Showing 6001 words to 9000 words out of 44977 words

Chapter 3 - MATAR UNCLE BOOK COMPLETE BY MISS HAJO.docx

11 Aug 2025

1442

ce ta wara idanu tare da rugowa da gudu ta na rungume Ayda ta ce.

“oyoyo besty sai lokacin sauran yan matan suka Lura dasu bayan sun zauna Raudat ta na hararar Ayda ta ce “yaushe rabonki da gidanmu Ayda kinfi wata biyu ba ko shekaranjiya saida Abban mu ya gama tambayarki “

ta na zaro ido ta ce”kardai kinmun had’i da shi kince ba na zuwa?jidda mai akalla shekaru 23 ta amshe zancen da cewa”yanzunma dalili yakawota kinsan bata zuwan banza saida dalili”tura Baki gaba tayi ta ce”Kai aunty Jidda haka ma zaki ce zuwa nayi in ganku fa ni ba wani dalili " ta ce "Allah sa"kallon babbar cikinsu da tunda ta kalleta sau d’aya ta mai da hankalinta ga waya ta ce “Aunty Asiya Ina yini “hankalinta har lokacin na ga waya ta ce”lfy ya y’an gidan”Ta ce”suna lafiya”

“Raudat ta je ta kawo musu abun tab’awa ruwa kawai suka sha Inda Jawahid ke danna wayarta saukowar mahaifiyarsu ce ya sanya gaban Ayda faduwa.

cin karo da fuskar Ayda ya sanya Umma tayi kicin kicin da fuska kamar an aiko mata da Sakon ranar mutuwarta ta na zama tare da had’e rai.

Ayda gabanta na faduwa ta ce”Umma Ina yini”ba tare da ta kalleta ba tace”lafiya “Shiru Ayda tayi a ranta Ta na tunanin ta ya zata samu ta hadu da yaya faruq ga Umma ta sauko sanin Halin umma ba jituwa suke da Ayda ba ya sanya Raudat jansu dakinta sai a sannan hankalin Ayda ya kwanta ba bata lokaci suna shiga cikin sauri ta ce”ta ce”sis don Allah taimakamun zakiyi yaya faruq nake son gani”Dariya raudat ta yi ta ce

”wlh daman a Raina na San wajen sa kikazo anyi Halin da aka Saba ko”Harara wasa tayi mata ta ce”nidai ba ruwanki kawai ya za ayi na Gansa na San da duk magrib ya na gida ba inda yake zuwa shiyasa na zo”Kin ko yi sa’a yau ya na gida wlh kwana biyu ba ya fita sai zaman daki ayi sallah sai muje ko?

Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke ta ce”Eh amma bana son Umma ta gani kuma kinga ga shi ya na

Palour kuma dole sai ta palour zanbi “Ke Umma Ana magrib ta ke shigewa ciki bata zaman palour sosai idan Abba yana nan”



Ajiyar zuciya Ayda ta sauke Ana gama magrib kamar yanda Raudat ta fada duk sauran yayin nasu ma basa nan haka Umma wannan damar Ayda ta samu ta nufi dakin faruq kusan cin karo sukayi zai fito zata shiga wani irin hade fuska Yayi tamau tare da cewa”

“Ubanme ya kawoki waje na ko kin dawo ne ki Kara chusamun sauran bakincikin da Baki gama ba”Lokaci guda hawaye masu dumi suka zubo mata tare da saurin girgiza Kai ta ce”don Allah ka yi hakuri yaya faruq magana zamuyi”Kofa ya nuna mata yayinda zuciyarta ta kafe ta ki tafiya sai ma karasa shigewa dakin tayi tare da zama gefen gado “kinsan Umma ta zo ta sameki a nan Fad’a zatayi ki tashi ki tafi na ce”Ya fad’a a zafafe”Cike da taurin rai ta ce “ni fa ba inda zanje ”wlh ko ki tafi ko na nakada maki shegen duka munafuka maciya amana idanma wayarki kikazo amsa kinyi zuwan banza don keda ita har abada mayaudariya Allah ya Toni asirinki Ashe ba karamun munafurtata kike ba Samarin da suka dinga kiranki sunfi talatin kuma d’aya bayan d’aya na dauka na zazzagesu tare da shaida musu ni ne ajalinsu na Kara ganinsu da ke sannan na karya sim dinki dan nasan wayarce ta kawoki tashi ki ba ni waje ni “

Batayi mamaki ba kuma tasan daman hakan zai faru don tasan dole za akirata kuma dole zai karya sim dinta amma ita kam wlh saiya bata wayarta tunda ba shi ya saya mata ba duka 2 months da sayar wayar zai amshe mata”cikin kwantar da murya ta ce”to yaya faruq ka yi hakuri mana tunda har gida na biyo na Baka hakuri ba shikenan ba tunda ka dau mataki na maka alkawari bazan Kara kula kowa ba amma don Allah kayi hakuri ka daina fushi da ni kasan bazan jure ba please ta fada hawaye na zuba daga idanuwanta “

Jikin faruq ne Yayi sanyi Tare da dawowa ya Zauna ya ce”kinsan duk wannan abun da nake saboda sonki na ke Ayda don Allah ki mun alkawari kin daina kula kowa “gyada Kai tayi ta ce”na daina yaya faruq”Goge hawayen to”gogewa tayi tare da kirkirar murmushi ta ce ka hakura”gyada mata Kai Yayi ya na murmushi tare da kama hannunta ya ce “na yi kewarki “Cikin narkar da murya ta ce”Na fika azabtuwa da kewarka yaya faruq don Allah ka daina fushi da ni wlh Ina cutuwa da yawa”Ya na murza tafin hannunta ya ce” na daina”yanzu muje na maidake gida dare na yi kar umma ta samemu a nan “

“gyada kai tayi tare da mikewa ya bita murnar sun shirya Sam ya mantar da Ayda tare da jawahid sukazo Kai tsaye motarsa ya dauka tare da mayar da ita gida sunjima a cikin mota suna hira har karfe Goma bai mata maganar wayar ba itama bata masa ba tasan zai maido mata idan ta lallabasa ta na Shirin fita ya janyo hannunta ya na hade fuska ya nuna mata kumcinsa,

Ta gane me yake nufi hakan ya sa ta yi kasa da kanta gabanta na faduwa Allah ya sani bata kaunar ire-iren abubuwan nan da yaya faruq ke mata “hade fuska tamau Yayi tare da cewa”bazakiyi abunda na sakaki ba”girgiza Kai tayi kamar zatayi kuka ta ce”yay..”da Allah Yiwa mutane shiru fita”ba musu ta fita ta na tura Baki gaba a ranta ta ce “mutum sai masifa “

“daga Ina kike har karfe goma Ayda Bance 8 tayiwa kowa a gida ba duk inda yaje “ummi Ina haraba fa tun 8 din”Kedawa?Yaya Faruq”Sau nawa zan hanaki zan ce a mota Ayda bakyaji ko?kodan kinga Ina wasa dake”ummi yaya faruq ne fa”ta fada a shagwabe”Faruq d’in to daga yau karna kuma ganin kun shige motar nan da ba Aganin komai idan bazakuyi zancen a harabar waje ba ai ga palour nan kinji na fada maki?Gyada Kai tayi ta ce”Toh ummi”

tare da zama gefen Mufedah da ke Galla mata harara ta ce”aramun wayarki in Kira jawahid “don sai sannan ta tuna Ta barota a cha shaf ta manta “Bazan ara ba tunda bikon da kikaje baiyi amfani ba “kar alasa ki bada d’in”

ta fada ta na hayewa sama tare da Aron ta aunty hasana ta Kira jawahid ta na Jin muryarta ta hau balbaleta da masifa”ai wlh kin Kara cewa na rakaki watau kinma mayar Dani shashasha soyayya ta debeki kawai kika tafi kika barni “Dariya Ayda tayi ta ce”sorry besty ai dai yanzu kin koma gida”ta ce”bansaniba “dakyal ta shawo kanta ta hakura.

Bikin hasana da husaina na ta karatowa saura kwana goma Wanda busy duk yayiwa ummi yawa zaune take a bedroom dinta ta na waya kallo d’aya zakayi mata kaga tsantsar damuwa a cikin fuskarta kwalla na zuba daga idanuwanta ta cigaba da cewa.

”wannan ya nuna mun kenan ba da kowa kake fushi ba Adnan da ni kake fushi watau har yanzu ba ka manta da abunda ya Riga ya wuce ba?ba wata magana da zaka fadamun na Aminta da ita Adnan na lallab’aka na yi maka nasihar duk wani lallashi nayi maka amma ka ki saurarona shikenan kar kazo Insha Allah wannan shine karo na karshe da zan gama rokonka Akan kadawo gareni shekaru goma kasan ko irin halin bakin cikin da kuncin da nake ciki a dalilin rashinka rayuwa nake amma ba yanda nake so kullum zuciyata makale take da tunaninka bani da walwala kamar ko wani D’an adam duk don saboda Kai Adnan kodan Baka haihu ba bakasan halin kuncin da iyaye suke shiga ba idan y’ay’ayensu suka guje su “

saida ta ja numfashi kafin ta goge sabbin hawayen da suka zubar mata “zatayi magana maganarsa ta katse na ta tsayawa tayi tana saurarensa kafin ta sauke Nauyayyar ajiyar lokaci guda murmushi ya subce mata Cike da mamaki ta ce “da gaske sati mai zuwa kamar haka Ina tare da Kai”shiru tayi alamun sauraro kafin ta furta kalmar “Alhamdulillah alhamdulillah Allah nagode maka Allah Yayi maka albarka D’ana Allah ya dawomun dakai lafiya cikin aminci Kai amma najima banji abunda ya sanyani farinciki kamar haka ba Allah Yayi maka albarka “

Farincikin da ummi ta shiga kasa musaltuwa Yayi da hanzari ta katse wayar tare da saukowa palour inda ta samu yaran nata suna ta harkokinsu Cike da doki ta ce”Albishirunku!

Har doki da murna suke wajen cewa “ummi goro”Saida ta sauke ajiyar zuciya kafin ta saki murmushi ta ce “Adduar da muka dade munayi tsawon shekaru Allah ya amsa Ranar Juma’a mai zuwa idan Allah ya bamu aron rayuwa Adnan zai dawo kasarnan “

Hasana da husaina ce sukayi saurin zaro idanu tare da cewa”Don Allah Ammi da gaske ba wasa ba!

“Na taba muku irin wannan wasan daman bai taba fadamun cewa zai zo ba duk lallashin da nake masa kusan kullum sai a wannan Karon kuma tabbas din zaizo saboda nasan Adnan ba ya magana Biyu Kai alhamdulillah Allah nagode maka”

Cike da doki su da suka sanshi suka ce “Alhamdulillah Allah mungode maka Allah dawo dashi lafiya Amma ummi bazaki Bari ya Kara komawa ba idan yadawo gaskiya munyi kewar uncle da yawa?

cewar aunty husaina “Haba husaina fad’i ma ai batawa Insha Allah ya dawo kasar nan shi da barinta sai Allah bazan Kara yarda ya tafi ba”

“Ummi wai Uncle ne zai dawo”Farinciki ya kasa batuwa a fuskar ummi ta ce”Shi Ayda uncle dinku dukda nasan ba lallai ki tuna sa ba tunda shekara goma ba wasa ba ce saboda lokacin Baku da wayau ke da Mufedah”.

Shiru tayi ta na son tuna kamannin uncle d’in nata amma akwai abu biyu da ta kasa mantawa game dashi a rayuwarta lokacin da ya kaita primary school bayan gama nursery dinta ya sauya mata makaranta inda wajen saka suna headmaster ya ce”ya sunanta Kai tsaye ya ce”Maryam muhammad Ali “Sai kuma lokacin tafiyarsa wanda ya kasa barin memory dinta kuka ta ke sosai a jikinsa gab da tashin jirginsu wanda har sik’ewa take don kuka ya yi dai ta lallashinta da maganganu amma ta kasa rike maganganu sai hoto da ya daukesu a wayarsa su kadai ta rike amma gaba daya ta manta komai game dashi hatta kamanninsa “

“yanzu ko zan Kira aminiyarsa na mata babban albishir “maganar ummi ta katse mata tunaninta a yayinda ummi ta doka kira

saida ta katse kafin ta kuma Kira jin ta katse ta kira ne ya sanyata saurin cewa”albishirinki Amera”Daga bangaren ta amsa da “goro Ummi”Amininki ya amince rana ita yau zaidawo a cewarsa zai zo biki nasan hada kokarinki ya amince zaizo yanzu yaushe za ki taho ke?daga bangaren ta ce”ummi ai yanzu muka gama waya da shi yake fadamun kinsan ummi zance bayan ke babu wanda ya kaini farinciki da dawowar Adnan”

Da murmushi a fuskar ummi ta ce”ai nasani Amera rabi duk kokarinki ne Allah dai ya muku albarka yanzu yaushe zaki taho daga Lagos din yakamata ace kunxo da wuri an shishshirya abubuwa biki sai karatowa yake duk kunki zuwa Abubuwa sunyimun Cha”Daga Chan bangaren kamar zatayi kuka ta ce”Ummi shi ne nake ta kokarin ya barni na taho ko saura kwana goma ne yakiya don Allah ummi ko magana zaki masa”A a ki lallabasadin dai da kanki ba sai na sa Baki ba sai ku taho tare da Lailah”

“to Insha Allah kafin dai Friday din nasan na zo”ta ce”Allah ya sa agaida mun da Barrister “ta ce “zai ji ummi”Ayda na sauraronsu a ranta ta na Jin haushin nemanta da momyn takiyi kwana nawa bata da waya ko ta nemeta ita ma ko shiyasa taki nemanta,…….✍🏾

*Juma’at kharem Allah sadamu da dukkan Albakatun dake cikin ranar*🙏

_*Miss Hajo ce*_🤙🏿



♠️♣️ *MATAR UNCLE*♣️♠️



```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*

Miss Hajo✍🏾

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*Marubuciyar*

👇🏾

Auren wata Tara

Ni da yaya arman

Khadijatul sabren

Ribar so

Najmat abiy

Mata tace

Komai mukaddari ne

And now

MATAR UNCLE

🅿️……………………….*5*

A ranta ta na Jin haushin me ya sa momyn ba ta neme ta ba itama kuwa shi yasa tak’i nemanta bayan komawarsu d’aki kallon Mufedah da ke gefent ta yi tare da cewa”Don Allah aramun wayarki”nuna mata wayar a side drawer ta yi ta dauka daman ta haddace number Waziri a take ta karanto tare da danna masa Kira Jin muryarta ta na Jin irin Nauyayyar ajiyar zuciyar da ya sauke kafin ya ce.

”babe me ya sa zakimun haka kinsan an sanya maki aure kika dinga wahalar da zuciyata”Kenan an sanya mata aure Yaya faruq ya ce”ka na garin ?iya abunda ta iya cewa kenan”Eh ki bani amsa da gaske ne an kusa bikinki ko kuma?kamar ya na gabanta ta girgiza Kai ta ce”ba gaskiya ba ne ya fada maka ne don ka rabu da ni”To shid’in waye “D’an uwa na ne”?Kuma Saurayinki ko?Ta ce”Eh”ya ce”hmm Toh mu zuba Allah ya ba me Rabo Sa’a Yayi tunanin barazanar sa zata tsoratani “

Ce“yanzu dai ba wannan ba gobe mu had’u a miet Corner Karfe hud’u ba waya hannuna”ya ce”Allah ya kaimu”washegarin yanda ta fada haka akayi daga school ta wuce suka hadu da waziri Wanda ta Kara tabbatar masa daba haka ba ne”bai kamata ba ace Baki da waya babe ba girman ki ba ne muje a sama maki ko 15 ce”cewar waziri

”ta yi saurin girgiza Kai ta na hade fuska ta ce”idan Ina bukatar ka sayamun na fad’a maka ai ynzu dai ba na bukata “Toh me za akawo maki ki ci yau dai muna tare har Magrib tunda kinga wajen nan ya na da sirri “ta ce no 6 zan koma “yana sakar mata murmushi ya ce”Haba Babe Toh saki ran mana An had’e fuska dukda a kowani yanayi cikin kyau kike amma kinfi kyau da fara’a “Bata saki fuskar ba sai k’ara hade fuska ta yi ta ce”shawarma bread da tea kawai zanci”ya ce yau har naman baza aci ba?ta gyada masa Kai “ya mike zai fita ta ce “aramun wayarka “ya Mika mata ya na barin wajen “cikin sauri ta Danna kiran wata number da hanzari bayan dauka ta ce “Vappie Ayda ce gobe 6:00pm mu had’u a S cape Banda waya hannuna wannan ba wayata ba ce karka kira”Ya ce “Allah kaimu darling kamar kinsan nayi kewarki da yawa”tayi saurin katsewa ganin tahowar Waziri tare da blocking number ta goge“Washegari yanda ta fada lokacin suka had’u da vappie shima ta warware masa maganar Faruq don shi ya tsorata sosai”kusan 50k ya kashe musu a ciye ciye daman shine dalilinta na kula samari kullum a ciki kowa da ranar fidda ita hauka ta ke ta Bari yaya faruq ya maka sakakka duk ya kore mata su shima ya ce zai saya mata waya ta ce bata so! A haka duk ta dawo da wasu daga cikin samarinta .





Ana sauran sati guda biki duk sauran y’an uwan ummi da wasu daga cikin Y’ay’ayen y’an uwanta suka hallara lokacin da sukazo su Ayda suna yawo da kawayenta ko sch ma ba su samu damar zuwa ba sai gab da magrib ta nufo gida da driver don kamar a alkakai takejin deriver nan da aka hadata dashi,nata na musamman domin ummi ta ce bazata basu mota ba hakan ya sa Ayda ta ce ita saidai a ware mata driver ta daban ummi tayi mata yanda take so d’in ganin da farko ta so driver su hada Baki ya dinga kaita inda ta ke so zata Kara masa albashi Wanda ya shaida mata bazaiyi hakan ba bazaici amanar uwar d’akinsa ba iya makaranta da inda ummi ta umarta kad’ai zai dinga kaita hakan yasa ta ke dabara ya na kaita makaranta daga Chan ta wuce inda ta ke so domin ummi na da time table dinsu ta san lokacin zuwan su da tasowarsu haka driver shima ya na time table din ummi ta basa dalililin da yasa saidai ta hakura da lectures don wani Karin sai tayi fin one week ma ba tare da tayi attending lectures ko d’aya ba”.

Da sallama ta shigo palourn turus tayi cin karo da manyan bakin da ke garesu kusan Cike palourn.

ummi sai farinciki take karasawa palourn tayi Aunty Laila ce ta fara mata Oyoyo “Hugging din ta Ayda tayi da dan murmushi a fuskarta ta ce”Aunty irin suppressed haka ban San yau zakuzo ba ai da bazanje school ba”Da murmushin zallar Kaunar Ayda a ranta ta ce”ai suprised din Ummi mukayi daughter shiyasa”

d’iyarta da zatayi kusan sa’anni da ita ta kalla tare da harararta ta ce”Baki gaisheni”Itama hararar ta mayar mata ta ce”Allah kiyaye kinma Raina ni”kaiii yaushe idon ki Yayi tsauri yarinyar nan 7months fa na Baki “Dariya

Tasa tare da cewa “Toh meye a 7months Kalli fa wlh yanzu haka nafiki girma “”

Ayda na maida kallonta ga momy da tayi fuska ta ce”kibar doya ce rainon Lagos amma ba don haka ba da baxaki hadani da ke ba “

ta mai da kallonta ga Aunty Aishaa da ke saukowa da gudu ta ruga tare da rungume ta ta ce”Wayyo dadi aunty hadake saukar yaushe”da fara a fuskarta ta ce”duka yau muka sauka mukayi supresed dinku “

“Kai amma kun kyauta wlh aunty Ina mutuniyar Farhat”Ta na hannun Ayman sunfita sai a sannan Ayda ta kalli momy da suke da hira da ummi kamar ta shige cikinta kanta na bisa kafadarta ta ce

”Ina yini momy anzo lafiya “Alhmdulillah ya makaranta”Ta amsa cikin ko in kula”ta ce”Alhmdulillah” ”Toh Allah huta gajiya”ta fada ta na mikewa tare

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login