ta sa dariya ta na kallon Mufeda ta ce “tab kinga wacce ta fini ni ba laifi ina D’an son karatun saboda ko banza ance graduate ce ni amma Sam ba na Kaunar karatu ke idan na shiga Ana lectures ji nake kamar na shako malamin da duka Sam na tsani karatu Nima wlh”Mufedah ta ce “wlh karatu na da amfani Ayda da kinji tawa da kun nutsu kun mai da hankalinku shi lokaci ne da shi sannan ke fa Ayda kina da kokari da gangan kike nema ki maida kanki marar kokari kin biyewa shirme kinsan dai baki tsaya kika tab’uka abun azziki ba ba ta yanda zaki fita da result ”

“Noor ta ce”ke da fa gaskiyarta kudai da kukaga zaku iya kuci gaba Allah taya mukam dadi biyu zamuci ga graduate ga ba abimu bashin rayuwa ba ko bamu amshi result ba wani ya sani”

Dariya Ayda ta sa suna kashewa da Noor suna cikin hira Aunty khadija ta shigo da waya a kunnanta ga alamu da mijinta take waya wata takwas baya akayi bikinta y’ar ummi wacce daga ita sai Mufedah shiru duk sukayi da hirar ganinta saida ta katse wayar kafin ta mai da kallonta garesu ta ce”ga alamu munafurci ake hadawa injiwo shewarku ynzu kuma duk kuyi shiru “dariya sukayi Ayda ta ce”ba wani munafurci mrs Habu zuwan yaushe”ta na yatsine fuska ta ce”tun dazu na zo muna tare da twins ne A bedroom dinsu yanzu ma zuwa nayi ku taimakamun y’an k’annena cikinku wata ta soyamun wainar fulawa“gyara kwanciya Ayda tayi Tana rubda ciki bisa pillow ta ce"ni ga shi aunty khadija

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login