Showing 21001 words to 24000 words out of 80494 words

Chapter 8 - INSAF BOOK COMPLETE BY Amnah El Yaqoub.doc

"ke zonan"

gabanta ne ya tsananta faduwa ahankali ta juyo tazo gabansa ta taugunna batare data kalleshi ba, tace "gani Yaya"

Duk da yaji Dadin muryarta dakuma yanda takirashi da sunan hakan bai Hana shi daure fuska ba, bayason tagama kallansa ta raina shi

"me kikeyi afalo bakiyi bacci ba?"

Tambayar tashi tazo mata a bazata, tarasa wacce amsa zata bashi, cikin inda inda tace "dama... dama... am kallo nazo zanyi.... Shine naleqa waje nadawo"

Zuba mata ido yayi Yana kallanta batare da yayi magana ba, dataji Shiru saita dago kanta ta kalleshi karaf idonta yasauka a cikin nasa, cikin sauri ta maida kanta qasa, Shima kallanta yayi ya sake tsuke qafafunsa Yana hadesu waje daya (>?#?=?H?)
Sannan yace "kawomin cup a kitchen"

Cikin sauri tatashi tayi kitchen din dama Zaman ya gundureta, tana kawo masa cup din tasake taugunna wa tabashi, karba yayi ya ajiye shi aqasa sannan yabude gorar ruwan yafara zubawa a cup din, saida yazuba sannan yasa hannu zai dauka cup din ya qwace daga hannunsa zai Fadi awajan, cikin sauri tasa hannunta zata tare cup din Shima yasa ka nasa hannun, hannunsa bai sauka ko'ina ba Sai Akan nata hannun, dago kanta tayi tana kallonsa Shima yazuba mata ido Yana Kallan manyan idanuwanta batare da sun janye hannayensu ba

Adede lokacin Lubna tabude kofar d'akin nasu tafuto taana zuba hamma, (=?F? @&?)

tashafa wajan baccinsa taji baya nan, kuma ta duba toilet ma baya nan, bakin data Bude tana hamma saita Kasa rufe shi tazub???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?a ido tana kallon su baki bude(>?#?)
Lokaci daya ta nemi baccin dayake idonta tarasa, huci tafara yi kamar zakanya ta nufesu, batayi wata wataba ta hankade Amina daga kusa dashi tafadi can gefe



Har hakan yayi sanadiyar faduwar cup din qasa, cikin fishi tace "annamimiya, uban me kikeyi anan Keda mijina? Ki tashi kibar nan wajan tun kafin nazama ajalinki"

Ahankali ta miqe tsaye tace "Anty Lubna bafa komai nake...."

"banason jin komai kibace kibar nan wajan nafada miki"

Girgiza kanta tayi tajuya tayi cikin dakinsu, Lubna ta juya ta kalli Asim daya zuba mata ido Yana kallonta Idonsa yayi jajir, tasan idan tayi magana tsaf zai Iya wanka mata Mari, Dan haka batace masa komai ba tashige daki tana sakin tsaki, sake kallonta yayi Yana jinjina rashin taarbiya irinna Lubna, yanzu shi takewa tsaki? Haqiqa tafara kawo shi wuya, Idan ya tashi yimata hukunci ba zataji dadi ba, in banda shirme metake tunani zai aikata da wannan yarinyar dayasan cewa idan yayi aure da wuri zai haifi kamarta?


Amina kuwa bataji Dadin abinda Lubna tayi mata ba, to Naga itama din mijinta ne, meyasa zatake mata haka? Cikin ranta tace wallahi Allah saiya saka min, kuma niba annamimiya bace, saide ke


Washe Gari da safe weekend ne kowa Yana gida, Amina Bata tashi da wuri ba kasancewar ta Dade batayi bacci ba, Sai wajan karfe goma tafarka, azabure tatashi kasancewar tatuna da maganar Lubna, idanunta tahau murtsikawa ta diro daga kan gadon tashiga toilet ta wanke bakinta da idonta tafuto falon, duk mutanan gidan suna nan banda Daddy

Anty Amrah tashige daki tana amsa wayar Amjad

"kakusa zuwa ne? Kaga niba wani kitchen dazan shiga, Kai inde baka takurani ba bakajin dadi kwata kwata rayuwarka" (>?#?)

hamdala Amina tayi dataga Asim baya nan, qila baici abinci Bama kwata kwata

Qamshin girki taji Yana tashi a kitchen, tadan leqa saita hango Anty Lubna tana girki, haka nan taji zuciyarta takasa samun nutsuwa da wannan abincin, Bata saniba ko acikinsa tazubawa Asim maganin, idaanma tazuba idan ma Bata zubaba insha Allah bazata Bari yaci abincin Nan ba

Zama tayi akujera tana tunanin dabara, agabanta Anty Lubna tagama jera abincin akan tire, ta qwalawa Amrah Kira

"Amrah!, nagama ki futo kikai sauran kan dinning, gana yayanku nazuba masa nasa daban zan kai masa daki"

Tazo wucewa tagaban Amina ta kalleta ta watsa mata harara, Amina ta yunqura ta tashi kamar zatayi cikin d'akin su da niyya tabangaje Anty Lubna, aikuwa abinci ya 6are (=??=?F? @&?)

Tana ganin abincin ya zube tayi hamdala a ranta

Anty Lubna kuwa baqin ciki ne ya kamata kamar ta mutu, maganin da suka dauki tsawon lokaci suna so su sakawa Asim a abinci yau tasamu tasaka masa shine wannan yarinyar zata zubar da abincin? Ta daga kai ta kalli Amina, tasaka yatsanta abakinta Tama rasa me zata mata taji sanyi, Amina ta sunkuya tahada mata kayan daya zube ta dago tace "Anty Lubna Dan Allah kiyi haku...." Bata qarasa ba Lubna ta zabge ta da wani irin gigitaccen Mari (=?F? @&?)

Akan Idonsa yaga Marin da Lubna ta zabga mata, ya tsaya a bakin kofar falon nasu yanaso yaga gudun ruwan ta

Ihun kukan datasa ne yasa Amrah futowa daga d'akin su da gudu, tana ganin Yaya Asim a bakin kofar falon ransa a mutuqar 6ace, Sai tayi Shiru

Anty Lubna tasake kallon Amina cikin haushi, saboda tayi mata wannan Dan Marin ne yasa tabude baki take mata wannan uban ihun? Aidama haushinta takeji, da baqin cikinta ta kwanta cikin dare saboda ta ganta da mijinta, cikin bacin rai tace "Dan uban ki Nasha wahala na yi girkin zaki zubar min dashi? Tsugunna ki tas ki debeshi"

Tana kokarin tsugunna wa tasake dauke ta da wani Marin wanda ya gagata Amina, cikin tsawa yace "Lubna!!!"

Atare suka kai kallonsu wajan kofar, Amina tashige cikin dakinsu da gudu tana kuka, cikin falon ya qara so cikin fishi yace "waike Lubna wacce irin mahaukaciya ce ne?"

Amrah tana ganin haka tayi d'akin mamy tadugu zata sanar mata, saboda Bata taba ganin ran yayan nata yabaci haka ba

Cikin bacin rai itama tace "nikake cewa mahaukaciya saboda wannan yarinyar marar asali?, kasan wahalar danasha wajan wannan girkin zatazo tazubar min dashi?"

Nunata yayi da hannu yace "to waye zaiyi abinda kikayi yanzu inba mahaukaci ba? Yarinyar dabatafi ki zaneta da tsinken tsintsinya ba shine zaki kamata kina duka kamar Kin samu baiwa? Dududu nawa yarinyar take dazaki mata irin wannan dukan? Kokuma bakya tunanin irin wannan dukan zaisata ta kangare? Duka lalata Yaro yake, idan kika kuskura kika sake dukanta wallahi Sai ranki yabaci "

Yana fadar haka yabi bayan Amina cikin d'akin su

Mamaki, taraddadi, dakuma faduwar gaba duk suka taru sukayiwa Lubna yawa, Anya kuwa Asim bai fara samun matsala Akan yarinyar nan ba? Kode ba kalau tabarshi ba? >??
Yanzu wannan yarinyar zai Dubi idonta yace mata tadaketa da tsinken tsintsiya? Saikace Widad?

Yana shiga d'akin ya ganta ta kifa kanta Akan gado tana rusgar kuka, tausayi tabashi sosai, shide Yana tausayin yarinyar
Ahankali ya zauna agefen gadon dab da'ita, so yake yabata hakuri, amma yarasa mezai ce mata, shide ba lallashin matarsa yake ba bare ya qware wajan lallashi, komaai saide ayi masa, kamar bakinsa Yana masa nauyi yace "kiyi Shiru"

Dago kanta tayi ta kalleshi, batare da tunanin komai ba tafada kan faffadan qirjinsa ta rungume shi sosai tana cigaba da kuka

Mamaki ya kama shi, yarinyar nan kuwa kalau take? Meyasa zata rungume shi,sake kallanta yayi yaga yanda ta kwantar da kanta Akan qirjinsa,Kasa rungumeta yayi da hannayensa, kukan datake dakuma yanda yake jin tudun nashanunta Akan qirjinsa shine ya haddasa Masa shiga cikin wani yanayi, gakuma tsikar jikinsa Sai tashi take, Ahankali kamar mai tsoron wani abu yasa ka hannunsa ya rungumeta sosai,Yana bubbuga bayan ta alamar lallashi, ita datake kuka maimakon ace itace take sauke Ajiyar a zuciya Sai abin yazo a bazata, domin kuwa wata irin wawuyar Ajiyar zuciya Asim yake saukewa Ajere (=??)

Lubna tabiyosu cikin d'akin cike da masifa, amma saide me? A halin data gansu ne yasa tajuya cikin tashin hankali ta Dora hannu aka, tasaki ihun kuka "nashiga uku na,nashiga uku shikkenan ta qwacemin mijina"

Asim yanajin kukanta yajanye jikinsa daga na Amina ahankali, ya tashi yakulle kofar d'akin,(=?3?) sannan yadawo yazauna aqasan gadon, yakamo hannyen Amina datake zaune Akan gado yariqe hannayen nata cikin nasa,yazubawa fuskarta ido Yana kallon yanda gashin idonta suka jiqe, saboda kuka

Ita kuwa Amina Kasa dago kanta ta kalleshi tayi, hawaye Yana silalowa daga idanuwanta zuwa kan kumatunta, gashi babu Damar gogewa ya kama hannayen nata duka biyun yariqesu cikin tattausan hannunsa


Mamy da Amrah ne suka qara so wajan, futowar ta kenan daga wanka Amrah tace mata gidan nasu ba qalau ba tazo tayi musu magana

Lubna tayi wani irin zama a falon tana ihun kuka Minal ta qwace mata miji

Mamy ta qarasa bakin kofar d'akin tafara nocking













Tofa, wata dramar Sai a gidan Asim, >?#?>?#?>?#?







Sharhi pls







Amnah El~Yaqoub
' [2/9, 11:07 PM] El~Yaqoub: INSAAF

Writing by:Amnah El yaqoub

Like my page on Facebook =?G?
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


15&16



Yana jinsu suna nocking amma ko alamun tashi baiyi ba, asalima hannunta dayake cikin nasa yafara murzawa ahankali,shikansa baisan dalilin dayasa yake murza mata hannun ba, amma bazai iya daina wa ba saboda sabon al'amarin dayake shigar sa, Kasa dagowa tayi ta kalleshi, gaba daya yayi mata wani irin kwarjini, shidin babban mutum ne ba qananun Samari ba irinsu Amjad..., muryarsa ya sassauta cikin sigar rad'a yakirata "Minal"

Dago idonta tayi ta kalleshi, idonta har yayi ja, hawaye ya zubo daga cikin idonta guda daya, cikin ransa yace "yasalam..."

Tunda take dashi yau ne Karon farko daya taba Kiran sunan ta, saita ji abun wani iri, saboda bai sababa, saide koda yaushe yace mata "ke", kokuma
Ke zonan, ke tashi mutafi, ke dauko min abu kaza, yanda yake murza hannunta saiya hakan yafara haddasa mata shiga cikin yanayi, Ahankali tace "na'am"

Tashi yayi daga qasan gadon yadawo dab da'ita ya zauna batare daya Raba hannunsa danata ba
Cikin rad'a yasake ambaton sunanta akaro biyu "Minal"

Muryarta na rawa ta amsa masa, hannunta yasaki yasake matsowa dab da'ita har suna jin numfashin juna, hannayensa yasaka yariqe fuskarta dashi, sannan yazuba mata ido Yana kallanta batare dayace komai ba,d'an qaramin lips dinta yake kallo,wanda yake ji kamar yadora nasa akai, Ahankali tadago kanta tazuba masa manyan idonta, idonsu ya sarqe dana juna, wannan Karon Bata janye idonta daga cikin nasaba, haka Shima baice mata komai ba, yade riqe fuskartata da hannunsa Yana kallonta kamar yasamu sabuwar halitta, idonta ne yayi raurau yafara kawo qwalla, Ahankali ya Matso da fuskarsa kusa da Tata kamar mai shirin yimata kiss, cikin rad'a yace "ki.... kiyi... hakuri..."

Kallansa tayi, sauran qwallar datake riqewa suka zubo mata, ba kukan komai takeba saina tausayin sa, Yana tare da mata amma baisan tana masa zagon qasa ba.


Sake sassauta Muryarsa yayi yace "kinji..."

Hannunta tasa ta share hawayen tace "babu komai Yaya, na haqura"

Kallanta yasake yi yace "are you serious?"

Jijjiga masa kai tayi kawai.


Mummunan bugon da a kayi wa kofar ne yasa yasaki fuskar Tata ahankali sannan ya tashi ya nufi kofar yabude


Gaba dayansu ne suka Danno kansu cikin d'akin (=??)
Mamy, Amrah, da Anty Lubna wadda fuskarta tayi sha6e-sha6e da hawaye, Kallan Asim tayi dayake tsaye sannan ta kalli mamy cikin kuka tace "gashinan mamy ki tambayeshi, wallahi rungume ta yayi, male-male naganta a qirjinsa" (=?F? @&?)

Gaban Amina yayi wata irin faduwa, idanunta yayi tsilli-tsilli tana kallon mamy
Shikuwa gogan babu alamun damuwa afuskar sa yara6a ta gefensu yafice daga d'akin

Anty Amrah tafice daga d'akin tana girgiza kanta, tayaya Yaya Asim zai rungume Minal? Mamy ta kalli Lubna tace "kiyi hakuri Lubna, zanyi magana dashi"

Daga nan taja hannunta suka fice daga d'akin, Anty Lubna tadawo d'akin hannunta dauke da ruwa a cup, miqawa Amina tayi tace "ki karba Kisha Minal"

Babu musu tasa hannu ta karbi cup din tashanye duka ruwan, sannan tasaki Ajiyar zuciya, Anty Amrah tayi qasa da murya ta kalli Amina tace "Minal waida gaske ne yaya ya rungume ki?" (=? ?)
tafadi maganar cikin sigar son jin gulma

Cikin sauri ta girgiza kanta "a a Anty Amrah, ni be rungume niba"

Murmushi Amrah tayi tasake kallanta da kyau "to kuma nida nake qawar takima boyemin zakiyi? Dan Allah ya rungume ki?"

Sake girgiza kanta tayi "Anty Amrah bafa haka bane"

"bawani nan, kede kawai kice yau Yaya yarage zafi" (>?#?)

Amina takalleta tace "Anty Amrah kifahimce ni..."

Katseta Amrah tayi "bawani fahimta yarinya, tome yake fada miki dakuka kulle d'akin?"

Kai tsaye tace "hakuri yabani"

Cikin sauri Amrah tace "Dan Allah da gaske kike? Yaya Asim ne yabaki hakuri da kansa?"

Cikin mamaki tace "baya bayarwa ne?"

Amrah ta jinjina kanta tace "lalle bansan wacce irin sa'ah gareki ba, nida zai aure ki ma danaji dadi wallahi, Anty Lubna kishin ta yayi yawa wallahi, kuma yawanci masu zafafa kishin nan Allah yafi jarabtar su dayi musu kishiya, domin ya gwada imaninsu"

Tana Gama maganar ta tashi tsaye yace "qanina yakusa dawowa daga Yola, Bari naje bakin gate na taro shi"

Amina ta daga mata kai, Wai qaninta, dama Anty Amrah tanada qanine?

Amrah nafita falo taci Karo da Amjad harma ya shigo gidan, hannunta tabude tatafi da sauri kamar zata rungume shi tace "oyoyo d'an qanina" (>?#?)

Amjad ya kalleta, ya sake kallonta daga Sama har qasa, yadaga murya yace "Wai ke Anty Amrah meyake damunki ne Dan Allah?,yanzu inda tare muke da wasu haka zaki dizgani, Wai qaninki"

Bacin rai sosai a saman fuskar sa, ya nemi waje yazauna a daya daga cikin kujerun falon

Itama zama tayi tace "Dan rainin hankali, danma kasamu inama oyoyo, waye yazo yayima haka a gidan?"

Cikin fada yace "eh Karki qarayi inde saikin cemin qaninki, harda wani god'ai god'ai dani Saina zauna kina cemin qaninki"

"toba qanin nawa bane? Nawa kake? Fina kayi?dakaqi dakaso Anty Amrah dole, kuma nice de gaba dakai, babu yanda zakayi dani"

Cikin bacin rai yace "OK haka kikace?"

Itama cikin dakewa tace "yes"

Yace "OK, to wallahi kinemi abokin shawararki, bade niba, samarin ki kowa kika kwaso saikinzo kin nemi shawara ta, todaga yau ta qare, kinemi yayanki, wanda yafi ki, saiya baki shawara" (=? ?)

Tace "inde Akan nace qaninane kake wannan ihun, wallahi Amjad bazan daina ba, qilama har goyaka nayi lokacin dakake Yaro, wayasani ma ko harda wanka nama (=?3?)
Kawai daga zuwan ka kamar wani jarababbe kazo kahau ni da masifa"

Amjad yayi Shiru Yama rasa mezai ce mata (>?#?)
Da Hankalinsa mamy take musu wanka gaba dayansu, amma saboda tsabar rainin hankali shi zata kalla tace tayiwa wanka, harda cewa kamar jarababbe, kallanta yayi Shima yace "aini kamar jarababben ne, ke kuwa jarabar Cema gaba dayanta" (>?#?)

Kallansa tayi tace "yayi kyau, ka gwadamin hankali, gobe ma idan zaka dawo zan futo ina rawar jiki, na tarbeka" daga nan tafara yunqurin tashi

Hannunsa yasa ya fuzgota saigata azaune Akan kujera, Kallan mamaki tayi masa, yanzu Amjad ne yake da wannan qarfin har ya fuzgota haka?
Shikuma baima lura da irin kallon datake masa ba, yayi qasa da murya yace "haba Anty Amrah, ai Bama 'yar haka dake, menene kuma rayuwar?"

Cikin fishi tace "to ai Kaine kake neman rainani Amjad, saboda kaga kafara ajiye gemu"

Cikin qasa da murya kamar bashi ba yace "kifadi komai ma baji, inde babu mutane awajan (=??)
ina jama'ar gidan suke ne?"

Ajiyar zuciya tayi tace "kowa Yana d'akin sa, ai yau baram baram akayi in fadama"

Zamansa ya gyara yace "haba? dawa akayi?"

"Yaya Asim da Anty Lubna, Akan Minal ne fadan, saura kadan ya Mari Anty Lubna, aikuwa nabar wajan ban tsaya ba, Anty Lubna Sai ihu take Wai Minal zata qwace mata miji, Wai ta gansu itada Yaya Asim harma ya rungume ta"

Gaban Amjad yafadi yace "waida gaske kike?"

Amrah tace "haka de Anty Lubna tace"

Cikin sauri ya miqe zai tafi d'akin mamy, hannunsa ta ruqo tace "ina zaka?"

"zuwa zanyi wajan mamy, wallahi inason yarinyar nan, tun lokacin dana fara ganin ta" (=?F? @&?)

Tace "aikuwa karka shiga yanzu, Dan naji maganar Yaya acikin d'akin, kabari sugama magana shida mamy Sai kaje"

Cikin damuwa yakoma kan kujerar ya zauna, yace mata "ina abinci na?"

Nuni tayi masa da dining tace "gashi can a dining, Anty Lubna ce tayi"

Girgiza mata kansa yayi, sannan ya nufi dining din





*** ***** ***




"Asim, kafadamin gaskiya, wacce irin magana naji Lubna ta nayi? Da gaske ne ka rungume Minal?"

Karon farko daya fara yiwa mahaifiyarsa qarya, koda yaushe baya boye mata komai, kullum cikin fada mata gaskiya yake, qeyarsa ya Sosa sannan yakalleta yace "mamy...runguma kuma?"

Tace "Asim matarka zatama qarya ne? Baka rungume Minal dinba?"

Shima cikin dakiya yace "to mamy saboda me? Niban rungume taba"

"to koma de menene banason naqara jin hakan, kadena biyewa shirman Lubna"


Wata irin Ajiyar zuciya yasaki a6oye, sannan yayi hamdala a ransa da mamy Bata ganoshi ba, kansa aqasa yace "insha Allah mamy"

Tace "Allah yayi maka albarka, tashi katafi"

Babu musu ya tashi yafuto daga d'akin, mamy tabishi da kallo, itade tasan Asim baya mata qarya, amma wannan Sosa qeyar da yayi alamu ne na rashin gaskiya, kuma tunda take da Asim baitaba kawo mata yarinya yace yanaso ba, ita kanta Lubna tasan cewa bayaso amma ahaka ya aureta, to kode son Minal din yake? Tayaya zata yarda cewa bai rungume taba? Bayan kulle d'akin sukayi? (>?#?)
Kuma sunaji Ana nocking sukaqi budewa, idan ba rungume ta yayi ba to nasiha yake mata?>??

Ajiyar zuciya tasaki tana fatan ace Bahaka bane, Dan batasan tashin hankalin da Lubna zata shiga ba Akan haka, kuma kowa Sai hankalin sa ya tashi Akan haukan kishinta

Amjad ne ya shigo d'akin, Yana zuwa yafada jikinta, cikin shagwaba yace "mamy I miss you sosai wallahi"

Kansa ta shafa tace "Anya kuwa Amjad wannan aikin naka baka saka shiririta acikinsa? Daga zuwa wajan aiki yan Kwanaki harka dawo gida?"

Cikin shagwaba yace "uhm... Allah mamy ni bazan iya irinna Yaya ba, bazan iya wata daya batare dana ganki ba"

Taji Dadin furucinsa sosai, tace "Allah yayi muku albarka autana, Allah yaraya minku"

Sake shigewa jikinta yayi yace "Amin, mamy wata magana zamuyi"

Dagoshi tayi daga jikinta, sannan tayi masa kallon fahimta tace "inajin ka, wacce irin magana?"

Kallanta yayi yace " mamy dama zan fada miki ne, inason Minal, inason in aureta idan kun amince Keda Yaya"

Murmushin manya mamy tayi, cikin ranta taji dadi sosai, ko banza Amjad yakawo musu maslaha Akan rikicin Lubna da Asim, tace "to Allah ya tabbatar mana da Alkhairi, zan sameshi muyi maganar dashi insha Allah"

Cikin murna Amjad yace "yes...shiyasa nake sonki mamy na, Allah yabar mana ke" yakama hannunta yayi kissing hannun, sannan yafuto daga d'akin cikin murna





*** ****** ***






Zaune suke a d'akin su washe Gari, itada Amrah

Amrah ta kalleta taga tayi Shiru tana tunani, ta matsa kusa da'ita tace "Minal, in baki wata shawara mana"

Kallonta tayi tace "menene Anty Amrah?"

Amrah takama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login