Showing 42001 words to 44977 words out of 44977 words

Chapter 15 - MATAR UNCLE BOOK COMPLETE BY MISS HAJO.docx

11 Aug 2025

1453

NA CE INA CAPACITY A WAJEN MACEN DA BA TA K’AMSHI*?📢 NA K’ARA DA CEWA INA AMARE DA UWAYEN GIDAN DA SUKA AMSA SUNANSU SHALELEN MAI HOUSE KAI HAR MA DA Y’AN MATAN DA SUKE KAN CIN LOKACINSU UWA UBA AMARE MASU NIYYAR SHIGA DAGA CIKI TOH GA BABBAN ALBISHIR GAREKU MANYAN MATA NESA TA ZO KUSA DOMIN HAD’ADDIYAR MAI KAYAN K’AMSHIN NAN WATAU *AREEJBYABEER* TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA TURARRUKA KO WANI IRIN LAUNI TUNDAGA KAN *TURAREN WUTA,NA KABBASA,HUMRA,OIL,HALUT OUD,KAJIJI,HUMRA’S GUMELIAN DA SAURANSU* KUNSAN KIMAR MACE DA DARAJARTA BA TA TAB’A CIKA SAI DA K’AMSHI,TURAREN @byabeer YA NA DA MATUK’AR SIRRIKA DA TASIRI GARE KU MASOYA MUSAMMAN WANNAN DA YA KASANCE NA MUSAMMAN DAGA WAJEN Y’AR MUTAN LARABAWA NA TABBATAR KIKA FARA AMFANI DA KAYAN K’AMSHIN arej by Abeer SAU D’AYA TO FA GASKIYA KIN GAMA NEMAN KO WANI IRIN TURARE DON MAI HOUSE DA KANSA ZAI DINGA MAGIYAR A NEMO WANI TA NA NAN A CIKIN GARIN KADUNA *Areej by abeer*

SANANNA CE A HARKAR K’AMSHI TA NA TURA KAYANTA KO WANI STATE CIKIN AMINCI UWA UBA HAR MA DA KASASHEN K’ETARE MUSAMMAN Y’AN UWA MUTANEN NIGER GA KAYANTA DA SAUK’IN KUD’i GA KUMA BIYAR BUK’ATA DA ZUCIYAR MASOYI KU TUNTUB’ETA A KAN NUMBER WAYARTA +234 816 492 1522 KO KUMA A SHAFIKANTA NA SADA ZUMUNTA DOMIN GANI DA IDO TIKTOK @areejbyabeer INSTAGRAM @byabeer SAYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA*

*KWALISA!!!!!KWALISA!!!!!KWALISA*

*INA MATA Y’AN KWALISA MASU JI DA GAYU HAFSAT COLLECTION TA MUSAMMAN CE WAJEN ZAKULO MABANBANTA HADAD’D’UN KAYA NA GAYU TUNDAGA KAN NA SAKAWA,KITCHEN, K’AWATA D’AKI DA SAURANSU ADO DA KWALLIYA SHINE CIKAR MACEN DA TASAN KANTA BA TA WASA DA KAYAN GAYU MUSAMMAN DA SUKA KASANCE NA DABAN DAGA FITACCIYAR Y’AR KASUWAR DA TA YI FICE A WANNAN FANNIN UWA UBA GA SAUKIN FARASHI BABU INDA BA TA AIKA KAYAN TA KUMA CIKIN YARDA DA AMINCI KAR KI BARI A BAKI LABARI Y’AR UWA DOMIN DUK MACEN DA TASAN KANTA BA TA WUCE HAFSAT COLLECTION BA TA NA SAYAR DA,

ATAMFA

LACE

CAMPY GWON

BAGS

SHOES

KITCHEN VTENSILS AND MORE

KAI TSAYE ZA KU SAMETA A ADDRESS D’INTA KAMAR HAKA

*KANO STATE KURNA LAYIN KUNYA STORE*

KO KUMA NUMBER WAYARTA KAMAR HAKA

*08131850861*

_*Miss Hajo ce*_🤙🏿

♠️♣️ *MATAR UNCLE* ♣️♠️



```MALLAKAR```

*HAJARA L SADEQ*

Miss Hajo✍🏾

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*Marubuciyar*

👇🏾

Auren wata Tara

Ni da yaya arman

Khadijatul sabren

Ribar so

Najmat abiy

Mata tace

Komai mukaddari ne

And now

MATAR UNCLE

*LAST FREE PAGE*🤸🏼‍♂️🤸🏼‍♂️🤸🏼‍♂️

*KARKU MANTA GARAB’ASA 300 DAGA 26july TA K’ARE PRICE D’IN LITTAFIN YADAWO YANDA YA KE 500 domin turawa kai tsaye 7026166536 opay Hajara Abubakar Lawal tare da shaidar biya ta 07026166536*

🅿️……………………….*20*

Tare da sulalewa a jikin motar sumammiya wani shu’umi murmushi Waziri ya saki tare da cigaba da tuk’i cikin sauri.,

Bangaren su jawahid wasa wasa shiru ba Ayda ba labari ita kanta khairat sai ta tsure saboda sun lek’a ba kowa ga shi driver da ummi ta aiko ya zo daukarsu lurar da khairat ta yi cikinsu ba Wanda ya lura tare suka fita hakan ya sanyata itama k’in fad’a a ranta ta ce.

”na shiga ukku kar dai waziri yaudarata yayi guduwa ya yi da Ayda da na shiga ukku na lalace ni

Khairat “

tun hankalinsu bai tashi ba har takai ga baki dayansu hankulansu a tashe ya ke domin lungu da sakon wajen ba inda ba a duba ba ba Ayda ba labarin ta,

Sun Kai awa biyu Ana nemanta hakan ya sa driver cewa kawai ya saukesu gida tunda ba ta nan gashi dare na yi kowaccensu iyayensu sai Kira suke musamman ummi.

haka akayi kowa aka sauketa gidansu Cike da tashin hankali.,

Kafin ka ce me b’atan Ayda ya karad’e dukkanin Family din da ke cikin gidan ummi labari kuma har ya kaiwa Faruq ga shi wayarta na hannun mufeda bare akai ga fara bincike da wayar.

Cike da tsananin tashin hankali ya fito waya kare a kunnansaa lokacin karfe d’aya saura umma da Abba suka fito a tare Jin motsin bude kofa tare da tambayar “lafiya”

Tamkar zaisa kuka ya ce”Abba Ayda ce ta b’ata”subhanallah b’ata kuma yaushe bayan dazunnan kuna tare wajen kamu”

ya ce”abba bayan tafiya ta wai aka nemeta aka rasa ba ni na mayar da su ba “

“umma ta ce”hmm daman barewa tayi gudu d’anta ya yi rarrafe yanzu haka wajen wani D’an iskan nata ta tafi ka zo ka na tada jijiyoyin wuya yarinyar da daman bataji ko a makaranta anfad’a Banda yawon iskanci ba abunda suke ba wani b’ata iskancine yanzu haka da za a bibiya bata wuce hotels daman ai sauran k’arti Y’an iska za ka kwasa kad’anma ka gani shiyasa ka ga ba ruwana da sha’anin watsatsten bikin nan ko gayya banyi ba ko y’an uwana ba Wanda na fad’awa chan ku k’arata kowa sai rariya yasan zata zubda ruwa”

ta na gama fadar haka ta shige ciki ba tare da ta jira me zasu ce ba ga mamakina Abba ko Kala be ce mata ba

sai kallonshi da ya maida ga faruq ya ce”koma ciki ka kwanta yanzu dare ya yi zuwa safe sai muje gidan tare”amma abba “daga masa hannu ya yi ya ce “kayi abunda na ce”.

Daga sallar asuba abba da faruq Kai tsaye gidan ummi suka nufa da kusan kowa na gidan kwanan zaune ya yi Cike da zullumi da tashin hankalin wannan al’amarin da ya faru “

Ummi tun jiya ta ke kiran wayar Adnan ba ta shiga Har safe yanzu ma shi ta ke Kira amma switch upp ga shi ta je part dinsa alamun baya nan ba gidan ya kwana ba Nan aka bada report ga y’an sanda na b’acewar Aydar “

“Yanzu ya za ayi da bikin nan gobe daurin Aure amarya ta b’ata”cewar Aunty Laila “ummi ta ce”d’aurin aure ba abunda zai fasu Insha Allah ko ta na nan ko ba ta nan za a d’aura “

Faruq da maganganun ummansa ke tayi masa yawo tun jiyan daddaren ya fara gaskatawa da maganganun na ta tunda shima daman ya na zarginta ai ko indai haka ne “wlh bazai kwashi sauran wasu ba shekara da shekaru duk burin da ya ci ya tashi a banza bazaiyu ba”

kowa na fadar albarkacin bakinsa Banda faruq da ya tashi ma ya bar palourn gaba d’aya tare da barin gidan.”

Abu kamar wasa har la’asr ba Ayda ba labarin ta daman ranar walima ce za ayi kasantuwar juma’a sai fasa walimar akayi hakan sosai ya k’ara d’agawa ummi hankali kar dai ace yarinyar nan guduwa ta yi Amma da ta kunyatani a idon duniya da wani ido zan kalli jama’ar da na Tara .”,

Ga shi duk inda ya dace a Kira a ji ta na nan an tambaya ba ta nan Aunty Laila ta ce “gaskiya a tuhume k’awayen nan nata ban yarda da su ba Ina tunanin tuntuni sun shirya tunda daman shekaranjiya ta na bata son Auren”

“Mamy ta ce “Nima Ina zargin haka d’aki guda aka Tara mafi kusan kawayen nata dukannsu da sunanan al’amarin ya faru don tun safe suka zo gidan ummi cikin kwantar da murya ta shiga musu nasiha da lallashi Akan idan da sa hannunsu a b’atar Ayda su fad’a”kowacce cikinsu ta rantse da ba ta da masaniya”

Mufeda ta ce”Toh wai garin ya ma ta sille daga cikinmu lokacin fa muna tare”?Ummi ta ce “shine abun tambayar zargina ya tabbata kenan guduwa ta yi da gangan ko ga shi harda barin wayarta alamun kar ma ta bada kofar da za a ganota Innalillahi wa inna ilaihirajiun Maryam ta kunyatani ya zanyi da jama’ar nan da na tara ta Ina zan bullowa al’amarin nan”

Khairat da har lokacin kuka ta ke tabbas ko me ya faru da Ayda itace sanadi ga shi kira ya fi d’ari tayiwa waziri wayarsa switch up banda dukan tara tara ba abunda gabanta ya ke ,

A haka dai har magrib y’an uwanta da Wanda suka San faruwan al’amarin nan dukakkaninsu da ka kalli fuskarsu kasan ba walwala.,

Jawahid da ta zuba uban tagumi ta kalli Mufeda ta ce”wai da gaske kin duba wayarta ba Wanda ta yi waya da shi kafin b’acewarta?

Mufeda da har lokacin ta na Hawaye ta ce”ga shi ummi ce karshen wayarsu suna gama waya ta miko mun kuma na duba tun yau ma babu Wanda ta yi waya dashi namiji bayan Faruq”

“Innalillahi wa inna ilaihirajiun Allah ubangiji ka mana maganin masifa wannan wani irin tashin hankali ne amarya ta b’ata gobe daurin aure”

Noor ta ce “Allah sa ma guduwa tayi da gaske da wannan masifaffen Auren ai gwara fasasa don fa bakuga irin abunda mamansa tayi mana ba wlh ko ni ce guduwa zanyi da in auri d’anta ai gwara in shiga duniya”

Fatima da ke jinsu ta ce”yiwa mutane shiru a wajen nan stupid da Chan ai tasan da hakan ta yarda saida biki ya rage kwana d’aya wannan ai cin fuska ne da wulakanci tayi “

Aunty Khadija ta ce”babba ma kuwa ni wlh Ummi ta fi ban ma tausayi “Fatima ta ce “ke ta ba tausayi ko ni Khadija Yanzu haka DR ya ke dubata jininta ya hau allurar bacci ma aka mata najima banga ummi a cikin tashin hankali kamar na yau ba “

Mufeda da ke hawaye ta ce”ni fa banajin Ayda zata gudu da gangan akwai dai abunda ke faruwa”

Noor na tab’e Baki ta ce”Allah sa ma guduwa ta yi ni wlh da ta yi ma shawara da ni da na bata mab’uya ko na rakata guduwar “

Fatima ta Kai mata bugu tare da zaginta ta ce don uwarki to kina sane a tuhumeki kinsan inda ta ke”

ta mike Tana harararta ta ce”

“karki sake dukana haihuwata kikayi k’arewar Ina sane sai najini a prison sai na fada inda ta ke mtwsss”“

Ta ja tsaki ta fita fatima ta mike zata bita Aunty khadija ta kamo hannunta ta ce”ba girmanki ba ne”ta ce”wlh sai naga ubanda ya tsaye mata a k’asar nan ni sa’artane ni wlh banma yarda da ita ba tasan inda ta ke”

Khadija ta ce”da ta San inda ta ke bazatayi wannan maganar ba tasan sai a tuhumeta muje mubar musu palourn don Allah “

suna barin Palourn jawahid ta rufe d’akin junansu suka cigaba da tuhuma amma amsar dai d’aya ce basu da masaniya domin khairat ta na tsoron fad’ar gaskiya bata San wani irin fasaara za a mata ba”

Bangaren Ummi sai goma da rabi Allurar ta saketa koda ta tashi tambayar an ganta ta shiga yi Amsar d’aya ce babu labarinta dafe goshinta ta yi ta na anbata hasbunallahu wani imal-wakim”

Ya zatayi da rayuwarta gashi police station ma maganar daya ce babu ita kuma ba ta k’araji daga Faruq da Abbansa ba “

kiramun Yaya Bukar Khadija”ummi ta fad’a ta na mikawa khadija wayarta daidai zata amsa Haidar Autan aunty Laila ya fad’o d’akin da gudu Cike da hak’i ya ce”

“ummi ga Aunty Ayda Chan muna waje wasu suka yaddota a mota jikinta duk jini kamar ma ta mutu”

“Innalillahi wa inna ilaihirajiun duka ilahirin d’akin aka kwasa kafin kowa ya fice A matukar guje sukayi waje kwance suka sameta kanta ba ko kallabi jini har ya fara bushewa a k’afafunta .

kallo d’aya Ummi tayi wa Ayda ta ji jinta da ganinta sun gushe tayi baya zata fad’i da hanzari Mamy tayi karfin halin rikota ta fada jikinta sai lokacin Mamy ta samu damar karanto “

“Innalillahi wa inna ilaihirajiun kafin ta ce mu hanzarta tafiya asibiti kunga ta na da hawan jini kar ta samu attack gaba d’aya sun rud’e lokacin tuni muhammad D’an Mamy ya fito da mota shi aka taimaka aka saka Ayda mota tare da ummi sai aunty Laila da Mamy suka nufi asibiti”

Allah yasa dare ne anguwar ba wanda ya fahimta halin da ake ciki.,

Gidan biki sai ya koma tamkar gidan mutuwa domin y’an matan da ke ciki koda suka koma kuka suka dingayi.,

tashin hankali ne ba k’arami ba ya nufi duk wani masoyin Ayda khairat ta San Ayda bazata tab’a yafe mata ba har abada amma waziri ya cucesu ita kanta ta shiga ukku ba shi ba“

Mufeda da har ta fara sikewa da kuka ta kalli aunty khadija da suma hawayen suke ta ce”Aunty rapping dinta akayi dagaske ko mafarki nake?

Kasa ba mufeda amsa tayi sai Bari dakin tayi ta na kuka wannan wani irin tashin hankaline ya ziyarci Family d’in nasu”.

Su ummi koda isarsu Asibitin Cikin gaggawa aka Karbesu tuni labari har ya kaiwa Faruq da Abbansa nan asibitin suka nufo cike da tsantsar tashin hankali faruq ya ke kallon jinin da ke jikin k’afar Ayda .,

rumtse ido yayi kafin ya bude ya gaskatar da abunda idanuwansa ke fad’a masa Baiyiwa kowa magana ba haka bai kula kowa ba da ke wajen ya juya ya bar asibitin tamkar zai tashi sama idanunsa har dishi dishi yake gani a yayinda zuciyarsa tamkar zata buga.,

ansamu an daidaita hawan jinin ummi a hankali ya fara sauka ta fara dawowa hankalinta a yayinda wata nurse ta shiga mata nasiha gami da lallashi ummi ta kalli nurse d’in ta ce .

“wani hali y’a ta take ciki likita ku kaini in ganta ta na raye”Nurse din ta ce”Ki kwantar da hankalinki hajiya Ta na Raye likitoci ne a kanta Insha Allah Za ta samu lfy”

Ummi ta ce “Ina hankalina zai kwanta ki barni naji sauki Ina son ganinta “

Nurse din ta ce”kiyi hakuri hajiya zaki ganta yanzu likitocine a kanta”

Hawaye na zuba daga idanun ummi ta koma ta na jinginawa jikin gadon tare da cewa”

“Wlh ko da kaf dukiya ta zata k’are sai na kwatar miki hakkinki wanda ya yi miki wannan bak’in zalincin Ayda bazan tab’a Bari ya ci bulus ba Ana gobe d’aurin Aurenki a keta miki Haddi ya subhanallah Allah ka sa ba gaske ba ne mafarki na ke ni maryama”Gaba d’aya ummi ta rude a matukar tashin hankali ta ke ciki ,

kafin ta maida kallonta ga nurse din ta ce “Da gaske abunda muke zargi ne ya faru da ita Fyad’e akayi mata da gaske likita……..✍️

Tirkashi Ana wata ga wata🙆‍♀️

Wacece asalin Ayda?

WAye Adnan?

Me ya faru da Rayuwar momyn Ayda a baya?

Waye mahaifin Ayda?

Wacece *MATAR UNCLE*

Ina labarin zahra ?

Me Ramadan da ummansa ke shiryawa Akan Adnan”?

Ya rayuwar Ayda zata kasance a gaba?

Me ya faru da ita?

Suwaye sabbin da zasu shigo labarin?

Hmmmmmm Da sauran rina akaba me akayi?kudai kawai ku gyara zama tare da cigaba da kasancewa da alqalamin miss hajo a wannan doguwar tafiyar mai

Cike da mabanbanta Salo da darussa!!

*Alhmdulillah a nan na kawo k’arshen Free pages na wannan littafin nawa mai suna *MATAR UNCLE* ga me bukatar cigaba da karatu Kai tsaye zai biya ta wannan asusun bankin 7026166536 palmpay Aliyu Lawal tare da shaidar biya ta number wayata kamar haka 07026166536 sai mun had’e Paid Grp Masoyan asali karkuji komai Wasa farin girki ba a fara komai ba a cikin littafin yanzu zamu Fara wannan din duk Sharan Fage ne kudai kawai ku kasance da Alqalamin miss hajo a koda yaushe🙏sannan ina hadaku da girman Allah kar ku saya da niyyar fitarmun da littafi hak’k’inane bazan yafe ba mu rikewa juna amana please*

🛍️Assalamu Alaikum – Hafsat Collection ce!

Kinason kayan masu inganci masu kyau kuma cikin sauƙin farashi? To ba ki da matsala! 🥳💃

📌 HAFSAT COLLECTION ta kawo muku: ✨ Kayan gyaran gida

✨ Kayan ado da kyalliya

✨ Kayan mata da maza masu kwalisa

✨ Kayan kitchen masu kyau da karko

🔥 Duk a cikin farashi mai sauƙi!

📦 Muna a Kano, amma muna aikawa zuwa ko ina cikin amincin Ubangiji! 🙏

Maza ki shiga group ɗinmu yanzu:

👉

📌 Kasance da Hafsat Collection – Sayan daidai, ko sari!

*CAPACITY CAPACITY CAPACITY NA CE INA MATA MASU CAPACITYN SUKE NA CE INA CAPACITY A WAJEN MACEN DA BA TA K’AMSHI*?📢 NA K’ARA DA CEWA INA AMARE DA UWAYEN GIDAN DA SUKA AMSA SUNANSU SHALELEN MAI HOUSE KAI HAR MA DA Y’AN MATAN DA SUKE KAN CIN LOKACINSU UWA UBA AMARE MASU NIYYAR SHIGA DAGA CIKI TOH GA BABBAN ALBISHIR GAREKU MANYAN MATA NESA TA ZO KUSA DOMIN HAD’ADDIYAR MAI KAYAN K’AMSHIN NAN WATAU *AREEJBYABEER* TA SHIRYA TSAF DOMIN GWANGWAJEKU DA TURARRUKA KO WANI IRIN LAUNI TUNDAGA KAN *TURAREN WUTA,NA KABBASA,HUMRA,OIL,HALUT OUD,KAJIJI,HUMRA’S GUMELIAN DA SAURANSU* KUNSAN KIMAR MACE DA DARAJARTA BA TA TAB’A CIKA SAI DA K’AMSHI,TURAREN @byabeer YA NA DA MATUK’AR SIRRIKA DA TASIRI GARE KU MASOYA MUSAMMAN WANNAN DA YA KASANCE NA MUSAMMAN DAGA WAJEN Y’AR MUTAN LARABAWA NA TABBATAR KIKA FARA AMFANI DA KAYAN K’AMSHIN arej by Abeer SAU D’AYA TO FA GASKIYA KIN GAMA NEMAN KO WANI IRIN TURARE DON MAI HOUSE DA KANSA ZAI DINGA MAGIYAR A NEMO WANI TA NA NAN A CIKIN GARIN KADUNA *Areej by abeer*

SANANNA CE A HARKAR K’AMSHI TA NA TURA KAYANTA KO WANI STATE CIKIN AMINCI UWA UBA HAR MA DA KASASHEN K’ETARE MUSAMMAN Y’AN UWA MUTANEN NIGER GA KAYANTA DA SAUK’IN KUD’i GA KUMA BIYAR BUK’ATA DA ZUCIYAR MASOYI KU TUNTUB’ETA A KAN NUMBER WAYARTA +234 816 492 1522 KO KUMA A SHAFIKANTA NA SADA ZUMUNTA DOMIN GANI DA IDO TIKTOK @areejbyabeer INSTAGRAM @byabeer SAYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA*

_*Miss Hajo ce_*🤙🏿

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login