Showing 15001 words to 18000 words out of 44977 words

Chapter 6 - MATAR UNCLE BOOK COMPLETE BY MISS HAJO.docx

11 Aug 2025

1452

```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*

Miss Hajo✍🏾

*Marubuciyar*

👇🏾

Auren wata Tara

Ni da yaya arman

Khadijatul sabren

Ribar so

Najmat abiy

Mata tace

Komai mukaddari ne

And now

MATAR UNCLE

🅿️……………………….*8*

A hankali ya juya kallonsa gareta bai kalli fuskarta duka ba ya dai ga gefen fuskarta sosai Yayi mamakin girman nata a ransa yana tunana randa aka haifeta ,

”Amera mu je ko”cewar Adnan ganin sunyi tsaitsaye Hararar wasa momy tayi masa ta ce”Aunty Amera dai”D’an murmushin da bama zaka ce Yayi ba ya yi kafin ya bi bayan su ummi don har sunyi gaba yana kallon yanda momy ta rike hannunsa gam ya ce”To ki sakeni mana disturber ko akace maki guduwa zanyi”sunannan bazai fita a bakinka ba Adnan ai idan kaga na sakeka to mota na saka ka karka kuma guduwa nemanka ya Kara mana wahala “

saida zai shiga mota sa’annan Ayda ta kare masa kallo Idanunta a kansa ba ko kiftawa ganin yanda momy ke farinciki kamar anyi mata albishiri da gidan aljanna ya sanyata Tabe Baki ta ce”Wannan murnar da take a kansa ai saita kusa kashe mutum.

Motar da su Mufedah suka zo ta bi driver ya ja suka wuce gida

Kasantuwar baya gudu Abdallah da ya dauki su ummi ya fi gudu ya sanya suka riga su zuwa don lokacin da su Ayda suka iso tuni har sun isa palour Jiki sanyaye Ayda ta shiga palourn kamar wacce kwai ya fashewa a ciki bata kalli ko mutanen da ke palourn ba ta nufi hanyar wucewa Sama.

“dawo nan Ayda”Muryar ummi ta katseta tare da cewa “Fushin ne har yanzu ba a huce ba Haba autar ummi zo zauna naji meye”ummi ta fada ta na kamo hannunta tare da zaunar da ita gefen ta sai a sannan Adnan ya dago cikin y’an sakwanni ya kare mata kallo kafin ya maida kallonsa ga noor da mufeda da ke gaishesa ya ce”Alhamdulillah ya school”suka ce “Lafiya qlau”ya ce”Masha Allah yana kallon Aunty Aisha da tayi fuska ya ce”Maman Iman Ina yini”murmushin yake tayi ta ce”Ina yini uncle anzo lafiya”domin ba da ita aka tarbosa ba ya ce”Alhmdulillah ya me gidan”ta ce “yana lafiya”nan su hasana da husaina ma suka gaishesa ya amsa da tambayarsu ya hidima Aisha ta fara barin d’akin ummi ta bita da kallo Allah sarki in Banda Adnan ya gujewa Auren Aisha da fa yanzu wad’annan yaran nata duk nasa ne dondai komai na Allah ne shima Allah zab’a masa mafi alkhairi ta Lura har yanzu da tabon Adnan a zuciyar Aisha don ta so shi kamar ranta ya watsa musu k’asa a ido Karshe ma ta na zargin hada gudun Auren ya sa yabar k’asar.

maida kallonshi ga momy da ke ta jere jeren kuloli ya yi a hankali kamar baya motsa labbansa ya ce”

“Wazai cinye maki kayan nan kinfa San cikina”Momy na zuba masa dambun shinkafar da yaji vegetables don tasan shine favorite food dinsa ta ce “Ai ko Baka isa ba komai na nan sai kaci”langwabar da Kai Yayi kamar yaro ya ce”To ai sai ki saka inyi jinya”Koma me zaka ce saikaci abincin nan ko na maka d’ure”

Tuba nake babbar Yaya amma sai na fara zuwa na watsa ruwa”Kai dai ka ce ka na nan da halin nan naka na kin cin abinci gaban mutane muje part din naka to na Kai maka Chan”ta fada ta na daukar kular tare da mikewa,idon noor ko D’aukewa bayayi Akan Adnan don ta Lura miskiline na karshe gaisuwar da sukayi mashi ma a dakile ya amsa “.

”ummi tayi murmushi Aunty Laila ta ce “Ai dole muja baya mukam Amera da Adnan ai sai Allah “mami ta ce”Bakiga ya maidamu fanko ba ba tamu yake ba”sai a sannan ya kallesu ya ce”sorry Mamy aunty laila tuba nake “

Ayda na Jin muryarsa ta tabe baki ta ce”kamar mace ko magana ma kamar bayaso”Tana tura Baki gaba Tana binsu da kallo har suka haye sama kafin ta maida kallonta ga ummi kamar zatayi kuka ta ce.

”ummi har fa wayata ta fasa”rabu da ita ki lallabata har ta tafi wayar nan dai sai a hakura da ita tunda an tisota gaba faruq ya amshe satittika tadawo an kuma fasawa na saya maki wata je ki ku fara shirinku naji sunce anjima zakuyi wani event a gidan Khadija na mata ko?gyada Kai tayi jiki sanyaye ta mike ta nufi dakinsu ko kallonsu su Mufeda dake musu magana batayi ba

Koda ta koma daki gado ta fada tare da sanya marayan kukan da bata yi ba kawai yau ta tabbatar momy bata sonta ta tsaneta wani irin zafi take ji a ranta ga faruq tasan ya shaku zai dauka da gangan ta kashe masa waya a fili ta furta “na gaji koma me zakamun kayimun ka kashe ni ma na huta “

kuka take sosai sosai ta bawa Noor da Mufedah tausayi Cike da damuwa ita da mufedah suka shiga lallashinta tare da rungumeta dakyal suka samu tayi shiru cikin kuka ta ce”momy ta tsaneni mufedah bansan laifin me nayi mata ba “

Noor na share mata hawaye ta ce”ba tsanarki momy tayi ba Ayda Ba ta kaunar taren ki da yaya faruq ne saboda wani dalilinsu da ya had’asu da mahaifiyarsa sannan da irin cin zalin da yake maki.

”to Ina ruwan mahaifiyarsa da shi ai ko Allah ba ya Kama bawa da laifin da ba nasa ba sannan yaya faruq fa jinintane mafi kusa kuma Ina sonsa sosai itama ta sani me yasa bazatayimun uzuri ba sannan ba ruwan kowa da abunda yakemun a haka naji na gani “

Numfashi Noor ta ja kafin ta ce”kiyi hakuri ki dinga addua zamu tayaki yanzu ki bar kukan nan muje mu tafi gidan aunty khadija mu soma Shirin mu”dakyal suka lallasheta suka tafi da cewa tayi bazata je ba

Sosai night party din nasu Yayi kyau kuma ya tsaru komai anyi gwanin burgewa da tsarin tarbiya sunyi abunsu cikin class

A gidan aunty khadija suka kwana duk yanda Ayda ta dinga sauya number ta na kiran wayar faruq k’in dauka Yayi Karshe ma kashe wayarsa ya yi gaba d’aya Wanda sosai ta k’ara shiga damuwa.

Washegari misalin karfe sha biyu na rana d’umbin al’umma suka shaida daurin Auren Hasana da husaina tare da angwayensu Wanda sai a sannan mutane suka gaggaisa da Adnan Wanda daga daurin Auren Yayi sauri ya zame gidan gonarsa don shi mutum ne da a rayuwarsa baya son hayaniya,

sosai Yayi kewar gidan gonar nasa inda ya tarar da dukkan abunda ya Bari ya hayyafa sosai ya tabbatar da ummi na kula da dabbobin nasa lumshe ido Yayi ya na shafa kan kyakyawan police dog din nasa Yayi mamaki da har zuwa lokacin nan da bai manta sa ba don ya na zuwa ya nufo sa.

waje waje saida yaje ya duba

lambun gidan gonar ya tare inda aka ciro masa kayan itatuwa Cike da nishadi da annashuwa yake ci har wani lumshe ido ya ke don sosai yake Jin wata nutsuwa na Kara ratsa sa.

Daidai lokacin kiran momy ya shigo wayarsa bata Bari Yayi magana ba ta ce Ina kaje wai Adnan tun dazu Ana nemanka”ina gidan Gona”?ya bata amsa

”Haba Adnan Ana biki ka tafi wani waje ga shi kowa na son ganinka ai yakamata ka zo ka gaggaisa da y’an uwa mutanen Daura ma sai tambayarka su ke”

“Amera ni fa kinsan bana son hayaniya Ina hutawa anjima ai zan dawo”ba ason ran momy ba taki jansa da magana tasan ba dawowa zaiyi ba ta ce”to shikenan don Allah kar kayi dare take care”Yana lumshe ido ya ce”Toh Mom”murmushi tayi daga bangaren tace “Allah maka albarka “Y’ar dariya Yayi marar sauti tare da cewa”Baki daina son girma.

Bangaren su Ayda saida suka raka kowacce amarya gidajenta masha allah komai Yayi yanda ake so tundaga kan gidajen da kuma kayan da aka zuba ko makiyi yasan ba makusa saidai fatan zama lfy bayan gama Nasihohin iyaye suka tafi suka barsu da yaran “

Ayda da ke zance da sabon saurayinta a gidan husaina tun dazu Noor da ke nufowa wajen ta kalla bayan sun gaisa da shi ta kalli Ayda ta ce”momyna ta kira tace mudawo gida mu barta da kawayenta su zasuyi sayan Baki”

Cike da zakuwa saurayin ya ce “to muje na saukeku”kallon Noor Ayda tayi ta ce”yiwa Mufeda magana to”

A motar sabon saurayin Ayda suka koma gida Wanda su Noor suka wuce gida ita kuma ta tsaya suna ci gaba da zance Wanda duk hirar saurayince bata biyesa daidai lokacin dannowar motar Adnan gidan ganin irin hasken da ya dallesu dashi wanda ba alamun kashewa ne ya sanyata sallamar saurayin ta na Jan tsaki

Ko Waye zai dalleta haka don rainin hankali





palourn Cike ta sameshi da dangi tundaga dangin iyayen su ummi da kakanni masha Allah mutanen na da zumunci Ayda ganin suna ta zolayantan da suka saba ya sanyata zamewa ta koma ciki

kamar yanda ta yi jiya yau ma kira yakai biyar tayiwa faruq a wayar noor bai dauka ba sai taji duk kunci ya mamaye zuciyarta

Cikin kwana biyu kowa dangi na nesa da na kusa duk sun koma mami ma da Abdallah sun dauki hanyar Kaduna haka aunty Aisha itama ta bi mijinta da yazo daurin aure bai koma ba hakan yasa Washegari ta bisa suka wuce kano inda take aure.

Bak’i dai ya rage daga momy sai aunty laila da suke Auren gari daya estate d’aya sune ma zasu k’ara kwana biyu.

Zaune suke a palour suna ta hira su hud’u Mufedah,Aunty Khadija sai noor Ayda dai hankalinta duk ba jikinta yake ba ya na wajen faruq ganin shigowar momy da kuloli a hannunta ne ya sanya suka tsagaita kallon Ayda tayi ba yabo ba fallasa ta ce”amshi ki kaiwa uncle d’inku part dinsa “

kallon momy tayi da mamaki duk su hudu sai ita zata zab’a ta Kai masa”Momy kamar tasan tunanin me take ta ce”Eh saboda ke kadaice mai tsaurin idon da bakije kin gaishe sa ba kin masa Sannu da zuwa tun zuwan sa shiyasa na Baki ki Kai masa daga nan ki gaishesa “

A hankali ta amsa jiki sanyaye tayi waje ba tare da amsawa momyn ba

Ta kai minti biyar bakin kofar ta kasa shiga ta kasa knoking gabanta takeji na faduwa saida ta rumtse ido kafin ta fara knoking Jin anbata umarnin shigowane ya sanyata tura kofar a hankali cikin siririyar zazzakar muryarta tayi sallama “wa ailakumussalam”ya fad’a tamkar ba shi Yayi maganar ba don gaba daya hankalinsa na kan laptop.

lumshe ido tayi Jin wani irin sanyayyen kamshi da ya hadu da ac na tashi a palourn “kai gaskiya kamshi rahama ne”

Ta fad’a a cikin zuciyarta kamar gunki haka taci gaba da karewa dakin kallo komai na dakin off white ne fes fes tamkar ba a taba shiga dakinba babu alamar kazanta ko daud’a da zakace ta taba samun mahallin zama sosai tsarin kayan dakin da komai suka burgeta musamman lather kujerun da sukayi matukar karshen haduwa tamkar d’akin shugaban k’asa.

Gyaran muryar da akayi ne ya dawo da ita hayyacinta don sosai ta lula wata duniyar ta daban sai a sannan ta kallesa sanye yake cikin kananun kaya jiens da t-shirt sai sirirn farin glass da ya sanya wanda kana ganin kwayar idanunsa tura baki gaba tayi a ranta ta ce”Don yana da kyau shine yake girman Kai Alhalin ko ni da ake cewa Ina dakyau amma bana irin haka”

“ta fada kasa kasa yanda ba mai ji karo na farko da ya D’ago ya kalleta cikin y’an seconds ya k’arewa street gown din jikinta kallo sosai red atamfar ta amsheta tayi mata kyau normal daurin D’an kwali ne kanta ba gyale tab’e baki Yayi ya na kauda Kai ya ce.

”baki iya zama ba”A ranta ta maimaita maganar saidai kwarjinin da Yayi mata ya sanyata kasa cewa komai ta zauna kasa bisa lausassan carpet din dake malale a tsakiyar palourn kasantuwar suna facing din juna ya sanyata kallonsa kamar mai shirin yin kuka ta ce”Ina yini uncle anzo lafiya”

yana lumke laptop din dake gabansa ya kalleta tare da cewa “ban anshi gaisuwar nan ba tunda ba daga zuciyarki ta fito ba”Toh uncle daga Ina ta fito”daga bakin amerah mana”Kasa tayi da kanta Tana tura Baki kafin ta dago ta na narkar da fuska kamar zatayi kuka ta ce”daman Ina son zuwa na zo na gaishe ka Hidimar biki ta Hana”Saida ta kusan minti guda da maganar har ta cire rai da zai bata amsa ya ce”………..✍️

_*Miss Hajo ce_*🤙🏿

♠️♣️ *MATAR UNCLE* ♣️♠️



```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*

Miss Hajo✍🏾

*Marubuciyar*

👇🏾

Auren wata Tara

Ni da yaya arman

Khadijatul sabren

Ribar so

Najmat abiy

Mata tace

Komai mukaddari ne

And now

MATAR UNCLE

🅿️……………………….*9*

Har ta cire rai da zai bata amsa sai kuma ta tsinkayi muryarsa da cewa”ya karatu”kanta k’asa ta ce”Alhamdulillah “j s s nawa kike?tana shagwabe fuska ta ce”

“uncle js s kuma level 1 fa nake zan jona two” ya D’an wara idanu irin mamakin nan ya ce”

“serious “murmushi tayi da ta lotsar da dimple dinta guda biyu tare da bayyanar da wushiryarta ta ce”Allah uncle “ya ce”Masha Allah Allah ya bada sa’ar karatu”

Ta amsa da amen tare da d’an tura kulolin kusa dashi ta ce”momy ta ce”na kawo maka”Rankwafowa yayi wanda har sunajin numfashin juna wani irin lumshe ido Ayda tayi Jin wani daddad’an kamshin dake fita daga jikinsa

komawa Yayi ya zauna bayan ya maida kulolin gabansa yana daddagawa shinkafa da Miya ce da ta sha green beans da carrot a cikinsa da dafaffen dankalin turawa daga sama gefe miyar yankakkun kayan miya ce da ta sha kifin geangwani sai kamshi take gefe kuma hadadden cowslow ne murmushi yayi yana maidawa ya rufe a ransa yana jinjina iya girki na amerah don yasan girkintane kuma course din umminsu ne”

maida kallonsa ga Ayda yayi da a zuciyarta ta ke Allahsa karya sallameta don kamshin dakin ba karamin dadi yake yi mata ba

“Ko hira zaki tayani kikayi zaune”Girgiza Kai ta yi ta ce”a a “to tashi ki tafi”Dagowa tayi ta kallesa idanunsu suka sartse cikin na juna shi ya fara janye nasa idanun ya k’ara cewa”Ki tashi ki tafi kar ummi ta nemeki “mik’ewa ta yi ba tare da ta tanka masa ba tabar d’akin ya bita da kallon mamaki har yanzu mamakin girman yarinyar yake kafin ya shingida jikin kujera tare da Lumshe ido ya tafi wani tunanin na daban.

”koda ta isa part dinsu samun ummi tayi tare da aunty Laila gefen ummi ta zauna ta na dora kanta bisa kafadarta ta ce”ummi wani saurayina ya ce zai kawomun waya don Allah ki yarda na karba”lokaci guda ummi ta hade rai tamau ta ce”ban yarda ba karki sake ki amsa kuma naji labarin makammancin haka ranki zaiyi mugun b’aci zan saya maki cikin satin nan Insha Allah kowace iri kike so nayi busy ne da yawa shiyasa ”

”Toh ummi nagode”ta fad’a ta na mikewa tare da barin bedroom din gaba d’aya dakinsu ta koma inda ta samu su Mufedah na ta fira kallonta Noor ta yi ta ce,

“har kin dawo”Gyada musu Kai tayi ta na kwanciya jiki sanyaye mufedah ce ta ce “me kuma ya sameki kikayi sanyi haka“Ita dai Ayda ba ta Kara ce musu k’ala ba ta juya ta kwanta Tana ta shak’ar kamshin turaren d’akin uncle Dan ita kanta da ta shiga jikinta kamshin yake”

Noor ta ce”wlh na so ace ni Aunty Amera ta aika na Kai masa Allah Uncle ba karamun haduwa ya yi ba bakison yanda lokaci guda na kamu ba wlh”

ta fada ta na kallon mufe ta ce”wlh noor kin ishemu da zancen uncle saikace sa’anki ke ko kunya ma bakya ji”

Ayda da batayi niyyar saka musu Baki ba ta sanya dariya tare da cewa”iska na wahalar da me Kayan Kara bai ma San kina yi ba ki rasa Wanda zakizo sai kusan sa’an mamanki ai ya maki tsufa ni ai wlh nafison D’an matashi 28,29 tayi nisa 30 kamar dai yaya faruq Wanda zaku ci duniyarku da tsinka amma Allah na tuba kamar uncle ai zaman uba da d’iya zakuyi ji fa yanda yake mummurtukewa tayama za a iya zaman aure da shi”

”noor ta ja dogon tsaki tare da cewa “ke wlh bakisan meye so ba ai irin su uncle wlh ko Shekara 60 Yayi Ina so Wama zai ce ya kusa 40 irinsu wlh sunfi iya soyayya da ririta mace hajiya Yaya Faruq din banza wlh Yanzu Haka Uncle ya fisa Kyan jiki saikace shine mai 29 d’in ma nesa ba kusa ba ga kyau ga aji ke ni Ina son namijin kamar uncle wlh ai *MATAR UNCLE* ta gama morewa don ta gama samun rabon duniya saidai ta nemu lahira amma a duniya dai wlh Allah ya gama mata komai kinga uncle dai ga kyau,nasaba,Gayu,tsafta aji,ilimin boko har Matsayin Dr yakai ilimin addini mahaddacin Alqur’ani mai karshema har rubuta sa ya yi uwa uba arziki shi da dukiyar mahaifinsa gwamnati ma saida ta gada har yau ba asan Adadin dukiyar da mahaifinsa ya bar masa ba da ansha kwana saidai wasu su k’ara fitowa kuma shi d’aya tillo D’an sa ke komai ma uncle ya had’a Ana zancen mazan kirki da Allah zaki kawo mana zancen Faruq zararre magana ake ta maza masu capacity Hajiya ki daina saka mana Baki”

Iya k’uluwa Ayda ta k’ulu noor ta kaita bangon karshe gani tayi komai zata ce bata more ba hakan ya sa ta kai mata

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login