Showing 9001 words to 12000 words out of 80494 words

Chapter 4 - INSAF BOOK COMPLETE BY Amnah El Yaqoub.doc

Asim yagane shine wanda akasa kudi Ana nemansa,saida yaqara kallonsa sosai har wani karkatar dakai yake Yana yiwa Asim kallon qurulla domin ya tantance shid'inne dayaga photonsa atv ta gidansu koba shi bane? (>??>?#?)
cikin sauri yabar wajan ya garzaya folice station domin sanar da 'yan sanda,bazaiyi sakaci wannan kudi ya wuceshi ba (>?#?>?#?)

Cikin damuwa Asim yadubi baba yace "haba Baba, wannan yarinyar ba 'yarku bace? Meyasa kuke jifanta da wannan kalaman?"

Baba yayi Shiru Yana kuka yakasa Bawa Asim amsa, inna ma cikin kuka tace "Amina ba 'yarmu bace, bamu San taba, bamu San tushenta ba, bamusan sunan taba, muma tsintarta mukai muka riqeta tsakani da Allah kamar yarmu ta cikin mu, munyi mata Rana mun rufa mata asiri ashe Bahaka bane a ranta, Gatanan azaune aurenta biyar duk mazajen data aura mutuwa suke, jiya jiya muka rufa mata asiri muka aura mata d'anmu, Toshima yau mun wayi Gari takashe shi, takashe Ammar, Ammar shine d'anmu na cikinmu, Amina ba 'yarmu bace " (=?F? @&?)

Gaban Amina yayi wata irin fad'uwa, cikin sauri tad'ago kanta ta kalli Inna, Inna ta kalli qwayar idonta tace"qwarai kuwa abinda kikaji shine gaskiya, kije can kinemi Iyayen ki, babu ni babu ke Amina tunda kikamin Sanadin rabani da d'ana "

Asim kuwa qamewa yayi atsaye, aure biyar? gakuma Ammar Aure shidafa kenan, wannan qanqanuwar yarinyar? Tayaya? Wannan wanne irin tashin hankali take gani?to suwaye Iyayen ta?

Begama tunanin saba yaga Amina ta tashi tazube gwiwoyinta qasa, tahade hannayenta biyu waje daya (=?O?
Inna ko kallonta batayi ba, baba kuwa yama Kasa d'ago kansa ya kalleta, larai ta riga tatona musu asiri, ta tonawa yarinya asiri a cikin wannan d'unbin jama'ah, da wanne ido zai kalli Amina?

Inna tajuya cikin kayansu da maigari yasa aka futo musu dashi ta dauko wata baqar Leda tasake jefawa Amina ledar tace "ga tsiyar kinan,dasu muka tsinceki,Allah yahadamu a darussalam"


Cikin bacin rai Asim ya qarasa wajanta tare da miqa mata fari kuma lallausan tafin hannunsa, fuska a d'aure yace "ke tashi mutafi"

Cikin sauri tad'ago jajayen idanunta da suke cike da hawaye ta kalleshi







Sorry fan's, kunji nace sunan labari INSAAF amma kuma inata maganar Amina Amina,>?? to Masu wayo dakuma fahimta ne kadai zasu gane wacece INSAAF a cikin wannan page din=? ?






Amnah El~yaqoub
' [2/5, 10:53 PM] El~Yaqoub: INSAAF



Writing by:Amnah El yaqoub


7&8

Like my page on Facebook =?G?
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493



Idonsa cikin nata ya d'aga mata kai alamun da gaske yake
Hawaye masu zafi suka sake zubo mata, yayinda jama'ar wajan suka zama 'yan kallo suna ganin wani sabon salon iskanci, namiji Yana meqawa mace hannu a cikin bainar jama'ah (>?#?)

Kallansa take hawayen idonta sunqi tsayawa, waye shi? Bata sanshi bafa, tayaya zata bishi tabarsu Inna? idan tabishi tasan irin tashin hankalin da zata haddasa masa agidansu? Cikin ranta take wannan tambayoyin, ahankli ta girgiza masa kanta alamun bazatabishi ba

Dago Idonsa yayi ahankali, asace yake kallon d'unbin mutanan da suke kallonsu amma yarinyar nan ta kunya tashi agabansu, saboda me zata zauna da mutanan da sukai mata irin wannan cin mutuncin,? Baiyi wata wataba yasa hannunsa ya fuzgota tare da bakkon kayan nata harma da ledar da Inna ta wullo mata
Mutanan wajan kuwa suna ganin haka suka fara salati (>?#?>?#?)

Hannunta takeson qwacewa amma yahana ta Damar hakan, janta yayi suka fara tafiya, Amma Amina sai kuka take sosai kamar ranta zai fita, juyowa tayi tana kallonsu Inna, cikin matsanancin kuka tace "Inna Karki barni, baba..."

Haka Inna ta dauke kanta, shikuma baba har zuwa wannan lokacin ya Kasa kallon Amina

Akan idon jama'ar wannan Gari, Asim yatafi da Amina babu wanda yahana shi, suna ganin kamar ma yatemakesu ne tunda yarabasu da masifa
Tun suna tafiya tana turjewa har tayi hakuri taci gaba da binsa, cikin bacin rai da tsananin damuwa ta fizge hannunta daga riqon dayayi mata

Cak! ya tsaya yadaina tafiya, juyowa yayi ya kalleta fuskar sa adaure, inbanda rashin hankali da kuma yarinta me zaisa wannan yarinyar tazabi zama a cikin mutanan da basa kaunar ta? Har sai yayi mata dole Akan rabuwa dasu? Afuto dakai waje ayima wannan tozarcin amma ahakan kake kuka kana kiransu? Haushi ya kamashi, jakar bakkon kayanta da d'aya ledar yazubar agabanta sannan yajuya yayi tafiyar sa (=? ?)

Wani irin zazzafan zazzabi yakeji, ga kansa da yake ciwo, shi mema yasa yadawo ne? da yanzu ba zaiga wannan tashin hankali ba, wani bangare da zuciyarsa yace masa laptop dinka, itace dalilin dawowarka, yatuna yanda su Inna suka iya rufe Idonsu suka ciwa wannan yarinyar mutunci tayaya zai Iya tambyarsu wata laptop bayan radadin dasukeji na rashin dansu? Yasan cewa laptop kam yariga yarasata, yarasa komai, bai kuma san Yaya zai fuskanci Ishraqa da wannan maganar ba (Tofa! >??)

Akan bakkon kayan nata tazube tana gunjin kuka, yanzu su Inna dama ba iyayenta bane? to suwaye iyayenta? Menene sunan ta? Babu wanda yasan amsar duka tambyoyinta Sai Allah
Dago kanta tayi, can ta hangeshi Yana tafiya har yayi Nisa, awannan halin batada wani zabi bayan tabishi, idan tabarshi yatafi ma ina zata? Ina ta nufa? Wata ke dashi a duniya bayan Allah?

Dasauri ta dauki kayanta tadora aka tabishi (>?#?)

Yanajin tafiyarta a bayansa amma ko kallon inda take Baiyi ba, suna tafiya babu wanda yake magana Sai kukanta da yake barazanar rabe masa kansa gida biyu wanda yake masa matsanancin ciwo, ita kuwa kuka take kamar hauka, barinma idan tatuna maganar su Inna, ita yar tsuntuwa ce, haka suka dinga tafiya har sukai nisa sosai daga qauyen suna shirin shiga wani qauyen nagaba

Yagaji sosai da wannan tafiya, shikansa baima San ina sukeyi ba, ga zazzabi daya rufeshi, sanyi yakeji a jikinsa kamar Ana zuba masa ruwan qanqara, ya kamata subar tafiyar haka su qarasa titi su nemi Mota

Har zuwa wannan lokacin Amina kuka take, har mamakin kukanta yake kwata kwata Bata gajiya, adede wata bishiya ya tsaya batare da tunanin komai ba yazube awajan tare da riqe kansa da yake masa mugun ciwo

Tana ganin haka kukanta ya qaru, bakkonta dake kanta tasauke qasa, sannan ta tsugunna akusa dashi har jikinta Yana gogar nasa, cikin muryar kuka tace "meyake damunka?, kaima mutuwa zakayi ka barni ko?, nikam nashiga ukuna..." ta qarasa maganar cikin matsanancin kuka tana Dora hannunta a kanta (=?F? @&?)

Jinta akusa dashi,dakuma sanyin dayakeji yasa yafuzgota jikinsa kozaiji dama dama, al'amarin yabawa Amina tsoro, harta zaro manyan idonta tana kallansa ganin yanda ya rungume ta hartanajin yanda Boobs dinta suka kwanta Akan faffad'an qirjinsa, shi kansa ya karbi saqon yanda ya kamata dukda Yana cikin yanayin zazzabi (=?H?)

Rawar sanyi da taga yanayi anan tagane nufinsa, Ahankali tasa hannu tacire babban dankwalin atamfar da yake kanta, iskar bishiyar da suke zaune takad'a dogon gashinta zuwa fuskar Asim, idanunsa a lumshe suke, amma Sarai yaji saukar gashin nata, hannunta tasa tajanye gashinta sannan tarufe masa jikinsa da d'ankwalin




*** ***** ***



A bangaren isyaku kuwa, Yana zuwa police station jikinsa har rawa yake yace Yana so ahadashi da d.p.o
kofur Shamsu yakalleshi "lafiya kake neman sa? Idan qara kakawo muzaka yiwa bayani"

"Yallabai ba qara nakawo ba, abinda nakawo ai ya girmi qara Yallabai,"

Yayi qasa-qasa da muryarsa yace "kuma zaku samu naku kason, zanbaku wani abu daga ciki"

Sunajin furucin isyaku suka fara washe baki, nan da nan suka kaishi har office din d.p.o, isyaku ya kalleshi da kyau yace "Yallabai ina mutumin nan da kwamishinan 'yan sanda yabada cigiyar sa? "

D.p.o ya kalleshi da kyau yace "eh inajin ka meyafaru"

Saida ya kalli gefe da gefensa kamar Yana tsoro Kar wani yaji shi (>?#?)
sannan yace "to yanzu haka Yana nan a cikin qauyenmu, inaso kabani yansanda Mota guda, muje ataho dashi" (>?#?=?F? @&?)

D.p.o ya kalli isyaku da kyau yace "ka tabbata abinda kake fadamin gaskiya ne?"

Isyaku yasa ka hannunsa dede fuskarsa yanuna idanunsa duka biyun yace "ganin Idona naganshi Yallabai" (>?#?)

D.p.o yasake kallansa da kyau yanaso ya Gano gaskiyar abinda isyaku yake fada masa,Anya kuwa gaskiya ne? Tayaya mutum babba kamar Asim zai Iya zama a cikin wannan qauyen? Anya ba qarya Yaron nan yake musu ba?

cikin zaquwa isyaku ya???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ce "haba Yallabai, me muke jirane? Kabasu umarni kawai mu tafi, ha'ah"
Yaqarasa maganar tasa cikin gundura (=??)


D.p.o yayi Ajiyar zuciya yace "tunda hakane, ainima banga ta zamaba, dani za'aje, tashi mutafi" (=?3?)

Murna ta kama isyaku, nan da nan kuwa aka cika Mota da yansanda kamar yanda isyaku ya buqata, saide suna zuwa kofar gidan Malam Buba sukaga babu Asim babu dalilinsa,(=?F? @&?)
Sai sauran mutane dasuka Gama watsewa daga jana'izar Yaya Ammar, dakuma Inna da baba dasuka kwashi kayansu a amalanke da alama Garin zasu Bari

Idanun isyaku yayi wiqi-wiqi ya raina fata (=??=??)
D.p.o ya kalleshi cikin bacin rai yace "ina yake?"

Isyaku yayi Shiru kamar andoka masa sanda yakasa d'ago kansa yakalli d.p.o bare su hada ido dashi (>?#?>?#?)

D.p.o Yana ganin alamar qarya isyaku ya shimfida musu nan take ya kalli yaransa yace "ku saukeshi a motar nan kuyi masa dukan kawo wuqa"

Isyaku yanajin haka yadora hannunsa aka (=?F? B&?) yace "nashiga uku ni isyaku namutu na lalace, Yallabai shi dukan dama harda na kawo wuqa?"

D.p.o yace "zaka ganshi yanzu-yanzu" yaqare maganar Yana Kallan yaransa

Nan da nan kuwa suka gane ma'anar kallon nasa, suka jefo isyaku waje daga cikin motar suka hau dukansa kamar Allah ya aikosu, Sai ribd'arsa suke Yana ihun neman agaji (=??)

Basubar isyaku ba saida suka nuna masa jiki, nan take zazzabin wahala ya rufeshi =?G? B&?




*** ***** ***



Tun dazu yake hangosu daga gonar sa, yaga alama kamar matafiya ne, gashi har yamma tayi yanaso Shima yatafi gida, dama gewaya yazoyi gonar tasa

"bayin Allah lafiya kuwa kuke zaune awajan nan tun dazu?"

Ahankali ta dago kanta ta kalleshi, babban mutum ne daya manyanta sosai, kansa Yana dauke da rawani irinna malamai, cikin sanyin murya tace "tafiya muke, bashida lafiya ne"

Mutumin ya kalleta yaga idonta duk hawaye sun bushe, ya kalli Asim daya riqe Amina a jikinsa yaga bacci yake, yace "Ashsha, Aida kin nemi temako yarinya, ku taso mu qarasa gidana yasha magani,tasoshi"

Duniyar tunani tafada, to ita dabatasan sunan saba tayaya zata kirashi harya tashi? Daga wa mutumin kai tayi alamun amsawa, Ahankali tafara zare jikinta daga nasa, cikin baccinsa yaji zatabar jikinsa yasaka hannu ya sake rungume ta
Mutumin ya kallesu yayi murmushi da alama de ma'aurata ne, ya kalleta yace "tashi mijin naki mana"

(miji) kalmar tadaki dodon kunnanta, Allah yakiyaye tasake yin waani auren a yanzu, idan tayi aure ma ai batayi wa kanta adalci ba, tunda tasan haqqin wanda ta aura zai rataya awuyanta ne idan ya mutu
Hannunta takai kan muscles =ت?
Mutumin dake tsaye ma yace "kuyi hakuri na tasheku, kuzo muje gidana ku huta gashinan babu Nisa"

Ahankali yamiqe tsaye Yana runtse Idonsa, yadora hannunsa Akan goshinsa daya Sara masa kasancewar ya tashi tsaye,jiyayi kansa Yana juyawa yatafi luuu zai Fadi, cikin sauri Amina tatareshi yazube ajikinta, kansa ya sauka adede qirjinta, gabanta yayi mugun faduwa,meta aikata haka? Wannan mutumin gaba daya yagama jin komai na jikinta yau, Sai bayan ta riqeshi ne take tambayar kanta mema yakaita tareshi batabarshi yafadi ba?

"subhanallah..." cewar wannan mutumin, yaci gaba da fadin "kamashi muje, sannu bawan Allah"

Haka Amina tariqeshi ajikinta, Shima mutumin yariqe masa hannu suka tafi, basu yi wata tafiya mai nisaba suka qara so kofar gidansa da yake cikeda almajirai sunata karatun Allo

Kai tsaye gidansa yakaisu, matarsa tayi musu tarba mai kyau, takaisu wani daki atsakar gidan dake gyare tsaf, harda shimfida, mutumin yadubi Asim yace "kwanta anan Yaro" ya sake Kallan matarsa yace "kawo musu abinci da ruwa, zanje nasiyo masa maganin zazzabi"

Matar ta Amsa masa sannan tafuta daga d'akin, Amina ta dubeshi tace "ga katifa nan ka kwanta"

Daga mata kai yayi alamun amsawa, sannan ya fara shirin kwanciya Akan katifar, tsugunnawa tayi asetin kansa tasaka hannu tana gyara masa fillon daya Dora kansa akai

Yasaba duk lokacin dabayajin dadi Mamy ce take zama atare dashi, musanman idan Yana ciwon kai ta dinga yimasa massage akansa kenan harsai yadanji dama dama, Amina kuwa tana gyara masa fillon tafara kokarin miqewa ahankali yasaka hannunsa da yayi zafi sosai yariqeta, bin hannun nasa tayi da kallo fari tas dashi, hannunta tafara zarewa ya sake damqe hannun nata cikin nasa, babu yanda ta'iya haka tadawo wajan tazauna tayi Shiru tana kallon ikon Allah, shikuwa bargon dake kan shimfidar yaja yarufa dashi har kansa

Sai gab da magrib maigidan yadawo, har lokacin tana nan zaune a d'akin tayi tagumi,saide ta qwace hannunta daga cikin nasa dataga yayi bacci, abincin da matar ta kawo musu ma cokali daya tayi tarufe abincin, maganin ya ajiye yace "tasheshi yaci abincin yasha magani"

Fillon nasa tafara bugawa, daqyar ya tashi, maigidan yabashi abincin, daqyar yaci kadan, Ahankali yace "ya'isa" kallansa tayi cikin sauri, tun taho warsu daga qauyensus Sai yanzu taji yayi magana, ga fuskarsa a daure, mamaki ya kamata tsawon wannan lokacin suna tafiya Amma beyi mata magana ba

Maganin yabashi,Asim ya kalli maganin ya yatsina fuska, sannan yace "banson magani" murmushi mutumin yayi, yace "haba dana Sai kace ba namiji ba kace bakason magani? Kokuma saboda baku sanni bane shiyasa? To sunana malam Ibrahim mai Allo, ni limamin Garin nan ne, ga mata ta can, nakawo ku gidanane kuhuta idan kaji sauqi bayan kwana biyu saiku tafi, bazan cutar daku ba Yaro"

Murmushin qarfin hali Asim yayi jin wannan dogon Bayani da yayi musu, Ahankali kamar me koyon magana yace "A a... ni.. dama can banso"

Malamin yayi murmushi ya ballo maganin yabawa Amina yace "toke yata karbi kibashi, wata qila ke kikasan Yanda kike bashi" (>?#?)

Cikin inda inda tace "a a Nima fa bansan..."

Ganin zata tona musu asiri yasa Asim cikin sauri yabawa liman hannu, liman yabashi maganin, yaqyar ya'iya hadiye maganin har wani girgiza kansa yake kamar me iskokai (=??)

Sannan yatashi yafuto domin yin alwala, Shima liman yafuto Yana tambayar sa menene sunan sune, basu fada masa ba, itade Amina bataji amsar daya bashi ba


Wajan karfe Tara na dare ta futo daga d'akin tazauna a tsakar gidan, liman yashigo gidan ya ganta azaune yace"yata meyasa baki kwanta ba har yanzu? "

Tace"yana cikine, shine na futo"

Mamaki ya kama liman, yace "a a, ba mijin ki bane dama?"

Tace "Eh baba"

Liman yace "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un" yayi Shiru kamar Yana nazarin wani abu, yadago ya kalleta yace "dazu yafadamin sunan ki Amina, 'yata Amina meyasa kuka Bari kuna cudanya da juna bayan kunsan bakuda aure?"

Amina tayi Shiru takasa bashi amsa, Shima Shiru yayi Yana tuno yanda yasamesu a bishiya rungume da juna, dakuma inda zai Fadi tatareshi yafada jikinta"

Kansa ya jinjina yace "taso kishiga d'akin talatu ku kwana tare"
Babu musu tashige d'akin matarsa, shikuma yayi d'akin da Asim yake ciki

Washe garima haka matar gidan tayi musu abubuwan daya dace, jikin Asim kuma da sauqi sosai ba kamar jiya ba,da yamma yasha magani ya kwanta daga Naan yayi bacci, d'akin ta leqa taga Yana bacci, tana juyowa zata koma wajan matar liman saiga liman dinma yashigo gidan, ya kalleta yace " 'yata zo zamuyi magana"

Binsa tayi abaya, suka shiga d'akin matarsa, ya kalleta sannan yafara mata magana cikin fahimta yace, "Amina"

Dago kanta tayi ta kalleshi, tunda suka hadu da mutumin yake mata kwarjini, tana ganinsa kamar mahaifinta, tace "Na'am baba"

Yace "Amina a'ina kuka hadu da wannan bawan Allah?"

"a garinmu, yajima acan" cewar Amina

Liman yace "to ko made a'ina kuka hadu na temaka muku Amina, nafarko jiya yafadamin Lagos zaku tafi, daga nan bai fadamin komai naku ba, Nima ban tambayeshi ba, Amina tafiyar ku tare ni inaganin kamar akwai hatsari a cikinta, tafiya zakuyi doguwa, kuma a hanyar nan bakusan abinda zai faru atsakanin Kuba, ko babu komai akwai shaid'an, yanayin dana ganku jiya ni kaina nayi tunanin mata da miji ne, saboda haka na yanke hukunci dazu dazun nan natara almajirai na dakuma maqotana nadaura miki aure kedashi " (=?3?)

Dam! Dam! Gaban Amina yahau luguden faduwa, meyasa hakane? Sai yaushe ne masifa zata Dena bibiyar rayuwarta? Batasan lokacin data fashe da kuka ba, cikinKuka tace "innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, nashiga uku na, Dan girman Allah karaba auren nan, wallahi Allah banaso, ni banason shi, qaddarar dana Bari abaya ba ta isheni, bazan sake auren kowa ba"

"Amina banida ikon Raba muku aure, wannan Yana hannun mijin ki, bansan haka abin yake ba, da banyi gaggawar daura muku aure ba, amma inaso kisani, ni Allah baibani haihuwa ba, yanda kike kirana da suna baba Amina sainakeji kamar yata ce take kirana, ina jiye muku tsoron abinda zai Iya faruwa atsakanin kune shiyasa nayi muku auren, Amina tunda muka hadu daku naji kamar da yan'uwana nahadu, Dan Allah Karki watsamin qasa a'ido, shikuma dan'uwan tafiyar taki zan zauna dashi Gobe da safe in sanar dashi abinda nayi muku "


Gefen dankwalinta taja tana share hawaye dashi, kuka take sosai harda Jan zuciya, liman ya kalleta yace" kiyi hakuri Amina "
Ahankali ta daga kanta tace"to baba"

Liman yace"Allah yayi miki albarka, wannan sadakinki ne danayi miki shi, nera dubu goma "

Ya ajiye mata kudin agefenta sannan yafita daga d'akin, matarsa ce ta shigo d'akin tajanyota jikinta tana Bata hakuri, har dare yayi Amina Bata Dena zubar hawaye ba, idonta har zafi yake saboda kuka, kuma adaren matar liman ta rakata d'akin da Asim yake sannan tayi mata sallama, shikam baisan ma tashigo dakinba Yana bacci, ita kuwa zaune ta kwana
Sai gab da sallar Asuba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login